« Prev

42. Surah Ash-Shűra سورة الشورى

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
حم
Hausa
 
Ḥ. M̃.

Ayah   42:2   الأية
عسق
Hausa
 
Ĩ. Ṣ̃.

Ayah   42:3   الأية
كَذَٰلِكَ يُوحِي إِلَيْكَ وَإِلَى الَّذِينَ مِن قَبْلِكَ اللَّهُ الْعَزِيزُ الْحَكِيمُ
Hausa
 
Kamar wancăn (asĩrin) Allah, Mabuwayi, Mai hikima, ke yin wahayi zuwa gare ka da zuwa ga waɗanda ke gabăninka .

Ayah   42:4   الأية
لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ ۖ وَهُوَ الْعَلِيُّ الْعَظِيمُ
Hausa
 
(Allah) Shi ne da abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa, kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma.

Ayah   42:5   الأية
تَكَادُ السَّمَاوَاتُ يَتَفَطَّرْنَ مِن فَوْقِهِنَّ ۚ وَالْمَلَائِكَةُ يُسَبِّحُونَ بِحَمْدِ رَبِّهِمْ وَيَسْتَغْفِرُونَ لِمَن فِي الْأَرْضِ ۗ أَلَا إِنَّ اللَّهَ هُوَ الْغَفُورُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
Sammai nă kusan su tsăge daga bisansu, kuma mală'iku nă yin tasĩhi game da gődẽ wa Ubangijinsu kuma sună istigfări dőmin wanda ke cikin ƙasa. To, lalle Allah Shĩ ne Mai găfara, Mai jin ƙai.

Ayah   42:6   الأية
وَالَّذِينَ اتَّخَذُوا مِن دُونِهِ أَوْلِيَاءَ اللَّهُ حَفِيظٌ عَلَيْهِمْ وَمَا أَنتَ عَلَيْهِم بِوَكِيلٍ
Hausa
 
Kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majiɓinta waɗanda bă Shĩ ba Allah ne Mai tsaro a kansu, kuma kai, bă wakili ne a kansu ba.

Ayah   42:7   الأية
وَكَذَٰلِكَ أَوْحَيْنَا إِلَيْكَ قُرْآنًا عَرَبِيًّا لِّتُنذِرَ أُمَّ الْقُرَىٰ وَمَنْ حَوْلَهَا وَتُنذِرَ يَوْمَ الْجَمْعِ لَا رَيْبَ فِيهِ ۚ فَرِيقٌ فِي الْجَنَّةِ وَفَرِيقٌ فِي السَّعِيرِ
Hausa
 
Kuma kamar haka ne Muka yi wahayin abin karăntăwa (Alƙur'ăni) na Lărabci zuwa gare ka, dőmin ka yi gargaɗi ga Uwar Alƙaryu (Makka) da wanda ke a kẽwayenta, kuma ka yi gargaɗi game da rănar taruwa, băbu shakka gare ta, wata ƙungiya tană a cikin Aljanna kuma wata ƙungiya tăna a cikin sa'ĩr.

Ayah   42:8   الأية
وَلَوْ شَاءَ اللَّهُ لَجَعَلَهُمْ أُمَّةً وَاحِدَةً وَلَٰكِن يُدْخِلُ مَن يَشَاءُ فِي رَحْمَتِهِ ۚ وَالظَّالِمُونَ مَا لَهُم مِّن وَلِيٍّ وَلَا نَصِيرٍ
Hausa
 
Kuma dă Allah Ya so, da Ya haɗă su al'umma guda, kuma Amma Yană shigar da wanda Ya so a cikin rahamarSa alhăli kuwa azzăluMai bă su da, wani majiɓinci, kuma bă su da wani mataimaki.

Ayah   42:9   الأية
أَمِ اتَّخَذُوا مِن دُونِهِ أَوْلِيَاءَ ۖ فَاللَّهُ هُوَ الْوَلِيُّ وَهُوَ يُحْيِي الْمَوْتَىٰ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ
Hausa
 
Kő kuma sun riƙi waninSa majiɓinta? To Allah Shĩ ne Majiɓinci, kuma Shĩ ne ke răyar da matattu alhăli kuwa Shĩ, Maiĩkon yi ne a kan dukan kőme.

