First Ayah 1 الأية الأوليبِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
Ayah 42:2 الأية
Ayah 42:3 الأية
كَذَٰلِكَ يُوحِي إِلَيْكَ وَإِلَى الَّذِينَ مِن قَبْلِكَ اللَّهُ الْعَزِيزُ
الْحَكِيمُ
Hausa
Kamar wancăn (asĩrin) Allah, Mabuwayi, Mai hikima, ke yin wahayi zuwa gare ka da
zuwa ga waɗanda ke gabăninka .
|
Ayah 42:4 الأية
لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ ۖ وَهُوَ الْعَلِيُّ الْعَظِيمُ
Hausa
(Allah) Shi ne da abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa, kuma Shi ne
Maɗaukaki, Mai girma.
|
Ayah 42:5 الأية
تَكَادُ السَّمَاوَاتُ يَتَفَطَّرْنَ مِن فَوْقِهِنَّ ۚ وَالْمَلَائِكَةُ
يُسَبِّحُونَ بِحَمْدِ رَبِّهِمْ وَيَسْتَغْفِرُونَ لِمَن فِي الْأَرْضِ ۗ أَلَا
إِنَّ اللَّهَ هُوَ الْغَفُورُ الرَّحِيمُ
Hausa
Sammai nă kusan su tsăge daga bisansu, kuma mală'iku nă yin tasĩhi game da gődẽ
wa Ubangijinsu kuma sună istigfări dőmin wanda ke cikin ƙasa. To, lalle Allah
Shĩ ne Mai găfara, Mai jin ƙai.
|
Ayah 42:6 الأية
وَالَّذِينَ اتَّخَذُوا مِن دُونِهِ أَوْلِيَاءَ اللَّهُ حَفِيظٌ عَلَيْهِمْ وَمَا
أَنتَ عَلَيْهِم بِوَكِيلٍ
Hausa
Kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majiɓinta waɗanda bă Shĩ ba Allah ne Mai tsaro a
kansu, kuma kai, bă wakili ne a kansu ba.
|
Ayah 42:7 الأية
وَكَذَٰلِكَ أَوْحَيْنَا إِلَيْكَ قُرْآنًا عَرَبِيًّا لِّتُنذِرَ أُمَّ الْقُرَىٰ
وَمَنْ حَوْلَهَا وَتُنذِرَ يَوْمَ الْجَمْعِ لَا رَيْبَ فِيهِ ۚ فَرِيقٌ فِي
الْجَنَّةِ وَفَرِيقٌ فِي السَّعِيرِ
Hausa
Kuma kamar haka ne Muka yi wahayin abin karăntăwa (Alƙur'ăni) na Lărabci zuwa
gare ka, dőmin ka yi gargaɗi ga Uwar Alƙaryu (Makka) da wanda ke a kẽwayenta,
kuma ka yi gargaɗi game da rănar taruwa, băbu shakka gare ta, wata ƙungiya tană
a cikin Aljanna kuma wata ƙungiya tăna a cikin sa'ĩr.
|
Ayah 42:8 الأية
وَلَوْ شَاءَ اللَّهُ لَجَعَلَهُمْ أُمَّةً وَاحِدَةً وَلَٰكِن يُدْخِلُ مَن
يَشَاءُ فِي رَحْمَتِهِ ۚ وَالظَّالِمُونَ مَا لَهُم مِّن وَلِيٍّ وَلَا نَصِيرٍ
Hausa
Kuma dă Allah Ya so, da Ya haɗă su al'umma guda, kuma Amma Yană shigar da wanda
Ya so a cikin rahamarSa alhăli kuwa azzăluMai bă su da, wani majiɓinci, kuma bă
su da wani mataimaki.
|
Ayah 42:9 الأية
أَمِ اتَّخَذُوا مِن دُونِهِ أَوْلِيَاءَ ۖ فَاللَّهُ هُوَ الْوَلِيُّ وَهُوَ
يُحْيِي الْمَوْتَىٰ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ
Hausa
Kő kuma sun riƙi waninSa majiɓinta? To Allah Shĩ ne Majiɓinci, kuma Shĩ ne ke
răyar da matattu alhăli kuwa Shĩ, Maiĩkon yi ne a kan dukan kőme.
