1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
المر ۚ تِلْكَ آيَاتُ الْكِتَابِ ۗ وَالَّذِي أُنزِلَ إِلَيْكَ مِن رَّبِّكَ
الْحَقُّ وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَ النَّاسِ لَا يُؤْمِنُونَ
Alif-lam-meem-ra tilka ayatualkitabi wallathee onzila ilayka minrabbika alhaqqu
walakinna akthara annasila yu/minoon
Hausa
A. L̃. M̃. R. Waɗancan ayõyin littãfi ne kuma abin da aka saukar gare ka daga
Ubangijinka ne gaskiya, kuma amma mafi yawan mutãne bã su yin ĩmãni.
|
Ayah 13:2 الأية
اللهُ الَّذِي رَفَعَ السَّمَاوَاتِ بِغَيْرِ عَمَدٍ تَرَوْنَهَا ۖ ثُمَّ
اسْتَوَىٰ عَلَى الْعَرْشِ ۖ وَسَخَّرَ الشَّمْسَ وَالْقَمَرَ ۖ كُلٌّ يَجْرِي
لِأَجَلٍ مُّسَمًّى ۚ يُدَبِّرُ الْأَمْرَ يُفَصِّلُ الْآيَاتِ لَعَلَّكُم
بِلِقَاءِ رَبِّكُمْ تُوقِنُونَ
Allahu allathee rafaAAa assamawatibighayri AAamadin tarawnaha thumma istawa
AAalaalAAarshi wasakhkhara ashshamsa walqamara kullunyajree li-ajalin musamman
yudabbiru al-amra yufassilu al-ayatilaAAallakum biliqa-i rabbikum tooqinoon
Hausa
Allah Shi ne wanda Ya ɗaukaka sammai, bã da ginshiƙai ba waɗanda kuke ganin su.
Sa'an nan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi, kuma Ya hõre rãnã da watã, kõwane
yanã gudãna zuwa ga ajali ambatacce. Yanã shirya al'amari, Yanã rarrabe ãyõyi
daki-daki, mai yiwuwa ne ku yi yaƙĩni da haɗuwa da Ubangijinku.
|
Ayah 13:3 الأية
وَهُوَ الَّذِي مَدَّ الْأَرْضَ وَجَعَلَ فِيهَا رَوَاسِيَ وَأَنْهَارًا ۖ وَمِن
كُلِّ الثَّمَرَاتِ جَعَلَ فِيهَا زَوْجَيْنِ اثْنَيْنِ ۖ يُغْشِي اللَّيْلَ
النَّهَارَ ۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَاتٍ لِّقَوْمٍ يَتَفَكَّرُونَ
Wahuwa allathee madda al-ardawajaAAala feeha rawasiya waanharan waminkulli
aththamarati jaAAala feeha zawjayniithnayni yughshee allayla annahara inna fee
thalikalaayatin liqawmin yatafakkaroon
Hausa
Kuma shĩ, ne wanda Ya shimfiɗa kasa, kuma Ya sanya duwãtsu da kõguna a cikinta,
kuma daga dukan 'ya'yan itãce Ya sanya ma'aura biyu cikinsu. Yanã sanya dare ya
rufe yini. Lalle ne a cikin wancan, haƙĩƙa akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke
yin tunãni.
|
Ayah 13:4 الأية
وَفِي الْأَرْضِ قِطَعٌ مُّتَجَاوِرَاتٌ وَجَنَّاتٌ مِّنْ أَعْنَابٍ وَزَرْعٌ
وَنَخِيلٌ صِنْوَانٌ وَغَيْرُ صِنْوَانٍ يُسْقَىٰ بِمَاءٍ وَاحِدٍ وَنُفَضِّلُ
بَعْضَهَا عَلَىٰ بَعْضٍ فِي الْأُكُلِ ۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَاتٍ لِّقَوْمٍ
يَعْقِلُونَ
Wafee al-ardi qitaAAun mutajawiratunwajannatun min aAAnabin wazarAAun
wanakheelun sinwanunwaghayru sinwanin yusqa bima-in wahidinwanufaddilu baAAdaha
AAala baAAdinfee alokuli inna fee thalika laayatinliqawmin yaAAqiloon
Hausa
Kuma a cikin ƙasa akwai yankuna mãsu maƙwabtaka, da gõnaki na inabõbi da shũka
da dabĩnai iri guda, da waɗanda bã iri guda ba, anã shayar da su da ruwa guda.
Kuma Munã fĩfĩta sãshensa a kan sãshe a wajen ci. Lalle ne a cikin wancan akwai
ãyõyi ga muiãne waɗanda suke hankalta.
|
Ayah 13:5 الأية
وَإِن تَعْجَبْ فَعَجَبٌ قَوْلُهُمْ أَإِذَا كُنَّا تُرَابًا أَإِنَّا لَفِي خَلْقٍ
جَدِيدٍ ۗ أُولَٰئِكَ الَّذِينَ كَفَرُوا بِرَبِّهِمْ ۖ وَأُولَٰئِكَ الْأَغْلَالُ
فِي أَعْنَاقِهِمْ ۖ وَأُولَٰئِكَ أَصْحَابُ النَّارِ ۖ هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ
Wa-in taAAjab faAAajabun qawluhum a-ithakunna turaban a-inna lafee khalqin
jadeedinola-ika allatheena kafaroo birabbihim waola-ikaal-aghlalu fee aAAnaqihim
waola-ika as-habuannari hum feeha khalidoon
Hausa
Kuma idan ka yi mãmãki, to, mãmãkin kam shi ne maganarsu, "Shin, idan muka
kasance turɓãya, zã mu zama a cikin wata halitta sãbuwa?" Waɗancan ne waɗanda
suka kãfirta da Ubangijinsu, kuma waɗanda akwai ƙuƙumai a cikin wuyõyinsu, kuma
waɗancan ne abõkan wuta. Sũ, a cikinta, mãsu dawwama ne.