Ayah   42:10   الأية
وَمَا اخْتَلَفْتُمْ فِيهِ مِن شَيْءٍ فَحُكْمُهُ إِلَى اللَّهِ ۚ ذَٰلِكُمُ اللَّهُ رَبِّي عَلَيْهِ تَوَكَّلْتُ وَإِلَيْهِ أُنِيبُ
Hausa
 
Kuma abin da kuka săɓă wa jũna a cikinsa kő męne ne, to, hukuncinsa (a mayar da shi) zuwa ga Allah. Wancan Shĩ ne Allah Ubangijĩna, a gare Shi na dőgara, kuma zuwa gare Shi nake mayar da al'amarĩna.

Ayah   42:11   الأية
فَاطِرُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ جَعَلَ لَكُم مِّنْ أَنفُسِكُمْ أَزْوَاجًا وَمِنَ الْأَنْعَامِ أَزْوَاجًا ۖ يَذْرَؤُكُمْ فِيهِ ۚ لَيْسَ كَمِثْلِهِ شَيْءٌ ۖ وَهُوَ السَّمِيعُ الْبَصِيرُ
Hausa
 
(Shĩ ne) Mai ƙăga halittar sammai da ƙasa, Ya sanya muku ma'aura daga jinsinku, kuma (Ya sanya) daga dabbőbi maza da mătă, Yană halitta ku a cikinsu, wani abu bai zama kamar tamkarSa ba, kuma Shĩ ne Mai ji, Mai gani.

Ayah   42:12   الأية
لَهُ مَقَالِيدُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۖ يَبْسُطُ الرِّزْقَ لِمَن يَشَاءُ وَيَقْدِرُ ۚ إِنَّهُ بِكُلِّ شَيْءٍ عَلِيمٌ
Hausa
 
Shĩ ne da mabuɗan sammai da ƙasa Yană shimfiɗa arziki ga wanda ya so kuma Yană hukuntăwa. Lalle ne, Shĩ Masani ne ga dukan kőme.

Ayah   42:13   الأية
شَرَعَ لَكُم مِّنَ الدِّينِ مَا وَصَّىٰ بِهِ نُوحًا وَالَّذِي أَوْحَيْنَا إِلَيْكَ وَمَا وَصَّيْنَا بِهِ إِبْرَاهِيمَ وَمُوسَىٰ وَعِيسَىٰ ۖ أَنْ أَقِيمُوا الدِّينَ وَلَا تَتَفَرَّقُوا فِيهِ ۚ كَبُرَ عَلَى الْمُشْرِكِينَ مَا تَدْعُوهُمْ إِلَيْهِ ۚ اللَّهُ يَجْتَبِي إِلَيْهِ مَن يَشَاءُ وَيَهْدِي إِلَيْهِ مَن يُنِيبُ
Hausa
 
Ya shar'anta muku, game da addini, abin da Ya yi wasiyya da shi ga Nũhu da abin da Muka yi wahayi da shi zuwa gare ka, da abin da Muka yi wasiyya da shi ga Ibrăhĩm da Mũsă da Ĩsă, cẽwa ku tsayar da addini sősai kuma kada ku rarrabu a cikinsa. Abin da kuke kira zuwa gare shi, ya yi nauyi a kan măsu shirki. Allah na zăɓen wanda Yake so zuwa gare Shi, kuma Yană shiryar da wanda ke tawakkali gare Shi, ga hanyarSa.

Ayah   42:14   الأية
وَمَا تَفَرَّقُوا إِلَّا مِن بَعْدِ مَا جَاءَهُمُ الْعِلْمُ بَغْيًا بَيْنَهُمْ ۚ وَلَوْلَا كَلِمَةٌ سَبَقَتْ مِن رَّبِّكَ إِلَىٰ أَجَلٍ مُّسَمًّى لَّقُضِيَ بَيْنَهُمْ ۚ وَإِنَّ الَّذِينَ أُورِثُوا الْكِتَابَ مِن بَعْدِهِمْ لَفِي شَكٍّ مِّنْهُ مُرِيبٍ
Hausa
 
Kuma ba su rarraba ba făce băyan da ilmi ya jẽ musu, dőmin zălunci a tsakăninsu kuma bă dőmin wata kalma tă gabata ba daga Ubangijinka, zuwa ga wani ajali ambatacce, dă an yi hukunci a tsakaninsu. Kuma lalle ne waɗanda aka gădar wa Littafi daga băyansu, haƙiƙa, sună cikin shakka a gare shi, mai sanya kokanto.