|
Ayah 42:10 الأية
وَمَا اخْتَلَفْتُمْ فِيهِ مِن شَيْءٍ فَحُكْمُهُ إِلَى اللَّهِ ۚ ذَٰلِكُمُ
اللَّهُ رَبِّي عَلَيْهِ تَوَكَّلْتُ وَإِلَيْهِ أُنِيبُ
Hausa
Kuma abin da kuka săɓă wa jũna a cikinsa kő męne ne, to, hukuncinsa (a mayar da
shi) zuwa ga Allah. Wancan Shĩ ne Allah Ubangijĩna, a gare Shi na dőgara, kuma
zuwa gare Shi nake mayar da al'amarĩna.
|
Ayah 42:11 الأية
فَاطِرُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ جَعَلَ لَكُم مِّنْ أَنفُسِكُمْ أَزْوَاجًا
وَمِنَ الْأَنْعَامِ أَزْوَاجًا ۖ يَذْرَؤُكُمْ فِيهِ ۚ لَيْسَ كَمِثْلِهِ شَيْءٌ ۖ
وَهُوَ السَّمِيعُ الْبَصِيرُ
Hausa
(Shĩ ne) Mai ƙăga halittar sammai da ƙasa, Ya sanya muku ma'aura daga jinsinku,
kuma (Ya sanya) daga dabbőbi maza da mătă, Yană halitta ku a cikinsu, wani abu
bai zama kamar tamkarSa ba, kuma Shĩ ne Mai ji, Mai gani.
|
Ayah 42:12 الأية
لَهُ مَقَالِيدُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۖ يَبْسُطُ الرِّزْقَ لِمَن يَشَاءُ
وَيَقْدِرُ ۚ إِنَّهُ بِكُلِّ شَيْءٍ عَلِيمٌ
Hausa
Shĩ ne da mabuɗan sammai da ƙasa Yană shimfiɗa arziki ga wanda ya so kuma Yană
hukuntăwa. Lalle ne, Shĩ Masani ne ga dukan kőme.
|
Ayah 42:13 الأية
شَرَعَ لَكُم مِّنَ الدِّينِ مَا وَصَّىٰ بِهِ نُوحًا وَالَّذِي أَوْحَيْنَا
إِلَيْكَ وَمَا وَصَّيْنَا بِهِ إِبْرَاهِيمَ وَمُوسَىٰ وَعِيسَىٰ ۖ أَنْ أَقِيمُوا
الدِّينَ وَلَا تَتَفَرَّقُوا فِيهِ ۚ كَبُرَ عَلَى الْمُشْرِكِينَ مَا تَدْعُوهُمْ
إِلَيْهِ ۚ اللَّهُ يَجْتَبِي إِلَيْهِ مَن يَشَاءُ وَيَهْدِي إِلَيْهِ مَن يُنِيبُ
Hausa
Ya shar'anta muku, game da addini, abin da Ya yi wasiyya da shi ga Nũhu da abin
da Muka yi wahayi da shi zuwa gare ka, da abin da Muka yi wasiyya da shi ga
Ibrăhĩm da Mũsă da Ĩsă, cẽwa ku tsayar da addini sősai kuma kada ku rarrabu a
cikinsa. Abin da kuke kira zuwa gare shi, ya yi nauyi a kan măsu shirki. Allah
na zăɓen wanda Yake so zuwa gare Shi, kuma Yană shiryar da wanda ke tawakkali
gare Shi, ga hanyarSa.
|
Ayah 42:14 الأية
وَمَا تَفَرَّقُوا إِلَّا مِن بَعْدِ مَا جَاءَهُمُ الْعِلْمُ بَغْيًا بَيْنَهُمْ ۚ
وَلَوْلَا كَلِمَةٌ سَبَقَتْ مِن رَّبِّكَ إِلَىٰ أَجَلٍ مُّسَمًّى لَّقُضِيَ
بَيْنَهُمْ ۚ وَإِنَّ الَّذِينَ أُورِثُوا الْكِتَابَ مِن بَعْدِهِمْ لَفِي شَكٍّ
مِّنْهُ مُرِيبٍ
Hausa
Kuma ba su rarraba ba făce băyan da ilmi ya jẽ musu, dőmin zălunci a tsakăninsu
kuma bă dőmin wata kalma tă gabata ba daga Ubangijinka, zuwa ga wani ajali
ambatacce, dă an yi hukunci a tsakaninsu. Kuma lalle ne waɗanda aka gădar wa
Littafi daga băyansu, haƙiƙa, sună cikin shakka a gare shi, mai sanya kokanto.