|
Ayah 13:6 الأية
وَيَسْتَعْجِلُونَكَ بِالسَّيِّئَةِ قَبْلَ الْحَسَنَةِ وَقَدْ خَلَتْ مِن
قَبْلِهِمُ الْمَثُلَاتُ ۗ وَإِنَّ رَبَّكَ لَذُو مَغْفِرَةٍ لِّلنَّاسِ عَلَىٰ
ظُلْمِهِمْ ۖ وَإِنَّ رَبَّكَ لَشَدِيدُ الْعِقَابِ
WayastaAAjiloonaka bissayyi-atiqabla alhasanati waqad khalat min qablihimu
almathulatuwa-inna rabbaka lathoo maghfiratin linnasiAAala thulmihim wa-inna
rabbaka lashadeedualAAiqab
Hausa
Kuma sunã nẽman ka da gaggãwa da azãba a gabãnin rahama, alhãli kuwa abũbuwan
misãli sun gabãta a gabãninsu. Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Ma'abũcin
gãfara ne ga mutãne a kan zãluncinsu, kuma lalle ne Ubangijinka,haƙĩƙa, Mai
tsananin uƙũba ne.
|
Ayah 13:7 الأية
وَيَقُولُ الَّذِينَ كَفَرُوا لَوْلَا أُنزِلَ عَلَيْهِ آيَةٌ مِّن رَّبِّهِ ۗ
إِنَّمَا أَنتَ مُنذِرٌ ۖ وَلِكُلِّ قَوْمٍ هَادٍ
Wayaqoolu allatheena kafaroo lawlaonzila AAalayhi ayatun min rabbihi innama anta
munthirunwalikulli qawmin had
Hausa
Kuma waɗanda suka kãfirta sunã cẽwa don me ba a saukar da wata ãyã a gare shi ba
daga Ubangijinsa? Abin sani kawai, kai dai mai gargaɗi ne kuma a cikin kõwaɗanne
mutãne akwai mai shiryarwa.
|
Ayah 13:8 الأية
اللهُ يَعْلَمُ مَا تَحْمِلُ كُلُّ أُنثَىٰ وَمَا تَغِيضُ الْأَرْحَامُ وَمَا
تَزْدَادُ ۖ وَكُلُّ شَيْءٍ عِندَهُ بِمِقْدَارٍ
Allahu yaAAlamu ma tahmilukullu ontha wama tagheedu al-arhamuwama tazdadu
wakullu shay-in AAindahu bimiqdar
Hausa
Allah Yanã sanin abin da kõwace mace take ɗauke da shi a cikinta da abin da
mahaifu suke ragẽwa da abin da suke ƙãrãwa. Kuma dukkan kõme, a wurinSa, da
gwargwado yake.
|
Ayah 13:9 الأية
عَالِمُ الْغَيْبِ وَالشَّهَادَةِ الْكَبِيرُ الْمُتَعَالِ
AAalimu alghaybi washshahadatialkabeeru almutaAAal
Hausa
Shi ne Masanin fake da bayyane, Mai girma, Maɗaukaki.
|
Ayah 13:10 الأية
سَوَاءٌ مِّنكُم مَّنْ أَسَرَّ الْقَوْلَ وَمَن جَهَرَ بِهِ وَمَنْ هُوَ مُسْتَخْفٍ
بِاللَّيْلِ وَسَارِبٌ بِالنَّهَارِ
Sawaon minkum man asarra alqawlawaman jahara bihi waman huwa mustakhfin billayli
wasaribunbinnahar
Hausa
Daidai ne daga gare ku, wanda ya asirta magana da wanda ya bayyana game da ita,
da wanda yake shi mai nẽman ɓõyewa ne da dare, da mai bayyana a cikin tafiyarsa
a hanya da rãna.
|
Ayah 13:11 الأية
لَهُ مُعَقِّبَاتٌ مِّن بَيْنِ يَدَيْهِ وَمِنْ خَلْفِهِ يَحْفَظُونَهُ مِنْ أَمْرِ
اللهِ ۗ إِنَّ اللهَ لَا يُغَيِّرُ مَا بِقَوْمٍ حَتَّىٰ يُغَيِّرُوا مَا
بِأَنفُسِهِمْ ۗ وَإِذَا أَرَادَ اللهُ بِقَوْمٍ سُوءًا فَلَا مَرَدَّ لَهُ ۚ
وَمَا لَهُم مِّن دُونِهِ مِن وَالٍ
Lahu muAAaqqibatun min bayni yadayhiwamin khalfihi yahfathoonahu min amri
Allahiinna Allaha la yughayyiru ma biqawmin hattayughayyiroo ma bi-anfusihim
wa-itha aradaAllahu biqawmin soo-an fala maradda lahu wamalahum min doonihi min
wal
Hausa
(Kowannenku) Yanã da waɗansu malã'iku mãsu maye wa jũna a gaba gare shi da bãya
gare shi, sunã tsare shi daga umurnin Allah. Lalle ne Allah bã Ya canja abin da
yake ga, mutãne sai sun canja abin da yake ga zukatansu. Kuma idan Allah Ya yi
nufin wata azãba game da mutãne, to, bãbu mai mayar da ita, kuma bã su da wani
majiɓinci baicin Shi.