Ayah   42:15   الأية
فَلِذَٰلِكَ فَادْعُ ۖ وَاسْتَقِمْ كَمَا أُمِرْتَ ۖ وَلَا تَتَّبِعْ أَهْوَاءَهُمْ ۖ وَقُلْ آمَنتُ بِمَا أَنزَلَ اللَّهُ مِن كِتَابٍ ۖ وَأُمِرْتُ لِأَعْدِلَ بَيْنَكُمُ ۖ اللَّهُ رَبُّنَا وَرَبُّكُمْ ۖ لَنَا أَعْمَالُنَا وَلَكُمْ أَعْمَالُكُمْ ۖ لَا حُجَّةَ بَيْنَنَا وَبَيْنَكُمُ ۖ اللَّهُ يَجْمَعُ بَيْنَنَا ۖ وَإِلَيْهِ الْمَصِيرُ
Hausa
 
Sabőda haka, sai ka yi kira kuma kai ka daidaitu kamar yadda aka umurce ka, kuma kada ka bi son zũciyőyinsu, kumaka ce, "Nă yi ĩmăni da abin da Allah Ya saukar na littăfi, kuma an umurce ni da in yi ădalci a tsakăninku. Allah ne Ubangijinmu, kuma Shĩ ne Ubangijinku, ayyukanmu nă gare mu, kuma ayyukanku nă gare ku, kuma băbu wata hujja a tsakăninmu da tsakăninku. Allah zai tara mu, kuma zuwa gare Shi makőma take."

Ayah   42:16   الأية
وَالَّذِينَ يُحَاجُّونَ فِي اللَّهِ مِن بَعْدِ مَا اسْتُجِيبَ لَهُ حُجَّتُهُمْ دَاحِضَةٌ عِندَ رَبِّهِمْ وَعَلَيْهِمْ غَضَبٌ وَلَهُمْ عَذَابٌ شَدِيدٌ
Hausa
 
Kuma waɗannan da ke jăyayya a cikin al'amarin Allah daga băyan an karɓa masa, hujjarsu ɓătăcciya ce a wurin Ubangijinsu, kuma akwai fushi a kansu, kuma sună da wata azăba mai tsanani.

Ayah   42:17   الأية
اللَّهُ الَّذِي أَنزَلَ الْكِتَابَ بِالْحَقِّ وَالْمِيزَانَ ۗ وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّ السَّاعَةَ قَرِيبٌ
Hausa
 
Allah ne Wanda Ya saukar da Littăfi da gaskiya, da sikeli. Kuma me ya sanar da kai (cẽwa ană) tsammănin Sa'ar kusa take?

Ayah   42:18   الأية
يَسْتَعْجِلُ بِهَا الَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِهَا ۖ وَالَّذِينَ آمَنُوا مُشْفِقُونَ مِنْهَا وَيَعْلَمُونَ أَنَّهَا الْحَقُّ ۗ أَلَا إِنَّ الَّذِينَ يُمَارُونَ فِي السَّاعَةِ لَفِي ضَلَالٍ بَعِيدٍ
Hausa
 
Waɗanda ba su yi ĩmănida ita ba, (sũ) ke nẽman gaggautőwarta. Alhăli kuwa waɗanda suka yi ĩmăni, măsu tsőro ne daga gare ta, kuma sun sani, cẽwa ita gaskiya ce. To, lalle ne waɗanda ke shakka a cikin Sa'a, haƙĩƙa,sună a cikin ɓata Mai nĩsa.

Ayah   42:19   الأية
اللَّهُ لَطِيفٌ بِعِبَادِهِ يَرْزُقُ مَن يَشَاءُ ۖ وَهُوَ الْقَوِيُّ الْعَزِيزُ
Hausa
 
Allah Mai tausasăwa ne ga băyinsa. Yană azurta wanda yake so, alhăli kuma Shĩ ne Maiƙarfi, Mabuwăyi.