|
Ayah 42:15 الأية
فَلِذَٰلِكَ فَادْعُ ۖ وَاسْتَقِمْ كَمَا أُمِرْتَ ۖ وَلَا تَتَّبِعْ أَهْوَاءَهُمْ
ۖ وَقُلْ آمَنتُ بِمَا أَنزَلَ اللَّهُ مِن كِتَابٍ ۖ وَأُمِرْتُ لِأَعْدِلَ
بَيْنَكُمُ ۖ اللَّهُ رَبُّنَا وَرَبُّكُمْ ۖ لَنَا أَعْمَالُنَا وَلَكُمْ
أَعْمَالُكُمْ ۖ لَا حُجَّةَ بَيْنَنَا وَبَيْنَكُمُ ۖ اللَّهُ يَجْمَعُ بَيْنَنَا
ۖ وَإِلَيْهِ الْمَصِيرُ
Hausa
Sabőda haka, sai ka yi kira kuma kai ka daidaitu kamar yadda aka umurce ka, kuma
kada ka bi son zũciyőyinsu, kumaka ce, "Nă yi ĩmăni da abin da Allah Ya saukar
na littăfi, kuma an umurce ni da in yi ădalci a tsakăninku. Allah ne
Ubangijinmu, kuma Shĩ ne Ubangijinku, ayyukanmu nă gare mu, kuma ayyukanku nă
gare ku, kuma băbu wata hujja a tsakăninmu da tsakăninku. Allah zai tara mu,
kuma zuwa gare Shi makőma take."
|
Ayah 42:16 الأية
وَالَّذِينَ يُحَاجُّونَ فِي اللَّهِ مِن بَعْدِ مَا اسْتُجِيبَ لَهُ حُجَّتُهُمْ
دَاحِضَةٌ عِندَ رَبِّهِمْ وَعَلَيْهِمْ غَضَبٌ وَلَهُمْ عَذَابٌ شَدِيدٌ
Hausa
Kuma waɗannan da ke jăyayya a cikin al'amarin Allah daga băyan an karɓa masa,
hujjarsu ɓătăcciya ce a wurin Ubangijinsu, kuma akwai fushi a kansu, kuma sună
da wata azăba mai tsanani.
|
Ayah 42:17 الأية
اللَّهُ الَّذِي أَنزَلَ الْكِتَابَ بِالْحَقِّ وَالْمِيزَانَ ۗ وَمَا يُدْرِيكَ
لَعَلَّ السَّاعَةَ قَرِيبٌ
Hausa
Allah ne Wanda Ya saukar da Littăfi da gaskiya, da sikeli. Kuma me ya sanar da
kai (cẽwa ană) tsammănin Sa'ar kusa take?
|
Ayah 42:18 الأية
يَسْتَعْجِلُ بِهَا الَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِهَا ۖ وَالَّذِينَ آمَنُوا
مُشْفِقُونَ مِنْهَا وَيَعْلَمُونَ أَنَّهَا الْحَقُّ ۗ أَلَا إِنَّ الَّذِينَ
يُمَارُونَ فِي السَّاعَةِ لَفِي ضَلَالٍ بَعِيدٍ
Hausa
Waɗanda ba su yi ĩmănida ita ba, (sũ) ke nẽman gaggautőwarta. Alhăli kuwa
waɗanda suka yi ĩmăni, măsu tsőro ne daga gare ta, kuma sun sani, cẽwa ita
gaskiya ce. To, lalle ne waɗanda ke shakka a cikin Sa'a, haƙĩƙa,sună a cikin
ɓata Mai nĩsa.
|
Ayah 42:19 الأية
اللَّهُ لَطِيفٌ بِعِبَادِهِ يَرْزُقُ مَن يَشَاءُ ۖ وَهُوَ الْقَوِيُّ الْعَزِيزُ
Hausa
Allah Mai tausasăwa ne ga băyinsa. Yană azurta wanda yake so, alhăli kuma Shĩ ne
Maiƙarfi, Mabuwăyi.