|
Ayah 13:12 الأية
هُوَ الَّذِي يُرِيكُمُ الْبَرْقَ خَوْفًا وَطَمَعًا وَيُنشِئُ السَّحَابَ
الثِّقَالَ
Huwa allathee yureekumu albarqakhawfan watamaAAan wayunshi-o assahaba aththiqal
Hausa
Shĩ ne Wanda Yake nũna muku walƙiya dõmin tsõro da tsammãni, kuma Ya ƙãga
halittar girãgizai mãsu nauyi.
|
Ayah 13:13 الأية
وَيُسَبِّحُ الرَّعْدُ بِحَمْدِهِ وَالْمَلَائِكَةُ مِنْ خِيفَتِهِ وَيُرْسِلُ
الصَّوَاعِقَ فَيُصِيبُ بِهَا مَن يَشَاءُ وَهُمْ يُجَادِلُونَ فِي اللهِ وَهُوَ
شَدِيدُ الْمِحَالِ
Wayusabbihu arraAAdu bihamdihiwalmala-ikatu min kheefatihi wayursilu
assawaAAiqafayuseebu biha man yashao wahum yujadiloonafee Allahi wahuwa shadeedu
almihal
Hausa
Kuma arãdu tanã tasbĩhi game da gõde Masa, da malã'iku dõmin tsoronsa. Kuma Yanã
aiko tsãwawwaki, sa'an nan Ya sãmi wanda Yake so da su alhãli kuwa sũ, sunã
jãyayya a cikin (al'amarin) Allah kuma shĩ ne mai tsananin hĩla.
|
Ayah 13:14 الأية
لَهُ دَعْوَةُ الْحَقِّ ۖ وَالَّذِينَ يَدْعُونَ مِن دُونِهِ لَا يَسْتَجِيبُونَ
لَهُم بِشَيْءٍ إِلَّا كَبَاسِطِ كَفَّيْهِ إِلَى الْمَاءِ لِيَبْلُغَ فَاهُ وَمَا
هُوَ بِبَالِغِهِ ۚ وَمَا دُعَاءُ الْكَافِرِينَ إِلَّا فِي ضَلَالٍ
Lahu daAAwatu alhaqqi wallatheenayadAAoona min doonihi la yastajeeboona lahum
bishay-in illakabasiti kaffayhi ila alma-iliyablugha fahu wama huwa bibalighihi
wamaduAAao alkafireena illa fee dalal
Hausa
Yanã da kiran gaskiya, kuma waɗanda (kãfirai) suke kira baicinsa, bã su karɓa
musu da kõme fãce kamar mai shimfiɗa tãfukansa Zuwa ga ruwa (na girgije) dõmin
(ruwan) ya kai ga bãkinsa, kuma shi bã mai kaiwa gare shi ba. Kuma kiran kãfirai
(ga wanin Allah) bai zama ba fãce yanã a cikin ɓata.
|
Ayah 13:15 الأية
وَلِلَّهِ يَسْجُدُ مَن فِي السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ طَوْعًا وَكَرْهًا
وَظِلَالُهُم بِالْغُدُوِّ وَالْآصَالِ ۩
Walillahi yasjudu man fee assamawatiwal-ardi tawAAan wakarhan
wathilaluhumbilghuduwwi wal-asal
Hausa
Kuma sabõda Allah wanda yake a cikin sammai da ƙasa suke yin sujada, so da ƙi,
kuma da inuwõyinsu, a sãfe da maraice.
|
Ayah 13:16 الأية
قُلْ مَن رَّبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ قُلِ اللهُ ۚ قُلْ أَفَاتَّخَذْتُم
مِّن دُونِهِ أَوْلِيَاءَ لَا يَمْلِكُونَ لِأَنفُسِهِمْ نَفْعًا وَلَا ضَرًّا ۚ
قُلْ هَلْ يَسْتَوِي الْأَعْمَىٰ وَالْبَصِيرُ أَمْ هَلْ تَسْتَوِي الظُّلُمَاتُ
وَالنُّورُ ۗ أَمْ جَعَلُوا لِلَّهِ شُرَكَاءَ خَلَقُوا كَخَلْقِهِ فَتَشَابَهَ
الْخَلْقُ عَلَيْهِمْ ۚ قُلِ اللهُ خَالِقُ كُلِّ شَيْءٍ وَهُوَ الْوَاحِدُ
الْقَهَّارُ
Qul man rabbu assamawatiwal-ardi quli Allahu qul afattakhathtummin doonihi
awliyaa la yamlikoona li-anfusihimnafAAan wala darran qul hal yastawee
al-aAAmawalbaseeru am hal tastawee aththulumatuwannooru am jaAAaloo lillahi
shurakaakhalaqoo kakhalqihi fatashabaha alkhalqu AAalayhim quliAllahu khaliqu
kulli shay-in wahuwa alwahidualqahhar
Hausa
Ka ce: "Wãne ne Ubangijin sammai da ƙasa?" Ka ce: "Allah". Ka ce: "Ashe fa, kun
riƙi waɗansu masõya baicin Shi, waɗanda ba su mallaka wa kansu wani amfãni ba
kuma haka bã su tũre wata cũta?" Ka ce: "Shin makãho da mai gani sunã daidaita?