Ayah   42:20   الأية
مَن كَانَ يُرِيدُ حَرْثَ الْآخِرَةِ نَزِدْ لَهُ فِي حَرْثِهِ ۖ وَمَن كَانَ يُرِيدُ حَرْثَ الدُّنْيَا نُؤْتِهِ مِنْهَا وَمَا لَهُ فِي الْآخِرَةِ مِن نَّصِيبٍ
Hausa
 
Wanda ya kasance yană nufin nőman Lăhira ză Mu ƙăra masa a cikin nőmansa, kuma wanda ya kasance yană nufin nőman dũniya, ză Mu sam masa daga gare ta, alhăli kuwa bă shi da wani rabo a cikin Lăhira.

Ayah   42:21   الأية
أَمْ لَهُمْ شُرَكَاءُ شَرَعُوا لَهُم مِّنَ الدِّينِ مَا لَمْ يَأْذَن بِهِ اللَّهُ ۚ وَلَوْلَا كَلِمَةُ الْفَصْلِ لَقُضِيَ بَيْنَهُمْ ۗ وَإِنَّ الظَّالِمِينَ لَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ
Hausa
 
Kő sună da waɗansu abőkan tărayya (da Allah) waɗanda suka shar'anta musu, game da addini, abin da Allah bai yi izni ba da shi? Kuma bă dőmin kalmar hukunci ba, da lalle, an yi hukunci a tsakăninsu. Kuma lalle azzălumai sună da azăba mai raɗaɗi.

Ayah   42:22   الأية
تَرَى الظَّالِمِينَ مُشْفِقِينَ مِمَّا كَسَبُوا وَهُوَ وَاقِعٌ بِهِمْ ۗ وَالَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ فِي رَوْضَاتِ الْجَنَّاتِ ۖ لَهُم مَّا يَشَاءُونَ عِندَ رَبِّهِمْ ۚ ذَٰلِكَ هُوَ الْفَضْلُ الْكَبِيرُ
Hausa
 
Kană ganin azzălumai sună măsu tsőro daga abin da suka sană'anta alhăli kuwa shi abin tsoron, mai aukuwa ne gare su, kuma waɗanda suka yi ĩmăni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai sună a cikin fadamun Aljanna sună da abin da suke so a wurin Ubangijinsu. Waccan fa ita ce falala mai girma.

Ayah   42:23   الأية
ذَٰلِكَ الَّذِي يُبَشِّرُ اللَّهُ عِبَادَهُ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ ۗ قُل لَّا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ أَجْرًا إِلَّا الْمَوَدَّةَ فِي الْقُرْبَىٰ ۗ وَمَن يَقْتَرِفْ حَسَنَةً نَّزِدْ لَهُ فِيهَا حُسْنًا ۚ إِنَّ اللَّهَ غَفُورٌ شَكُورٌ
Hausa
 
Wancan shĩ ne Allah ke băyar da bushăra da shi ga băyinSa waɗanda suka yi ĩmăni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai. Ka ce: "Bă ni tambayar ku wata ijăra a kansa, făce dai sőyayya ta cikin zumunta." Kuma wanda ya aikata wani abu mai kyau, ză Mu ƙară masa kyau a cikinsa, lalle Allah Mai găfara ne, Mai gődiya.

Ayah   42:24   الأية
أَمْ يَقُولُونَ افْتَرَىٰ عَلَى اللَّهِ كَذِبًا ۖ فَإِن يَشَإِ اللَّهُ يَخْتِمْ عَلَىٰ قَلْبِكَ ۗ وَيَمْحُ اللَّهُ الْبَاطِلَ وَيُحِقُّ الْحَقَّ بِكَلِمَاتِهِ ۚ إِنَّهُ عَلِيمٌ بِذَاتِ الصُّدُورِ
Hausa
 
Kő ză su ce: "Ya ƙirƙira ƙarya ga Allah ne?" To, idan Allah Ya so, zai yunƙe a kan zũciyarka, kuma Allah Yana shăfe ƙarya kuma Yana tabbatar da gaskiya da kalmőminSa. Lalle ne Shĩ Masani ne ga abin da ke cikin zukata.