|
Ayah 42:20 الأية
مَن كَانَ يُرِيدُ حَرْثَ الْآخِرَةِ نَزِدْ لَهُ فِي حَرْثِهِ ۖ وَمَن كَانَ
يُرِيدُ حَرْثَ الدُّنْيَا نُؤْتِهِ مِنْهَا وَمَا لَهُ فِي الْآخِرَةِ مِن
نَّصِيبٍ
Hausa
Wanda ya kasance yană nufin nőman Lăhira ză Mu ƙăra masa a cikin nőmansa, kuma
wanda ya kasance yană nufin nőman dũniya, ză Mu sam masa daga gare ta, alhăli
kuwa bă shi da wani rabo a cikin Lăhira.
|
Ayah 42:21 الأية
أَمْ لَهُمْ شُرَكَاءُ شَرَعُوا لَهُم مِّنَ الدِّينِ مَا لَمْ يَأْذَن بِهِ
اللَّهُ ۚ وَلَوْلَا كَلِمَةُ الْفَصْلِ لَقُضِيَ بَيْنَهُمْ ۗ وَإِنَّ
الظَّالِمِينَ لَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ
Hausa
Kő sună da waɗansu abőkan tărayya (da Allah) waɗanda suka shar'anta musu, game
da addini, abin da Allah bai yi izni ba da shi? Kuma bă dőmin kalmar hukunci ba,
da lalle, an yi hukunci a tsakăninsu. Kuma lalle azzălumai sună da azăba mai
raɗaɗi.
|
Ayah 42:22 الأية
تَرَى الظَّالِمِينَ مُشْفِقِينَ مِمَّا كَسَبُوا وَهُوَ وَاقِعٌ بِهِمْ ۗ
وَالَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ فِي رَوْضَاتِ الْجَنَّاتِ ۖ لَهُم
مَّا يَشَاءُونَ عِندَ رَبِّهِمْ ۚ ذَٰلِكَ هُوَ الْفَضْلُ الْكَبِيرُ
Hausa
Kană ganin azzălumai sună măsu tsőro daga abin da suka sană'anta alhăli kuwa shi
abin tsoron, mai aukuwa ne gare su, kuma waɗanda suka yi ĩmăni kuma suka aikata
ayyukan ƙwarai sună a cikin fadamun Aljanna sună da abin da suke so a wurin
Ubangijinsu. Waccan fa ita ce falala mai girma.
|
Ayah 42:23 الأية
ذَٰلِكَ الَّذِي يُبَشِّرُ اللَّهُ عِبَادَهُ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا
الصَّالِحَاتِ ۗ قُل لَّا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ أَجْرًا إِلَّا الْمَوَدَّةَ فِي
الْقُرْبَىٰ ۗ وَمَن يَقْتَرِفْ حَسَنَةً نَّزِدْ لَهُ فِيهَا حُسْنًا ۚ إِنَّ
اللَّهَ غَفُورٌ شَكُورٌ
Hausa
Wancan shĩ ne Allah ke băyar da bushăra da shi ga băyinSa waɗanda suka yi ĩmăni
kuma suka aikata ayyukan ƙwarai. Ka ce: "Bă ni tambayar ku wata ijăra a kansa,
făce dai sőyayya ta cikin zumunta." Kuma wanda ya aikata wani abu mai kyau, ză
Mu ƙară masa kyau a cikinsa, lalle Allah Mai găfara ne, Mai gődiya.
|
Ayah 42:24 الأية
أَمْ يَقُولُونَ افْتَرَىٰ عَلَى اللَّهِ كَذِبًا ۖ فَإِن يَشَإِ اللَّهُ يَخْتِمْ
عَلَىٰ قَلْبِكَ ۗ وَيَمْحُ اللَّهُ الْبَاطِلَ وَيُحِقُّ الْحَقَّ بِكَلِمَاتِهِ ۚ
إِنَّهُ عَلِيمٌ بِذَاتِ الصُّدُورِ
Hausa
Kő ză su ce: "Ya ƙirƙira ƙarya ga Allah ne?" To, idan Allah Ya so, zai yunƙe a
kan zũciyarka, kuma Allah Yana shăfe ƙarya kuma Yana tabbatar da gaskiya da
kalmőminSa. Lalle ne Shĩ Masani ne ga abin da ke cikin zukata.