Kõ shin duhu da haske sunã daidaita? ko sun sanya ga Allah waɗansu abõkan
tãrayya waɗanda suka yi halitta kamar halittarSa sa'an nan halittar ta yi kama
da jũna a gare su?" Ka ce: "Allah ne Mai halitta kõme kuma Shĩ ne Maɗaukaki,
Marinjãyi."
|
Ayah 13:17 الأية
أَنزَلَ مِنَ السَّمَاءِ مَاءً فَسَالَتْ أَوْدِيَةٌ بِقَدَرِهَا فَاحْتَمَلَ
السَّيْلُ زَبَدًا رَّابِيًا ۚ وَمِمَّا يُوقِدُونَ عَلَيْهِ فِي النَّارِ
ابْتِغَاءَ حِلْيَةٍ أَوْ مَتَاعٍ زَبَدٌ مِّثْلُهُ ۚ كَذَٰلِكَ يَضْرِبُ اللهُ
الْحَقَّ وَالْبَاطِلَ ۚ فَأَمَّا الزَّبَدُ فَيَذْهَبُ جُفَاءً ۖ وَأَمَّا مَا
يَنفَعُ النَّاسَ فَيَمْكُثُ فِي الْأَرْضِ ۚ كَذَٰلِكَ يَضْرِبُ اللهُ
الْأَمْثَالَ
Anzala mina assama-i maanfasalat awdiyatun biqadariha fahtamalaassaylu zabadan
rabiyan wamimma yooqidoonaAAalayhi fee annari ibtighaa hilyatinaw mataAAin
zabadun mithluhu kathalika yadribuAllahu alhaqqa walbatila faammaazzabadu
fayathhabu jufaan waamma mayanfaAAu annasa fayamkuthu fee al-ardi
kathalikayadribu Allahu al-amthal
Hausa
Ya saukar da ruwa daga sama , sai magudanai suka gudãna da gwargwadonsu, Sa'an
nan kõgi ya ɗauki kumfa mai ƙãruwa, kuma daga abin da suke zuga a kansa (azurfa
ko zinari kõ ƙarfe) a cikin wuta dõmin nẽman ado kõ kuwa kãyan ɗãki akwai kumfa
misãlinsa (kumfar ruwa). Kamar wancan ne Allah Yake bayyana gaskiya da ƙarya.
To, amma kumfa, sai ya tafi ƙẽƙasasshe, kumaamma abin da yake amfãnin mutãne sai
ya zauna a cikin ƙasa. Kamar wancan ne Allah Yake bayyana misãlai.
|
Ayah 13:18 الأية
لِلَّذِينَ اسْتَجَابُوا لِرَبِّهِمُ الْحُسْنَىٰ ۚ وَالَّذِينَ لَمْ يَسْتَجِيبُوا
لَهُ لَوْ أَنَّ لَهُم مَّا فِي الْأَرْضِ جَمِيعًا وَمِثْلَهُ مَعَهُ لَافْتَدَوْا
بِهِ ۚ أُولَٰئِكَ لَهُمْ سُوءُ الْحِسَابِ وَمَأْوَاهُمْ جَهَنَّمُ ۖ وَبِئْسَ
الْمِهَادُ
Lillatheena istajaboolirabbihimu alhusna wallatheena lamyastajeeboo lahu law
anna lahum ma fee al-ardijameeAAan wamithlahu maAAahu laftadaw bihi ola-ikalahum
soo-o alhisabi wama/wahum jahannamuwabi/sa almihad
Hausa
Ga waɗanda suka karɓa wa Ubangijinsu akwai abu mafi kyau a gare su, kuma waɗanda
suke ba su karɓa Masa ba, to, lalle dã sunã da abin da yake a cikin ƙasa gaba
ɗaya da misãlinsa tãre da shi, haƙĩƙa, dã sun yi fansa da shi. Waɗancan sunã da
mummunan bincike kuma matabbatarsu Jahannama ce, kuma tir da ita ta zama
shimfida.
|
Ayah 13:19 الأية
أَفَمَن يَعْلَمُ أَنَّمَا أُنزِلَ إِلَيْكَ مِن رَّبِّكَ الْحَقُّ كَمَنْ هُوَ
أَعْمَىٰ ۚ إِنَّمَا يَتَذَكَّرُ أُولُو الْأَلْبَابِ
Afaman yaAAlamu annama onzila ilaykamin rabbika alhaqqu kaman huwa aAAma
innamayatathakkaru oloo al-albab
Hausa
Shin, fa, wanda yake sanin cẽwa lalle abin da aka saukar zuwa gare ka daga
Ubangijinka ne gaskiya yanã zama kamar wanda yake makãho? Abin sani kawai masu
hankali sũ ke yin tunãni.
|
Ayah 13:20 الأية
الَّذِينَ يُوفُونَ بِعَهْدِ اللهِ وَلَا يَنقُضُونَ الْمِيثَاقَ
Allatheena yoofoona biAAahdi Allahiwala yanqudoona almeethaq
Hausa
Sũ ne waɗanda suke cikãwa da alkawarin Allah, kuma bã su warware alkawari.