Ayah   42:25   الأية
وَهُوَ الَّذِي يَقْبَلُ التَّوْبَةَ عَنْ عِبَادِهِ وَيَعْفُو عَنِ السَّيِّئَاتِ وَيَعْلَمُ مَا تَفْعَلُونَ
Hausa
 
Kuma Shi ne ke karɓar tũba daga băyinSa, kuma Yană Yafe ƙananan laifuffuka, alhăli kuwa Yană sanin abin da kuke aikatăwa.

Ayah   42:26   الأية
وَيَسْتَجِيبُ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَيَزِيدُهُم مِّن فَضْلِهِ ۚ وَالْكَافِرُونَ لَهُمْ عَذَابٌ شَدِيدٌ
Hausa
 
Kuma Yană karɓa wa waɗannan da suka yi ĩmăni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma Yană ƙăra musu (sakamako) daga falalarSa. Kuma kăfirai sună da wata azăba mai tsanani.

Ayah   42:27   الأية
وَلَوْ بَسَطَ اللَّهُ الرِّزْقَ لِعِبَادِهِ لَبَغَوْا فِي الْأَرْضِ وَلَٰكِن يُنَزِّلُ بِقَدَرٍ مَّا يَشَاءُ ۚ إِنَّهُ بِعِبَادِهِ خَبِيرٌ بَصِيرٌ
Hausa
 
Kuma dă Allah Ya shimfiɗa arziki ga băyinSa, dă sun yi zăluncin rarraba jama'a a cikin ƙasa, kuma amma Yană sassaukarwa gwargwado ga abin da Yake so. Lalle ne Shĩ, game da băyinSa, Mai labartawa ne, Mai gani.

Ayah   42:28   الأية
وَهُوَ الَّذِي يُنَزِّلُ الْغَيْثَ مِن بَعْدِ مَا قَنَطُوا وَيَنشُرُ رَحْمَتَهُ ۚ وَهُوَ الْوَلِيُّ الْحَمِيدُ
Hausa
 
Kuma Shĩ ne ke sassaukar da girgije (ruwa) a băyan sun yanke ƙauna kuma Yana wătsa rahamarSa, alhăli kuwa Shĩ ne Majiɓinci, Mai gődiya.

Ayah   42:29   الأية
وَمِنْ آيَاتِهِ خَلْقُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَثَّ فِيهِمَا مِن دَابَّةٍ ۚ وَهُوَ عَلَىٰ جَمْعِهِمْ إِذَا يَشَاءُ قَدِيرٌ
Hausa
 
Kuma akwai daga ăyőyinSa, halittar sammai da ƙasa da abin da Ya wătsa a cikinsu na dabba alhăli kuwa Shĩ Mai ĩko ne ga tăra su, a lőkacin da Yake so.

Ayah   42:30   الأية
وَمَا أَصَابَكُم مِّن مُّصِيبَةٍ فَبِمَا كَسَبَتْ أَيْدِيكُمْ وَيَعْفُو عَن كَثِيرٍ
Hausa
 
Kuma abin da ya săme ku na wata masifa, to, game da abin da hannăyenku suka sana' anta ne kuma (Alah) Yană Yafẽwar (waɗansu laifuffuka) măsu yawa.

Ayah   42:31   الأية
وَمَا أَنتُم بِمُعْجِزِينَ فِي الْأَرْضِ ۖ وَمَا لَكُم مِّن دُونِ اللَّهِ مِن وَلِيٍّ وَلَا نَصِيرٍ
Hausa
 
Kuma ba ku zama măsu buwăya ba a cikin ƙasa kuma bă ku da wani majiɓinci, wanin Allah, kuma bă ku da wani mataimaki.

Ayah   42:32   الأية
وَمِنْ آيَاتِهِ الْجَوَارِ فِي الْبَحْرِ كَالْأَعْلَامِ
Hausa
 
Kuma akwai daga ăyőyinsa, jirăge măsu gudăna a cikin tẽku kamar duwătsu.