|
Ayah 42:25 الأية
وَهُوَ الَّذِي يَقْبَلُ التَّوْبَةَ عَنْ عِبَادِهِ وَيَعْفُو عَنِ السَّيِّئَاتِ
وَيَعْلَمُ مَا تَفْعَلُونَ
Hausa
Kuma Shi ne ke karɓar tũba daga băyinSa, kuma Yană Yafe ƙananan laifuffuka,
alhăli kuwa Yană sanin abin da kuke aikatăwa.
|
Ayah 42:26 الأية
وَيَسْتَجِيبُ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَيَزِيدُهُم مِّن
فَضْلِهِ ۚ وَالْكَافِرُونَ لَهُمْ عَذَابٌ شَدِيدٌ
Hausa
Kuma Yană karɓa wa waɗannan da suka yi ĩmăni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai,
kuma Yană ƙăra musu (sakamako) daga falalarSa. Kuma kăfirai sună da wata azăba
mai tsanani.
|
Ayah 42:27 الأية
وَلَوْ بَسَطَ اللَّهُ الرِّزْقَ لِعِبَادِهِ لَبَغَوْا فِي الْأَرْضِ وَلَٰكِن
يُنَزِّلُ بِقَدَرٍ مَّا يَشَاءُ ۚ إِنَّهُ بِعِبَادِهِ خَبِيرٌ بَصِيرٌ
Hausa
Kuma dă Allah Ya shimfiɗa arziki ga băyinSa, dă sun yi zăluncin rarraba jama'a a
cikin ƙasa, kuma amma Yană sassaukarwa gwargwado ga abin da Yake so. Lalle ne
Shĩ, game da băyinSa, Mai labartawa ne, Mai gani.
|
Ayah 42:28 الأية
وَهُوَ الَّذِي يُنَزِّلُ الْغَيْثَ مِن بَعْدِ مَا قَنَطُوا وَيَنشُرُ رَحْمَتَهُ
ۚ وَهُوَ الْوَلِيُّ الْحَمِيدُ
Hausa
Kuma Shĩ ne ke sassaukar da girgije (ruwa) a băyan sun yanke ƙauna kuma Yana
wătsa rahamarSa, alhăli kuwa Shĩ ne Majiɓinci, Mai gődiya.
|
Ayah 42:29 الأية
وَمِنْ آيَاتِهِ خَلْقُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَثَّ فِيهِمَا مِن
دَابَّةٍ ۚ وَهُوَ عَلَىٰ جَمْعِهِمْ إِذَا يَشَاءُ قَدِيرٌ
Hausa
Kuma akwai daga ăyőyinSa, halittar sammai da ƙasa da abin da Ya wătsa a cikinsu
na dabba alhăli kuwa Shĩ Mai ĩko ne ga tăra su, a lőkacin da Yake so.
|
Ayah 42:30 الأية
وَمَا أَصَابَكُم مِّن مُّصِيبَةٍ فَبِمَا كَسَبَتْ أَيْدِيكُمْ وَيَعْفُو عَن
كَثِيرٍ
Hausa
Kuma abin da ya săme ku na wata masifa, to, game da abin da hannăyenku suka
sana' anta ne kuma (Alah) Yană Yafẽwar (waɗansu laifuffuka) măsu yawa.
|
Ayah 42:31 الأية
وَمَا أَنتُم بِمُعْجِزِينَ فِي الْأَرْضِ ۖ وَمَا لَكُم مِّن دُونِ اللَّهِ مِن
وَلِيٍّ وَلَا نَصِيرٍ
Hausa
Kuma ba ku zama măsu buwăya ba a cikin ƙasa kuma bă ku da wani majiɓinci, wanin
Allah, kuma bă ku da wani mataimaki.
|
Ayah 42:32 الأية
وَمِنْ آيَاتِهِ الْجَوَارِ فِي الْبَحْرِ كَالْأَعْلَامِ
Hausa
Kuma akwai daga ăyőyinsa, jirăge măsu gudăna a cikin tẽku kamar duwătsu.