|
Ayah 13:21 الأية
وَالَّذِينَ يَصِلُونَ مَا أَمَرَ اللهُ بِهِ أَن يُوصَلَ وَيَخْشَوْنَ رَبَّهُمْ
وَيَخَافُونَ سُوءَ الْحِسَابِ
Wallatheena yasiloonama amara Allahu bihi an yoosala wayakhshawnarabbahum
wayakhafoona soo-a alhisab
Hausa
Kuma sũ ne waɗanda suke sãdar da abin da Allah Ya yi umurni da shi dõmin a sãdar
da shi kuma sunã tsõron Ubangijinsu, kuma sunã tsõron mummũnan bincike.
|
Ayah 13:22 الأية
وَالَّذِينَ صَبَرُوا ابْتِغَاءَ وَجْهِ رَبِّهِمْ وَأَقَامُوا الصَّلَاةَ
وَأَنفَقُوا مِمَّا رَزَقْنَاهُمْ سِرًّا وَعَلَانِيَةً وَيَدْرَءُونَ
بِالْحَسَنَةِ السَّيِّئَةَ أُولَٰئِكَ لَهُمْ عُقْبَى الدَّارِ
Wallatheena sabarooibtighaa wajhi rabbihim waaqamoo assalatawaanfaqoo mimma
razaqnahum sirran waAAalaniyatanwayadraoona bilhasanati assayyi-ata ola-ikalahum
AAuqba addar
Hausa
Kuma waɗanda suka yi haƙuri dõmin nẽman yardar Ubangijinsu, kuma suka tsayar da
salla,kuma suka ciyar da abin da Muka azurta su da shi, a asirce da bayyane,
kuma sunã tunkuɗe mummunan aiki da mai kyau. Waɗancan sunã da ãƙibar gida mai
kyau.
|
Ayah 13:23 الأية
جَنَّاتُ عَدْنٍ يَدْخُلُونَهَا وَمَن صَلَحَ مِنْ آبَائِهِمْ وَأَزْوَاجِهِمْ
وَذُرِّيَّاتِهِمْ ۖ وَالْمَلَائِكَةُ يَدْخُلُونَ عَلَيْهِم مِّن كُلِّ بَابٍ
Jannatu AAadnin yadkhuloonahawaman salaha min aba-ihim
waazwajihimwathurriyyatihim walmala-ikatuyadkhuloona AAalayhim min kulli bab
Hausa
Gidãjen Aljannar zama sunã shigarsu, sũ da waɗandasuka kyautatu daga iyãyensu,
da mãtansu da zũriyarsu. Kuma malã'iku sunã shiga zuwa gunsu ta kõwace kõfa.
|
Ayah 13:24 الأية
سَلَامٌ عَلَيْكُم بِمَا صَبَرْتُمْ ۚ فَنِعْمَ عُقْبَى الدَّارِ
Salamun AAalaykum bima sabartumfaniAAma AAuqba addar
Hausa
"Aminci ya tabbata a kanku sabõda abin da kuka yi wa haƙuri. Sãbõda haka madalla
da ni'imar ãƙibar gida."
|
Ayah 13:25 الأية
وَالَّذِينَ يَنقُضُونَ عَهْدَ اللهِ مِن بَعْدِ مِيثَاقِهِ وَيَقْطَعُونَ مَا
أَمَرَ اللهُ بِهِ أَن يُوصَلَ وَيُفْسِدُونَ فِي الْأَرْضِ ۙ أُولَٰئِكَ لَهُمُ
اللَّعْنَةُ وَلَهُمْ سُوءُ الدَّارِ
Wallatheena yanqudoonaAAahda Allahi min baAAdi meethaqihi wayaqtaAAoonama amara
Allahu bihi an yoosala wayufsidoonafee al-ardi ola-ika lahumu allaAAnatu walahum
soo-oaddar
Hausa
Kuma waɗanda suka warware alkawarin Allah daga bãyan ƙulla shi, kuma sunã yanke
abin da Allah Ya yi umurui da shi dõmin a sãdar da shi kuma sunã ɓarna a cikin
ƙasar. Waɗancan sunã da wata la'ana, kuma sunã da mũnin gida.
|
Ayah 13:26 الأية
اللهُ يَبْسُطُ الرِّزْقَ لِمَن يَشَاءُ وَيَقْدِرُ ۚ وَفَرِحُوا بِالْحَيَاةِ
الدُّنْيَا وَمَا الْحَيَاةُ الدُّنْيَا فِي الْآخِرَةِ إِلَّا مَتَاعٌ
Allahu yabsutu arrizqaliman yashao wayaqdiru wafarihoo bilhayatiaddunya wama
alhayatu addunyafee al-akhirati illa mataAA
Hausa
Allah ne Yake shimfiɗa arziki ga wanda Yake so, kuma Yanã ƙuntatãwa. Kuma sun yi
farin ciki da rãyuwar dũniya, alhalikuwa rãyuwar dũniya ba ta zama ba dangane ga
ta Lãhira fãce jin dãɗi kaɗan.