Ayah   42:33   الأية
إِن يَشَأْ يُسْكِنِ الرِّيحَ فَيَظْلَلْنَ رَوَاكِدَ عَلَىٰ ظَهْرِهِ ۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَاتٍ لِّكُلِّ صَبَّارٍ شَكُورٍ
Hausa
 
Idan Ya so, sai Ya kwantar da iskar, sai jirăgen su yini sună măsu kawaici a kan băyan tẽkun,Lalle ne ga wancan, haƙĩƙa, akwai ăyőyi ga dukan mai haƙuri, Mai gődiya.

Ayah   42:34   الأية
أَوْ يُوبِقْهُنَّ بِمَا كَسَبُوا وَيَعْفُ عَن كَثِيرٍ
Hausa
 
Kő Ya halakă su (sũ jirăgen) sabőda abin da măsu su suka sană'anta, alhăli kuwa Yană yăfe (laifuffuka) măsu yawa.

Ayah   42:35   الأية
وَيَعْلَمَ الَّذِينَ يُجَادِلُونَ فِي آيَاتِنَا مَا لَهُم مِّن مَّحِيصٍ
Hausa
 
Kuma dőmin waɗanda ke jăyayya a cikin ăyőyinMu su sani (cẽwa) bă su da wata mafaka.

Ayah   42:36   الأية
فَمَا أُوتِيتُم مِّن شَيْءٍ فَمَتَاعُ الْحَيَاةِ الدُّنْيَا ۖ وَمَا عِندَ اللَّهِ خَيْرٌ وَأَبْقَىٰ لِلَّذِينَ آمَنُوا وَعَلَىٰ رَبِّهِمْ يَتَوَكَّلُونَ
Hausa
 
Sabőda haka abin da aka bă ku, kő mẽne ne, to, jin dăɗin rayuwar dũniya ne, kuma abin da ke a wurin Allah Shĩ ne mafĩfĩci,kuma Shĩ ne mafi wanzuwa ga waɗanda suka yi ĩmăni kuma sună dőgara a kan Ubangijinsu kawai.

Ayah   42:37   الأية
وَالَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَائِرَ الْإِثْمِ وَالْفَوَاحِشَ وَإِذَا مَا غَضِبُوا هُمْ يَغْفِرُونَ
Hausa
 
Kuma waɗanda ke nisantar manyan zunubbai da ayyukan alfăsha, kuma idan sun yi fushi, sũ, sună găfartawa.

Ayah   42:38   الأية
وَالَّذِينَ اسْتَجَابُوا لِرَبِّهِمْ وَأَقَامُوا الصَّلَاةَ وَأَمْرُهُمْ شُورَىٰ بَيْنَهُمْ وَمِمَّا رَزَقْنَاهُمْ يُنفِقُونَ
Hausa
 
Da waɗanda suka karɓa kira ga Ubangijinsu, kuma suka tsayar da salla, kuma al'amarinsu shăwara ne a tsakăninsu, kuma daga abin da Muka azurta su sună ciyarwa.

Ayah   42:39   الأية
وَالَّذِينَ إِذَا أَصَابَهُمُ الْبَغْيُ هُمْ يَنتَصِرُونَ
Hausa
 
Da waɗanda idan zălunci ya săme su, sună nẽman taimako (su răma).

Ayah   42:40   الأية
وَجَزَاءُ سَيِّئَةٍ سَيِّئَةٌ مِّثْلُهَا ۖ فَمَنْ عَفَا وَأَصْلَحَ فَأَجْرُهُ عَلَى اللَّهِ ۚ إِنَّهُ لَا يُحِبُّ الظَّالِمِينَ
Hausa
 
Kuma sakamakon cũta shĩ ne wata cũta kamarta, sai dai wanda Ya yăfe kuma ya kyautata, to lădarsa nă ga Allah. Lalle ne, Shĩ (Allah) bă Ya son azzălumai.

Ayah   42:41   الأية
وَلَمَنِ انتَصَرَ بَعْدَ ظُلْمِهِ فَأُولَٰئِكَ مَا عَلَيْهِم مِّن سَبِيلٍ
Hausa
 
Kuma Lalle ne, wanda ya nẽmi taimakon rămăwa a băyan an zălunce shi, to waɗannan băbu wata hanyar zargi a kansu.