|
Ayah 42:33 الأية
إِن يَشَأْ يُسْكِنِ الرِّيحَ فَيَظْلَلْنَ رَوَاكِدَ عَلَىٰ ظَهْرِهِ ۚ إِنَّ فِي
ذَٰلِكَ لَآيَاتٍ لِّكُلِّ صَبَّارٍ شَكُورٍ
Hausa
Idan Ya so, sai Ya kwantar da iskar, sai jirăgen su yini sună măsu kawaici a kan
băyan tẽkun,Lalle ne ga wancan, haƙĩƙa, akwai ăyőyi ga dukan mai haƙuri, Mai
gődiya.
|
Ayah 42:34 الأية
أَوْ يُوبِقْهُنَّ بِمَا كَسَبُوا وَيَعْفُ عَن كَثِيرٍ
Hausa
Kő Ya halakă su (sũ jirăgen) sabőda abin da măsu su suka sană'anta, alhăli kuwa
Yană yăfe (laifuffuka) măsu yawa.
|
Ayah 42:35 الأية
وَيَعْلَمَ الَّذِينَ يُجَادِلُونَ فِي آيَاتِنَا مَا لَهُم مِّن مَّحِيصٍ
Hausa
Kuma dőmin waɗanda ke jăyayya a cikin ăyőyinMu su sani (cẽwa) bă su da wata
mafaka.
|
Ayah 42:36 الأية
فَمَا أُوتِيتُم مِّن شَيْءٍ فَمَتَاعُ الْحَيَاةِ الدُّنْيَا ۖ وَمَا عِندَ
اللَّهِ خَيْرٌ وَأَبْقَىٰ لِلَّذِينَ آمَنُوا وَعَلَىٰ رَبِّهِمْ يَتَوَكَّلُونَ
Hausa
Sabőda haka abin da aka bă ku, kő mẽne ne, to, jin dăɗin rayuwar dũniya ne, kuma
abin da ke a wurin Allah Shĩ ne mafĩfĩci,kuma Shĩ ne mafi wanzuwa ga waɗanda
suka yi ĩmăni kuma sună dőgara a kan Ubangijinsu kawai.
|
Ayah 42:37 الأية
وَالَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَائِرَ الْإِثْمِ وَالْفَوَاحِشَ وَإِذَا مَا
غَضِبُوا هُمْ يَغْفِرُونَ
Hausa
Kuma waɗanda ke nisantar manyan zunubbai da ayyukan alfăsha, kuma idan sun yi
fushi, sũ, sună găfartawa.
|
Ayah 42:38 الأية
وَالَّذِينَ اسْتَجَابُوا لِرَبِّهِمْ وَأَقَامُوا الصَّلَاةَ وَأَمْرُهُمْ شُورَىٰ
بَيْنَهُمْ وَمِمَّا رَزَقْنَاهُمْ يُنفِقُونَ
Hausa
Da waɗanda suka karɓa kira ga Ubangijinsu, kuma suka tsayar da salla, kuma
al'amarinsu shăwara ne a tsakăninsu, kuma daga abin da Muka azurta su sună
ciyarwa.
|
Ayah 42:39 الأية
وَالَّذِينَ إِذَا أَصَابَهُمُ الْبَغْيُ هُمْ يَنتَصِرُونَ
Hausa
Da waɗanda idan zălunci ya săme su, sună nẽman taimako (su răma).
|
Ayah 42:40 الأية
وَجَزَاءُ سَيِّئَةٍ سَيِّئَةٌ مِّثْلُهَا ۖ فَمَنْ عَفَا وَأَصْلَحَ فَأَجْرُهُ
عَلَى اللَّهِ ۚ إِنَّهُ لَا يُحِبُّ الظَّالِمِينَ
Hausa
Kuma sakamakon cũta shĩ ne wata cũta kamarta, sai dai wanda Ya yăfe kuma ya
kyautata, to lădarsa nă ga Allah. Lalle ne, Shĩ (Allah) bă Ya son azzălumai.
|
Ayah 42:41 الأية
وَلَمَنِ انتَصَرَ بَعْدَ ظُلْمِهِ فَأُولَٰئِكَ مَا عَلَيْهِم مِّن سَبِيلٍ
Hausa
Kuma Lalle ne, wanda ya nẽmi taimakon rămăwa a băyan an zălunce shi, to waɗannan
băbu wata hanyar zargi a kansu.
