Prev  

80. Surah 'Abasa سورة عبس

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
عَبَسَ وَتَوَلَّىٰ
AAabasa watawalla

Hausa
 
Yã game huska kuma ya jũya bãya.

Ayah  80:2  الأية
أَن جَاءَهُ الْأَعْمَىٰ
An jaahu al-aAAma

Hausa
 
Sabõda makãho yã je masa.

Ayah  80:3  الأية
وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُ يَزَّكَّىٰ
Wama yudreeka laAAallahu yazzakka

Hausa
 
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

Ayah  80:4  الأية
أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ الذِّكْرَىٰ
Aw yaththakkaru fatanfaAAahu aththikra

Hausa
 
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

Ayah  80:5  الأية
أَمَّا مَنِ اسْتَغْنَىٰ
Amma mani istaghna

Hausa
 
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

Ayah  80:6  الأية
فَأَنتَ لَهُ تَصَدَّىٰ
Faanta lahu tasadda

Hausa
 
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

Ayah  80:7  الأية
وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ
Wama AAalayka alla yazzakka

Hausa
 
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

Ayah  80:8  الأية
وَأَمَّا مَن جَاءَكَ يَسْعَىٰ
Waamma man jaaka yasAAa

Hausa
 
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

Ayah  80:9  الأية
وَهُوَ يَخْشَىٰ
Wahuwa yakhsha

Hausa
 
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

Ayah  80:10  الأية
فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ
Faanta AAanhu talahha

Hausa
 
Kai kuma kã shagala ga barinsa!

Ayah  80:11  الأية
كَلَّا إِنَّهَا تَذْكِرَةٌ
Kalla innaha tathkira

Hausa
 
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

Ayah  80:12  الأية
فَمَن شَاءَ ذَكَرَهُ
Faman shaa thakarah

Hausa
 
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

Ayah  80:13  الأية
فِي صُحُفٍ مُّكَرَّمَةٍ
Fee suhufin mukarrama

Hausa
 
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

Ayah  80:14  الأية
مَّرْفُوعَةٍ مُّطَهَّرَةٍ
MarfooAAatin mutahhara

Hausa
 
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

Ayah  80:15  الأية
بِأَيْدِي سَفَرَةٍ
Bi-aydee safara

Hausa
 
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

Ayah  80:16  الأية
كِرَامٍ بَرَرَةٍ
Kiramin barara

Hausa
 
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

Ayah  80:17  الأية
قُتِلَ الْإِنسَانُ مَا أَكْفَرَهُ
Qutila al-insanu ma akfarah

Hausa
 
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

Ayah  80:18  الأية
مِنْ أَيِّ شَيْءٍ خَلَقَهُ
Min ayyi shay-in khalaqah

Hausa
 
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

Ayah  80:19  الأية
مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُ فَقَدَّرَهُ
Min nutfatin khalaqahu faqaddarah

Hausa
 
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

Ayah  80:20  الأية
ثُمَّ السَّبِيلَ يَسَّرَهُ
Thumma assabeela yassarah

Hausa
 
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

Ayah  80:21  الأية
ثُمَّ أَمَاتَهُ فَأَقْبَرَهُ
Thumma amatahu faaqbarah

Hausa
 
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

Ayah  80:22  الأية
ثُمَّ إِذَا شَاءَ أَنشَرَهُ
Thumma itha shaa ansharah

Hausa
 
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

Ayah  80:23  الأية
كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَا أَمَرَهُ
Kalla lamma yaqdi maamarah

Hausa
 
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

Ayah  80:24  الأية
فَلْيَنظُرِ الْإِنسَانُ إِلَىٰ طَعَامِهِ
Falyanthuri al-insanuila taAAamih

Hausa
 
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

Ayah  80:25  الأية
أَنَّا صَبَبْنَا الْمَاءَ صَبًّا
Anna sababna almaasabba

Hausa
 
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

Ayah  80:26  الأية
ثُمَّ شَقَقْنَا الْأَرْضَ شَقًّا
Thumma shaqaqna al-arda shaqqa

Hausa
 
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

Ayah  80:27  الأية
فَأَنبَتْنَا فِيهَا حَبًّا
Faanbatna feeha habba

Hausa
 
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya ,a cikinta.

Ayah  80:28  الأية
وَعِنَبًا وَقَضْبًا
WaAAinaban waqadba

Hausa
 
Da inabi da ciyãwa.

Ayah  80:29  الأية
وَزَيْتُونًا وَنَخْلًا
Wazaytoonan wanakhla

Hausa
 
Da zaitũni da itãcen dabĩno.

Ayah  80:30  الأية
وَحَدَائِقَ غُلْبًا
Wahada-iqa ghulba

Hausa
 
Da lambuna, mãsu yawan itãce.

Ayah  80:31  الأية
وَفَاكِهَةً وَأَبًّا
Wafakihatan waabba

Hausa
 
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

Ayah  80:32  الأية
مَّتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ
MataAAan lakum wali-anAAamikum

Hausa
 
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

Ayah  80:33  الأية
فَإِذَا جَاءَتِ الصَّاخَّةُ
Fa-itha jaati assakhkha

Hausa
 
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

Ayah  80:34  الأية
يَوْمَ يَفِرُّ الْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ
Yawma yafirru almaro min akheeh

Hausa
 
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

Ayah  80:35  الأية
وَأُمِّهِ وَأَبِيهِ
Waommihi waabeeh

Hausa
 
Da uwarsa da ubansa.

Ayah  80:36  الأية
وَصَاحِبَتِهِ وَبَنِيهِ
Wasahibatihi wabaneeh

Hausa
 
Da mãtarsa da ɗiyansa.

Ayah  80:37  الأية
لِكُلِّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍ شَأْنٌ يُغْنِيهِ
Likulli imri-in minhum yawma-ithinsha/nun yughneeh

Hausa
 
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

Ayah  80:38  الأية
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ مُّسْفِرَةٌ
Wujoohun yawma-ithin musfira

Hausa
 
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

Ayah  80:39  الأية
ضَاحِكَةٌ مُّسْتَبْشِرَةٌ
Dahikatun mustabshira

Hausa
 
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

Ayah  80:40  الأية
وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌ
Wawujoohun yawma-ithin AAalayhaghabara

Hausa
 
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

Ayah  80:41  الأية
تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ
Tarhaquha qatara

Hausa
 
Baƙi zai rufe su.

Ayah  80:42  الأية
أُولَٰئِكَ هُمُ الْكَفَرَةُ الْفَجَرَةُ
Ola-ika humu alkafaratu alfajara

Hausa
 
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu). 




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us