Ayah   42:42   الأية
إِنَّمَا السَّبِيلُ عَلَى الَّذِينَ يَظْلِمُونَ النَّاسَ وَيَبْغُونَ فِي الْأَرْضِ بِغَيْرِ الْحَقِّ ۚ أُولَٰئِكَ لَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ
Hausa
 
lnda hanyar zargi kawai take, shĩ ne a kan waɗanda ke zăluntar mutăne kuma sună ƙẽtare haddin shari'a cikin ƙasa bă tare da haƙƙi ba. Waɗannan sună da azăba Mai raɗaɗi.

Ayah   42:43   الأية
وَلَمَن صَبَرَ وَغَفَرَ إِنَّ ذَٰلِكَ لَمِنْ عَزْمِ الْأُمُورِ
Hausa
 
Kuma Lalle ne, wanda ya yi haƙuri kuma ya găfarta (wa wanda ya zălunce shi), to shĩ wancan aiki haƙĩƙa, yană daga manyan al'amura (da Allah ke so).

Ayah   42:44   الأية
وَمَن يُضْلِلِ اللَّهُ فَمَا لَهُ مِن وَلِيٍّ مِّن بَعْدِهِ ۗ وَتَرَى الظَّالِمِينَ لَمَّا رَأَوُا الْعَذَابَ يَقُولُونَ هَلْ إِلَىٰ مَرَدٍّ مِّن سَبِيلٍ
Hausa
 
Kuma wanda (Allah Ya ɓatar, to, bă shi da wani majiɓinci băyanSa, kuma ză ka ga azzălumai, a lőkacin da suka ga azăba, sună cẽwa, "Shin, akwai hanya zuwa ga kőmăwa?"

Ayah   42:45   الأية
وَتَرَاهُمْ يُعْرَضُونَ عَلَيْهَا خَاشِعِينَ مِنَ الذُّلِّ يَنظُرُونَ مِن طَرْفٍ خَفِيٍّ ۗ وَقَالَ الَّذِينَ آمَنُوا إِنَّ الْخَاسِرِينَ الَّذِينَ خَسِرُوا أَنفُسَهُمْ وَأَهْلِيهِمْ يَوْمَ الْقِيَامَةِ ۗ أَلَا إِنَّ الظَّالِمِينَ فِي عَذَابٍ مُّقِيمٍ
Hausa
 
Kuma kană ganin su ană gitta su a kanta, sună ƙasƙantattu sabőda wulăkanci, sună hange daga gefen gani ɓoyayye. Kuma waɗanda suka yi ĩmăni sai su ce, "Lalle ne, măsu hasăra, sũ ne waɗanda suka yi hasărar răyukansu da iyălansu a Rănar ˇiyăma." To, lalle ne, azzălumai sună a cikin wata azăba zaunanniya.

Ayah   42:46   الأية
وَمَا كَانَ لَهُم مِّنْ أَوْلِيَاءَ يَنصُرُونَهُم مِّن دُونِ اللَّهِ ۗ وَمَن يُضْلِلِ اللَّهُ فَمَا لَهُ مِن سَبِيلٍ
Hausa
 
Kuma waɗansu majiɓinta ba su kasance ba a gare su, waɗanda ke iya taimakonsu, baicin Allah. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, bă shi da wani gődabe na tsĩra.

Ayah   42:47   الأية
اسْتَجِيبُوا لِرَبِّكُم مِّن قَبْلِ أَن يَأْتِيَ يَوْمٌ لَّا مَرَدَّ لَهُ مِنَ اللَّهِ ۚ مَا لَكُم مِّن مَّلْجَإٍ يَوْمَئِذٍ وَمَا لَكُم مِّن نَّكِيرٍ
Hausa
 
Ku karɓă wa Ubangijinku tun gabănin wani yini ya zo, băbu makawa gare shi daga Allah, bă ku da wata mafaka a rănar nan, kuma bă ku iya yin wani musu.