|
Ayah 42:42 الأية
إِنَّمَا السَّبِيلُ عَلَى الَّذِينَ يَظْلِمُونَ النَّاسَ وَيَبْغُونَ فِي
الْأَرْضِ بِغَيْرِ الْحَقِّ ۚ أُولَٰئِكَ لَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ
Hausa
lnda hanyar zargi kawai take, shĩ ne a kan waɗanda ke zăluntar mutăne kuma sună
ƙẽtare haddin shari'a cikin ƙasa bă tare da haƙƙi ba. Waɗannan sună da azăba Mai
raɗaɗi.
|
Ayah 42:43 الأية
وَلَمَن صَبَرَ وَغَفَرَ إِنَّ ذَٰلِكَ لَمِنْ عَزْمِ الْأُمُورِ
Hausa
Kuma Lalle ne, wanda ya yi haƙuri kuma ya găfarta (wa wanda ya zălunce shi), to
shĩ wancan aiki haƙĩƙa, yană daga manyan al'amura (da Allah ke so).
|
Ayah 42:44 الأية
وَمَن يُضْلِلِ اللَّهُ فَمَا لَهُ مِن وَلِيٍّ مِّن بَعْدِهِ ۗ وَتَرَى
الظَّالِمِينَ لَمَّا رَأَوُا الْعَذَابَ يَقُولُونَ هَلْ إِلَىٰ مَرَدٍّ مِّن
سَبِيلٍ
Hausa
Kuma wanda (Allah Ya ɓatar, to, bă shi da wani majiɓinci băyanSa, kuma ză ka ga
azzălumai, a lőkacin da suka ga azăba, sună cẽwa, "Shin, akwai hanya zuwa ga
kőmăwa?"
|
Ayah 42:45 الأية
وَتَرَاهُمْ يُعْرَضُونَ عَلَيْهَا خَاشِعِينَ مِنَ الذُّلِّ يَنظُرُونَ مِن طَرْفٍ
خَفِيٍّ ۗ وَقَالَ الَّذِينَ آمَنُوا إِنَّ الْخَاسِرِينَ الَّذِينَ خَسِرُوا
أَنفُسَهُمْ وَأَهْلِيهِمْ يَوْمَ الْقِيَامَةِ ۗ أَلَا إِنَّ الظَّالِمِينَ فِي
عَذَابٍ مُّقِيمٍ
Hausa
Kuma kană ganin su ană gitta su a kanta, sună ƙasƙantattu sabőda wulăkanci, sună
hange daga gefen gani ɓoyayye. Kuma waɗanda suka yi ĩmăni sai su ce, "Lalle ne,
măsu hasăra, sũ ne waɗanda suka yi hasărar răyukansu da iyălansu a Rănar
ˇiyăma." To, lalle ne, azzălumai sună a cikin wata azăba zaunanniya.
|
Ayah 42:46 الأية
وَمَا كَانَ لَهُم مِّنْ أَوْلِيَاءَ يَنصُرُونَهُم مِّن دُونِ اللَّهِ ۗ وَمَن
يُضْلِلِ اللَّهُ فَمَا لَهُ مِن سَبِيلٍ
Hausa
Kuma waɗansu majiɓinta ba su kasance ba a gare su, waɗanda ke iya taimakonsu,
baicin Allah. Kuma wanda Allah Ya ɓatar, to, bă shi da wani gődabe na tsĩra.
|
Ayah 42:47 الأية
اسْتَجِيبُوا لِرَبِّكُم مِّن قَبْلِ أَن يَأْتِيَ يَوْمٌ لَّا مَرَدَّ لَهُ مِنَ
اللَّهِ ۚ مَا لَكُم مِّن مَّلْجَإٍ يَوْمَئِذٍ وَمَا لَكُم مِّن نَّكِيرٍ
Hausa
Ku karɓă wa Ubangijinku tun gabănin wani yini ya zo, băbu makawa gare shi daga
Allah, bă ku da wata mafaka a rănar nan, kuma bă ku iya yin wani musu.