|
Ayah 13:27 الأية
وَيَقُولُ الَّذِينَ كَفَرُوا لَوْلَا أُنزِلَ عَلَيْهِ آيَةٌ مِّن رَّبِّهِ ۗ قُلْ
إِنَّ اللهَ يُضِلُّ مَن يَشَاءُ وَيَهْدِي إِلَيْهِ مَنْ أَنَابَ
Wayaqoolu allatheena kafaroo lawlaonzila AAalayhi ayatun min rabbihi qul inna
Allahayudillu man yashao wayahdee ilayhi man anab
Hausa
Kuma wanɗanda suka kãfirta, sunã cẽwa, "Don me ba a saukar da wata ãyã ba a
kansa daga Ubangijinsa?" Ka ce: "Lalle ne Allah Yanã ɓatar da wanda Yake so kuma
Yanã shiryar da wanda ya tũba zuwa gare shi."
|
Ayah 13:28 الأية
الَّذِينَ آمَنُوا وَتَطْمَئِنُّ قُلُوبُهُم بِذِكْرِ اللهِ ۗ أَلَا بِذِكْرِ
اللهِ تَطْمَئِنُّ الْقُلُوبُ
Allatheena amanoo watatma-innuquloobuhum bithikri Allahi ala bithikriAllahi
tatma-innu alquloob
Hausa
Waɗanda suka yi ĩmãni kuma zukãtansu sukan natsu da ambaton Allah. To, da
ambaton Allah zukãta suke natsuwa.
|
Ayah 13:29 الأية
الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ طُوبَىٰ لَهُمْ وَحُسْنُ مَآبٍ
Allatheena amanoo waAAamiloo assalihatitooba lahum wahusnu maab
Hausa
Waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata aiki nagari, farin ciki yã tabbata a
gare su, da kyakkyawar makõma.
|
Ayah 13:30 الأية
كَذَٰلِكَ أَرْسَلْنَاكَ فِي أُمَّةٍ قَدْ خَلَتْ مِن قَبْلِهَا أُمَمٌ لِّتَتْلُوَ
عَلَيْهِمُ الَّذِي أَوْحَيْنَا إِلَيْكَ وَهُمْ يَكْفُرُونَ بِالرَّحْمَٰنِ ۚ قُلْ
هُوَ رَبِّي لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ عَلَيْهِ تَوَكَّلْتُ وَإِلَيْهِ مَتَابِ
Kathalika arsalnaka feeommatin qad khalat min qabliha omamun litatluwa
AAalayhimuallathee awhayna ilayka wahum yakfuroona birrahmaniqul huwa rabbee la
ilaha illa huwa AAalayhitawakkaltu wa-ilayhi matab
Hausa
Kamar wancan ne Muka aika ka a cikin al'umma wanda take waɗansu al'ummai sun
shũɗe daga gabaninta, dõmin ka karanta musu abin da Muka yi wahayi zuwa a gare
ka, alhãli kuwa sũ, sunãkãfirta da Rahaman. Ka ce: "Shi ne Ubangijĩna, bãbu
abin, bautãwa fãce Shi, a gare Shi na dõgara, kuma zuwa gare Shi tũbãta take."
|
Ayah 13:31 الأية
وَلَوْ أَنَّ قُرْآنًا سُيِّرَتْ بِهِ الْجِبَالُ أَوْ قُطِّعَتْ بِهِ الْأَرْضُ
أَوْ كُلِّمَ بِهِ الْمَوْتَىٰ ۗ بَل لِّلَّهِ الْأَمْرُ جَمِيعًا ۗ أَفَلَمْ
يَيْأَسِ الَّذِينَ آمَنُوا أَن لَّوْ يَشَاءُ اللهُ لَهَدَى النَّاسَ جَمِيعًا ۗ
وَلَا يَزَالُ الَّذِينَ كَفَرُوا تُصِيبُهُم بِمَا صَنَعُوا قَارِعَةٌ أَوْ
تَحُلُّ قَرِيبًا مِّن دَارِهِمْ حَتَّىٰ يَأْتِيَ وَعْدُ اللهِ ۚ إِنَّ اللهَ
لَا يُخْلِفُ الْمِيعَادَ
Walaw anna qur-anan suyyirat bihialjibalu aw quttiAAat bihi al-ardu awkullima
bihi almawta bal lillahi al-amru jameeAAanafalam yay-asi allatheena amanoo an
law yashaoAllahu lahada annasa jameeAAan walayazalu allatheena kafaroo
tuseebuhum bimasanaAAoo qariAAatun aw tahullu qareeban mindarihim hatta ya/tiya
waAAdu Allahiinna Allaha la yukhlifu almeeAAad
Hausa
Kuma dã lalle an saukar da wani littafi abin karatu wanda ake tafiyar da duwãtsu
game da shi, kõ kuma aka yanyanke ƙasa da shi, ko kuwa aka yi magana da matattu
da shi (dã ba su yi ĩmãni ba). Ã'a ga Allah al'amari yake gabã ɗaya! Shin fa,
waɗanda suka yi ĩmãni ba su yanke tsammãni ba da cẽwa da Allah Yã so, dã Yã
shiryar da mutãne gabã ɗaya? Kuma waɗanda suka yi kãfirci ba zã su gushe ba wata
masĩfa tanã samun su sabõda abin da suka aikata, kõ kuwa ka saukã kusa da
gidãjẽnsu, har wa'adin Allah ya zo. Kuma lalle ne Allah bã ya sãɓã wa lõkacin
alkawari.
