« Prev

78. Surah An-Naba' سورة النبأ

Next »




First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
عَمَّ يَتَسَاءَلُونَ
Hausa
 
A kan mẽ suke tambayar jũna?

Ayah   78:2   الأية
عَنِ النَّبَإِ الْعَظِيمِ
Hausa
 
A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?

Ayah   78:3   الأية
الَّذِي هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ
Hausa
 
Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?

Ayah   78:4   الأية
كَلَّا سَيَعْلَمُونَ
Hausa
 
A'aha! Zã su sani.

Ayah   78:5   الأية
ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ
Hausa
 
Kuma, a'aha! Zã su sani.

Ayah   78:6   الأية
أَلَمْ نَجْعَلِ الْأَرْضَ مِهَادًا
Hausa
 
Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?

Ayah   78:7   الأية
وَالْجِبَالَ أَوْتَادًا
Hausa
 
Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?

Ayah   78:8   الأية
وَخَلَقْنَاكُمْ أَزْوَاجًا
Hausa
 
Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?

Ayah   78:9   الأية
وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًا
Hausa
 
Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?

Ayah   78:10   الأية
وَجَعَلْنَا اللَّيْلَ لِبَاسًا
Hausa
 
Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

Ayah   78:11   الأية
وَجَعَلْنَا النَّهَارَ مَعَاشًا
Hausa
 
Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?

Ayah   78:12   الأية
وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًا شِدَادًا
Hausa
 
Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?

Ayah   78:13   الأية
وَجَعَلْنَا سِرَاجًا وَهَّاجًا
Hausa
 
Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?

Ayah   78:14   الأية
وَأَنزَلْنَا مِنَ الْمُعْصِرَاتِ مَاءً ثَجَّاجًا
Hausa
 
Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?

Ayah   78:15   الأية
لِّنُخْرِجَ بِهِ حَبًّا وَنَبَاتًا
Hausa
 
Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?

Ayah   78:16   الأية
وَجَنَّاتٍ أَلْفَافًا
Hausa
 
Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?

Ayah   78:17   الأية
إِنَّ يَوْمَ الْفَصْلِ كَانَ مِيقَاتًا
Hausa
 
Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.

Ayah   78:18   الأية
يَوْمَ يُنفَخُ فِي الصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًا
Hausa
 
Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.

Ayah   78:19   الأية
وَفُتِحَتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ أَبْوَابًا
Hausa
 
Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.

Ayah   78:20   الأية
وَسُيِّرَتِ الْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا
Hausa
 
Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.

Ayah   78:21   الأية
إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًا
Hausa
 
Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.

Ayah   78:22   الأية
لِّلطَّاغِينَ مَآبًا
Hausa
 
Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.

Ayah   78:23   الأية
لَّابِثِينَ فِيهَا أَحْقَابًا
Hausa
 
Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.

Ayah   78:24   الأية
لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًا وَلَا شَرَابًا
Hausa
 
Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.

Ayah   78:25   الأية
إِلَّا حَمِيمًا وَغَسَّاقًا
Hausa
 
Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.

Ayah   78:26   الأية
جَزَاءً وِفَاقًا
Hausa
 
Sakamako mai dãcẽwa.

Ayah   78:27   الأية
إِنَّهُمْ كَانُوا لَا يَرْجُونَ حِسَابًا
Hausa
 
Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.

Ayah   78:28   الأية
وَكَذَّبُوا بِآيَاتِنَا كِذَّابًا
Hausa
 
Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!

Ayah   78:29   الأية
وَكُلَّ شَيْءٍ أَحْصَيْنَاهُ كِتَابًا
Hausa
 
Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.

Ayah   78:30   الأية
فَذُوقُوا فَلَن نَّزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا
Hausa
 
Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.

Ayah   78:31   الأية
إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا
Hausa
 
Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

Ayah   78:32   الأية
حَدَائِقَ وَأَعْنَابًا
Hausa
 
Lambuna da inabõbi.

Ayah   78:33   الأية
وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًا
Hausa
 
Da cikakkun 'yammata, tsãrar jũna.

Ayah   78:34   الأية
وَكَأْسًا دِهَاقًا
Hausa
 
Da hinjãlan giya cikakku.

Ayah   78:35   الأية
لَّا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا كِذَّابًا
Hausa
 
Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

Ayah   78:36   الأية
جَزَاءً مِّن رَّبِّكَ عَطَاءً حِسَابًا
Hausa
 
Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

Ayah   78:37   الأية
رَّبِّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا الرَّحْمَٰنِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًا
Hausa
 
Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

Ayah   78:38   الأية
يَوْمَ يَقُومُ الرُّوحُ وَالْمَلَائِكَةُ صَفًّا ۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ الرَّحْمَٰنُ وَقَالَ صَوَابًا
Hausa
 
Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

Ayah   78:39   الأية
ذَٰلِكَ الْيَوْمُ الْحَقُّ ۖ فَمَن شَاءَ اتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِ مَآبًا
Hausa
 
Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

Ayah   78:40   الأية
إِنَّا أَنذَرْنَاكُمْ عَذَابًا قَرِيبًا يَوْمَ يَنظُرُ الْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ الْكَافِرُ يَا لَيْتَنِي كُنتُ تُرَابًا
Hausa
 
Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"





© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us