|
Ayah 42:48 الأية
فَإِنْ أَعْرَضُوا فَمَا أَرْسَلْنَاكَ عَلَيْهِمْ حَفِيظًا ۖ إِنْ عَلَيْكَ إِلَّا
الْبَلَاغُ ۗ وَإِنَّا إِذَا أَذَقْنَا الْإِنسَانَ مِنَّا رَحْمَةً فَرِحَ بِهَا ۖ
وَإِن تُصِبْهُمْ سَيِّئَةٌ بِمَا قَدَّمَتْ أَيْدِيهِمْ فَإِنَّ الْإِنسَانَ
كَفُورٌ
Hausa
To, idan sun bijire, to, ba Mu aike ka kană mai tsaro a kansu ba, băbu abin da
ke a kanka făce iyar da Manzanci. Kuma lalle ne, Mũ idan Mun ɗanɗana wa mutum
wata rahama daga gare Mu, sai ya yi farin ciki da ita, kuma idan wata masĩfa ta
săme su sabőda abin da hannayensu suka gabătar, to, lalle ne mutum mai tsananin
kăfirci ne.
|
Ayah 42:49 الأية
لِّلَّهِ مُلْكُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ يَخْلُقُ مَا يَشَاءُ ۚ يَهَبُ لِمَن
يَشَاءُ إِنَاثًا وَيَهَبُ لِمَن يَشَاءُ الذُّكُورَ
Hausa
Mulkin sammai da ƙasa na Allah kawai ne. Yană halitta abin da Yake so. Yană
băyar da 'ya'ya mătă ga wanda yake so, kuma Yană băyar da ɗiya maza ga wanda
Yake so.
|
Ayah 42:50 الأية
أَوْ يُزَوِّجُهُمْ ذُكْرَانًا وَإِنَاثًا ۖ وَيَجْعَلُ مَن يَشَاءُ عَقِيمًا ۚ
إِنَّهُ عَلِيمٌ قَدِيرٌ
Hausa
Kő kuma Ya haɗa su maza da mătă, kuma Yană sanya wanda Ya so bakarăre. Lalle
shi, Mai ilmi ne, Mai ĩkon yi.
|
Ayah 42:51 الأية
وَمَا كَانَ لِبَشَرٍ أَن يُكَلِّمَهُ اللَّهُ إِلَّا وَحْيًا أَوْ مِن وَرَاءِ
حِجَابٍ أَوْ يُرْسِلَ رَسُولًا فَيُوحِيَ بِإِذْنِهِ مَا يَشَاءُ ۚ إِنَّهُ
عَلِيٌّ حَكِيمٌ
Hausa
Kuma bă ya kasancẽwa ga wani mutum Allah Ya yi masa magana făce da wahayi, kő
daga băYan wani shămaki, kő Ya aika wani Manzo, sa'an nan Ya yi wahayi, da
izninsa ga abin da Yake so. Lalle Shĩ, Maɗaukaki ne Mai hikima.
|
Ayah 42:52 الأية
وَكَذَٰلِكَ أَوْحَيْنَا إِلَيْكَ رُوحًا مِّنْ أَمْرِنَا ۚ مَا كُنتَ تَدْرِي مَا
الْكِتَابُ وَلَا الْإِيمَانُ وَلَٰكِن جَعَلْنَاهُ نُورًا نَّهْدِي بِهِ مَن
نَّشَاءُ مِنْ عِبَادِنَا ۚ وَإِنَّكَ لَتَهْدِي إِلَىٰ صِرَاطٍ مُّسْتَقِيمٍ
Hausa
Kuma kamar wancan Mun aika wani rũhi (rai mai haɗa jama'a) zuwa gare ka, daga
gare Mu. Ba ka kasance kă san abin da yake littăfi ba, kő abin da Yake ĩmăni,
kuma amma Mun sanya shi (rũhin, watau Alƙur'ăni) wani haske ne, Mună shiryar da
wanda Muke so daga cikin băyĩnMu game da shi. Kuma Lalle kai, haƙĩƙa, kană
shiryarwa zuwa ga hanya, madaidaiciya.
|
Ayah 42:53 الأية
صِرَاطِ اللَّهِ الَّذِي لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ ۗ أَلَا
إِلَى اللَّهِ تَصِيرُ الْأُمُورُ
Hausa
Hanyar Allah wanda ke da mulkin abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin
ƙasa. To, zuwa ga Allah kawai al'amura ke kőmăwa.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|