|
Ayah 13:32 الأية
وَلَقَدِ اسْتُهْزِئَ بِرُسُلٍ مِّن قَبْلِكَ فَأَمْلَيْتُ لِلَّذِينَ كَفَرُوا
ثُمَّ أَخَذْتُهُمْ ۖ فَكَيْفَ كَانَ عِقَابِ
Walaqadi istuhzi-a birusulin min qablikafaamlaytu lillatheena kafaroo thumma
akhathtuhumfakayfa kana AAiqab
Hausa
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an yi izgili da Manzanni kãfinka, sai Na yi jinkiri ga
waɗanda suka kãfirta, sa'an nan Na kãma su. To, yãya uƙũbãta take?
|
Ayah 13:33 الأية
أَفَمَنْ هُوَ قَائِمٌ عَلَىٰ كُلِّ نَفْسٍ بِمَا كَسَبَتْ ۗ وَجَعَلُوا لِلَّهِ
شُرَكَاءَ قُلْ سَمُّوهُمْ ۚ أَمْ تُنَبِّئُونَهُ بِمَا لَا يَعْلَمُ فِي الْأَرْضِ
أَم بِظَاهِرٍ مِّنَ الْقَوْلِ ۗ بَلْ زُيِّنَ لِلَّذِينَ كَفَرُوا مَكْرُهُمْ
وَصُدُّوا عَنِ السَّبِيلِ ۗ وَمَن يُضْلِلِ اللهُ فَمَا لَهُ مِنْ هَادٍ
Afaman huwa qa-imun AAalakulli nafsin bima kasabat wajaAAaloo lillahi
shurakaaqul sammoohum am tunabbi-oonahu bima la yaAAlamufee al-ardi am
bithahirin minaalqawli bal zuyyina lillatheena kafaroo makruhum wasuddooAAani
assabeeli waman yudlili Allahu famalahu min had
Hausa
Shin fa, wanda shĩ Yake tsaye a kan kõwane rai game da abin da ya tanada (zai
zama kamar wanda ba haka ba)? Kuma suka sanya abõkan tãrayya ga Allah! Ka ce:
"Ku ambaci sũnãyensu."Ko kunã bai wa Allah lãbãri ne game da abin da bai sani ba
a cikin ƙasa? Kõ da bayyananniyar magana kuke yin shirka, (banda a cikin
zũciya)? Ã'a, an dai ƙawãta wa waɗanda suka kafirta mãkircinsu kuma an kange su
daga hanya. Kuma wanda Allah Ya ɓatar to, bãbu wani mai shiryarwa a gare shi!"
|
Ayah 13:34 الأية
لَّهُمْ عَذَابٌ فِي الْحَيَاةِ الدُّنْيَا ۖ وَلَعَذَابُ الْآخِرَةِ أَشَقُّ ۖ
وَمَا لَهُم مِّنَ اللهِ مِن وَاقٍ
Lahum AAathabun fee alhayatiaddunya walaAAathabu al-akhiratiashaqqu wama lahum
mina Allahi min waq
Hausa
Sunã da wata azãba a cikin rãyuwar dũniya, kuma haƙĩƙa azãbar Lãhira ce mafi
tsanani kuma bãbu wani mai tsare su daga Allah.
|
Ayah 13:35 الأية
مَّثَلُ الْجَنَّةِ الَّتِي وُعِدَ الْمُتَّقُونَ ۖ تَجْرِي مِن تَحْتِهَا
الْأَنْهَارُ ۖ أُكُلُهَا دَائِمٌ وَظِلُّهَا ۚ تِلْكَ عُقْبَى الَّذِينَ اتَّقَوا
ۖ وَّعُقْبَى الْكَافِرِينَ النَّارُ
Mathalu aljannati allatee wuAAidaalmuttaqoona tajree min tahtiha
al-anharuokuluha da-imun wathilluhatilka AAuqba allatheena ittaqaw waAAuqba
alkafireenaannar
Hausa
Misãlin Aljanna wadda aka yi alkawarinta ga mãsu taƙawa, ƙõramu sunã gudãna daga
ƙarƙashinta. Abincinta yana madawwami da inuwarta. Waccan ce ãƙibar waɗanda suka
yi taƙawa, kuma ãƙibar kãfirai, ita ce wuta,
|
Ayah 13:36 الأية
وَالَّذِينَ آتَيْنَاهُمُ الْكِتَابَ يَفْرَحُونَ بِمَا أُنزِلَ إِلَيْكَ ۖ وَمِنَ
الْأَحْزَابِ مَن يُنكِرُ بَعْضَهُ ۚ قُلْ إِنَّمَا أُمِرْتُ أَنْ أَعْبُدَ اللهَ
وَلَا أُشْرِكَ بِهِ ۚ إِلَيْهِ أَدْعُو وَإِلَيْهِ مَآبِ
Wallatheena ataynahumualkitaba yafrahoona bima onzila ilaykawamina al-ahzabi man
yunkiru baAAdahu qulinnama omirtu an aAAbuda Allaha wala oshrikabihi ilayhi
adAAoo wa-ilayhi maab
Hausa
Kuma waɗanda Muka bã su Littãfi sunã farin ciki da abin da aka saukar zuwa gare
ka, kuma daga ƙungiyõyi akwai mai musun sãshensa. Ka ce: "Abin sani kawai, an
umurce ni da in bauta wa Allah kuma kada in yi shirka da Shi, zuwa gare Shi nake
kira, kuma zuwa gare Shi makõmata take."
