Prev
86. Surah At-Târiq سورة الطارق
Next
1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَالسَّمَاءِ وَالطَّارِقِ
Wassama-i wattariq
Hausa
Inã rantsuwa da sama da mai aukõwa da dare.
|
Ayah 86:2 الأية
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الطَّارِقُ
Wama adraka ma attariq
Hausa
To, mẽ yã sanar da kai abin da ake cẽwa mai aukõwa da dare?
|
Ayah 86:3 الأية
النَّجْمُ الثَّاقِبُ
Annajmu aththaqib
Hausa
Shi ne taurãron nan mai tsananin haske.
|
Ayah 86:4 الأية
إِن كُلُّ نَفْسٍ لَّمَّا عَلَيْهَا حَافِظٌ
In kullu nafsin lamma AAalayha hafith
Hausa
Bãbu wani rai fãce a kansa akwai wani mai tsaro.
|
Ayah 86:5 الأية
فَلْيَنظُرِ الْإِنسَانُ مِمَّ خُلِقَ
Falyanthuri al-insanumimma khuliq
Hausa
To, mutum ya dũba, daga mẽ aka halittã shi?
|
Ayah 86:6 الأية
خُلِقَ مِن مَّاءٍ دَافِقٍ
Khuliqa min ma-in dafiq
Hausa
An halittã shi daga wani ruwa mai tunkuɗar jũna.
|
Ayah 86:7 الأية
يَخْرُجُ مِن بَيْنِ الصُّلْبِ وَالتَّرَائِبِ
Yakhruju min bayni assulbi wattara-ib
Hausa
Yanã fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji.
|
Ayah 86:8 الأية
إِنَّهُ عَلَىٰ رَجْعِهِ لَقَادِرٌ
Innahu AAala rajAAihi laqadir
Hausa
Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyãwa ne.
|
Ayah 86:9 الأية
يَوْمَ تُبْلَى السَّرَائِرُ
Yawma tubla assara-ir
Hausa
Rãnar da ake jarrabawar asirai.
|
Ayah 86:10 الأية
فَمَا لَهُ مِن قُوَّةٍ وَلَا نَاصِرٍ
Fama lahu min quwwatin wala nasir
Hausa
Saboda haka, bã shi da wani ƙarfi, kuma bã shi da wani mai taimako (da zai iya
kãre shi daga azãbar Allah).
|
Ayah 86:11 الأية
وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الرَّجْعِ
Wassama-i thati arrajAA
Hausa
Ina rantsuwa da sama ma'abũciyar ruwa mai kõmãwa yana yankẽwa.
|
Ayah 86:12 الأية
وَالْأَرْضِ ذَاتِ الصَّدْعِ
Wal-ardi thati assadAA
Hausa
Da ƙasa ma'abũciyar tsãgẽwa,
|
Ayah 86:13 الأية
إِنَّهُ لَقَوْلٌ فَصْلٌ
Innahu laqawlun fasl
Hausa
Lalle ne shĩ (Alƙur'ãni), haƙĩƙa magana ce daki-daki
|
Ayah 86:14 الأية
وَمَا هُوَ بِالْهَزْلِ
Wama huwa bilhazl
Hausa
Kuma shĩ bã bananci bane
|
Ayah 86:15 الأية
إِنَّهُمْ يَكِيدُونَ كَيْدًا
Innahum yakeedoona kayda
Hausa
Lalle ne sũ, suna ƙulla kaidi na sõsai.
|
Ayah 86:16 الأية
وَأَكِيدُ كَيْدًا
Waakeedu kayda
Hausa
Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi.
|
Ayah 86:17 الأية
فَمَهِّلِ الْكَافِرِينَ أَمْهِلْهُمْ رُوَيْدًا
Famahhili alkafireena amhilhum ruwayda
Hausa
Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|
|