Ayah   42:48   الأية
فَإِنْ أَعْرَضُوا فَمَا أَرْسَلْنَاكَ عَلَيْهِمْ حَفِيظًا ۖ إِنْ عَلَيْكَ إِلَّا الْبَلَاغُ ۗ وَإِنَّا إِذَا أَذَقْنَا الْإِنسَانَ مِنَّا رَحْمَةً فَرِحَ بِهَا ۖ وَإِن تُصِبْهُمْ سَيِّئَةٌ بِمَا قَدَّمَتْ أَيْدِيهِمْ فَإِنَّ الْإِنسَانَ كَفُورٌ
Hausa
 
To, idan sun bijire, to, ba Mu aike ka kană mai tsaro a kansu ba, băbu abin da ke a kanka făce iyar da Manzanci. Kuma lalle ne, Mũ idan Mun ɗanɗana wa mutum wata rahama daga gare Mu, sai ya yi farin ciki da ita, kuma idan wata masĩfa ta săme su sabőda abin da hannayensu suka gabătar, to, lalle ne mutum mai tsananin kăfirci ne.

Ayah   42:49   الأية
لِّلَّهِ مُلْكُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ يَخْلُقُ مَا يَشَاءُ ۚ يَهَبُ لِمَن يَشَاءُ إِنَاثًا وَيَهَبُ لِمَن يَشَاءُ الذُّكُورَ
Hausa
 
Mulkin sammai da ƙasa na Allah kawai ne. Yană halitta abin da Yake so. Yană băyar da 'ya'ya mătă ga wanda yake so, kuma Yană băyar da ɗiya maza ga wanda Yake so.

Ayah   42:50   الأية
أَوْ يُزَوِّجُهُمْ ذُكْرَانًا وَإِنَاثًا ۖ وَيَجْعَلُ مَن يَشَاءُ عَقِيمًا ۚ إِنَّهُ عَلِيمٌ قَدِيرٌ
Hausa
 
Kő kuma Ya haɗa su maza da mătă, kuma Yană sanya wanda Ya so bakarăre. Lalle shi, Mai ilmi ne, Mai ĩkon yi.

Ayah   42:51   الأية
وَمَا كَانَ لِبَشَرٍ أَن يُكَلِّمَهُ اللَّهُ إِلَّا وَحْيًا أَوْ مِن وَرَاءِ حِجَابٍ أَوْ يُرْسِلَ رَسُولًا فَيُوحِيَ بِإِذْنِهِ مَا يَشَاءُ ۚ إِنَّهُ عَلِيٌّ حَكِيمٌ
Hausa
 
Kuma bă ya kasancẽwa ga wani mutum Allah Ya yi masa magana făce da wahayi, kő daga băYan wani shămaki, kő Ya aika wani Manzo, sa'an nan Ya yi wahayi, da izninsa ga abin da Yake so. Lalle Shĩ, Maɗaukaki ne Mai hikima.

Ayah   42:52   الأية
وَكَذَٰلِكَ أَوْحَيْنَا إِلَيْكَ رُوحًا مِّنْ أَمْرِنَا ۚ مَا كُنتَ تَدْرِي مَا الْكِتَابُ وَلَا الْإِيمَانُ وَلَٰكِن جَعَلْنَاهُ نُورًا نَّهْدِي بِهِ مَن نَّشَاءُ مِنْ عِبَادِنَا ۚ وَإِنَّكَ لَتَهْدِي إِلَىٰ صِرَاطٍ مُّسْتَقِيمٍ
Hausa
 
Kuma kamar wancan Mun aika wani rũhi (rai mai haɗa jama'a) zuwa gare ka, daga gare Mu. Ba ka kasance kă san abin da yake littăfi ba, kő abin da Yake ĩmăni, kuma amma Mun sanya shi (rũhin, watau Alƙur'ăni) wani haske ne, Mună shiryar da wanda Muke so daga cikin băyĩnMu game da shi. Kuma Lalle kai, haƙĩƙa, kană shiryarwa zuwa ga hanya, madaidaiciya.

Ayah   42:53   الأية
صِرَاطِ اللَّهِ الَّذِي لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ ۗ أَلَا إِلَى اللَّهِ تَصِيرُ الْأُمُورُ
Hausa
 
Hanyar Allah wanda ke da mulkin abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa. To, zuwa ga Allah kawai al'amura ke kőmăwa. 
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us