|
Ayah 13:37 الأية
وَكَذَٰلِكَ أَنزَلْنَاهُ حُكْمًا عَرَبِيًّا ۚ وَلَئِنِ اتَّبَعْتَ أَهْوَاءَهُم
بَعْدَمَا جَاءَكَ مِنَ الْعِلْمِ مَا لَكَ مِنَ اللهِ مِن وَلِيٍّ وَلَا وَاقٍ
Wakathalika anzalnahu hukmanAAarabiyyan wala-ini ittabaAAta ahwaahum baAAda
majaaka mina alAAilmi ma laka mina Allahi minwaliyyin wala waq
Hausa
Kuma kamar wancan ne Muka saukar da shi, Hukunci a cikin Lãrabci. Kuma lalle ne
idan kã bi son zuciyõyinsu a bãyan abin da ya zo maka na ilmi, bãbu wani masõyi
a gare ka mai kãre ka daga Allah, kuma bãbu matsari.
|
Ayah 13:38 الأية
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا رُسُلًا مِّن قَبْلِكَ وَجَعَلْنَا لَهُمْ أَزْوَاجًا
وَذُرِّيَّةً ۚ وَمَا كَانَ لِرَسُولٍ أَن يَأْتِيَ بِآيَةٍ إِلَّا بِإِذْنِ
اللهِ ۗ لِكُلِّ أَجَلٍ كِتَابٌ
Walaqad arsalna rusulan min qablikawajaAAalna lahum azwajan wathurriyyatan
wamakana lirasoolin an ya/tiya bi-ayatin illabi-ithni Allahi likulli ajalin
kitab
Hausa
Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika waɗansu manzanni, daga gabãninka, kuma Muka sanya
mãtan aure a gare su da zũriyya, kuma ba ya kasancẽwa ga wani Manzo ya zo da
wata ãyã, sai da iznin Allah. Ga kõwane ajali akwai littãfi.
|
Ayah 13:39 الأية
يَمْحُو اللهُ مَا يَشَاءُ وَيُثْبِتُ ۖ وَعِندَهُ أُمُّ الْكِتَابِ
Yamhoo Allahu ma yashaowayuthbitu waAAindahu ommu alkitab
Hausa
Allah Yanã shafe abin da Yake so, kuma Yanã tabbatarwa kuma a wurinsa asalin
Littãfin yake.
|
Ayah 13:40 الأية
وَإِن مَّا نُرِيَنَّكَ بَعْضَ الَّذِي نَعِدُهُمْ أَوْ نَتَوَفَّيَنَّكَ
فَإِنَّمَا عَلَيْكَ الْبَلَاغُ وَعَلَيْنَا الْحِسَابُ
Wa-in ma nuriyannaka baAAdaallathee naAAiduhum aw natawaffayannaka
fa-innamaAAalayka albalaghu waAAalayna alhisab
Hausa
Kuma imma lalle Mu nũna maka sãshen abin da Muke yi musu wa'adi, kõ kuwa lalle
Mu karɓi ranka to abin sani kawai iyarwa ce a kanka, kuma hisãbi yana gare Mu.
|
Ayah 13:41 الأية
أَوَلَمْ يَرَوْا أَنَّا نَأْتِي الْأَرْضَ نَنقُصُهَا مِنْ أَطْرَافِهَا ۚ
وَاللهُ يَحْكُمُ لَا مُعَقِّبَ لِحُكْمِهِ ۚ وَهُوَ سَرِيعُ الْحِسَابِ
Awa lam yaraw anna na/tee al-ardananqusuha min atrafiha wallahuyahkumu la
muAAaqqiba lihukmihi wahuwasareeAAu alhisab
Hausa
Shin, kuma ba su gani ba cẽwa lalle ne, Muna jẽ wa ƙasar (su), Munã rage ta daga
gẽfunanta? Kuma Allah ne Yake yin hukuncinsa. Babu mai bincike ga hukuncinsa.
Kuma shĩ ne Mai gaggãwar sakamako.
|
Ayah 13:42 الأية
وَقَدْ مَكَرَ الَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ فَلِلَّهِ الْمَكْرُ جَمِيعًا ۖ يَعْلَمُ
مَا تَكْسِبُ كُلُّ نَفْسٍ ۗ وَسَيَعْلَمُ الْكُفَّارُ لِمَنْ عُقْبَى الدَّارِ
Waqad makara allatheena min qablihimfalillahi almakru jameeAAan yaAAlamu ma
taksibukullu nafsin wasayaAAlamu alkuffaru liman AAuqba addar
Hausa
Kuma lalle ne waɗanda suke a gabãninsu sun yi mãkirci. To, ga Allah mãkircin
yake gabã ɗaya. Ya san abin da kõwane rai yake tãnada. Kuma kãfirai zã su sani,
ga wane ãƙibar gida take.
|
Ayah 13:43 الأية
وَيَقُولُ الَّذِينَ كَفَرُوا لَسْتَ مُرْسَلًا ۚ قُلْ كَفَىٰ بِاللهِ شَهِيدًا
بَيْنِي وَبَيْنَكُمْ وَمَنْ عِندَهُ عِلْمُ الْكِتَابِ
Wayaqoolu allatheena kafaroo lastamursalan qul kafa billahi shaheedan
bayneewabaynakum waman AAindahu AAilmu alkitab
Hausa
Kuma waɗanda suka kãfirta sunã cẽwa: "Ba a aiko ka ba." Ka ce, "Allah Yã isa
zama shaida a tsakãnina da tsakãninku da wanda yake a wurinsa akwai ilmin
Littãfi."
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|