« Prev

50. Surah Qâf. سورة ق

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
ق ۚ وَالْقُرْآنِ الْمَجِيدِ
Hausa
 
ˇ̃ . Ină rantsuwa da Alƙur'ăni Mai girma.

Ayah   50:2   الأية
بَلْ عَجِبُوا أَن جَاءَهُم مُّنذِرٌ مِّنْهُمْ فَقَالَ الْكَافِرُونَ هَٰذَا شَيْءٌ عَجِيبٌ
Hausa
 
Ă'a, sun yi mămăki, cewa mai gargaɗi, daga gare su, yă zo musu, sai kăfirai suka ce: "Wannan wani abu ne mai ban mămăki."

Ayah   50:3   الأية
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا ۖ ذَٰلِكَ رَجْعٌ بَعِيدٌ
Hausa
 
"Shin idan muka mutu kuma muka kasance turɓăya (ză a kőmo da mu)? Waccan kőmowa ce mai nĩsa."

Ayah   50:4   الأية
قَدْ عَلِمْنَا مَا تَنقُصُ الْأَرْضُ مِنْهُمْ ۖ وَعِندَنَا كِتَابٌ حَفِيظٌ
Hausa
 
Lalle ne Mun san abin da ƙasă ke ragẽwo daga gare su, kuma wurinMu akwai wani littăfi mai tsarẽwa.

Ayah   50:5   الأية
بَلْ كَذَّبُوا بِالْحَقِّ لَمَّا جَاءَهُمْ فَهُمْ فِي أَمْرٍ مَّرِيجٍ
Hausa
 
Ă'a, sun ƙaryata ne game da gaskiyar a lőkacin da ta je musu, sabőda haka sună a cikin wani al'amari mai raurawa.

Ayah   50:6   الأية
أَفَلَمْ يَنظُرُوا إِلَى السَّمَاءِ فَوْقَهُمْ كَيْفَ بَنَيْنَاهَا وَزَيَّنَّاهَا وَمَا لَهَا مِن فُرُوجٍ
Hausa
 
Shin, to, ba su yi dubi ba zuwa ga samă a bisa gare su, yadda Muka gĩna ta, kuma Muka ƙawăce ta, kuma bă ta da waɗansu tsăgogi?

Ayah   50:7   الأية
وَالْأَرْضَ مَدَدْنَاهَا وَأَلْقَيْنَا فِيهَا رَوَاسِيَ وَأَنبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوْجٍ بَهِيجٍ
Hausa
 
Da ƙasă, Mun mĩƙe ta, kuma Mun jẽfa kafaffun duwătsu a cikinta, kuma Mun tsirar, a cikinta daga kőwane ma'auri mai ban sha'awa?

Ayah   50:8   الأية
تَبْصِرَةً وَذِكْرَىٰ لِكُلِّ عَبْدٍ مُّنِيبٍ
Hausa
 
Dőmin wăyar da ido da tunătarwa ga dukan băwa mai tawakkali?

Ayah   50:9   الأية
وَنَزَّلْنَا مِنَ السَّمَاءِ مَاءً مُّبَارَكًا فَأَنبَتْنَا بِهِ جَنَّاتٍ وَحَبَّ الْحَصِيدِ
Hausa
 
Kuma Mun sassakar, daga samă ruwa mai albarka sa'an nan Muka tsirar game da shi (ităcen) lambuna da ƙwăya abin girbẽwa.

Ayah   50:10   الأية
وَالنَّخْلَ بَاسِقَاتٍ لَّهَا طَلْعٌ نَّضِيدٌ
Hausa
 
Da ităcen dabĩno dőgăye, sună da'ya'yan ităce gunda măsu hauhawar jũna.

Ayah   50:11   الأية
رِّزْقًا لِّلْعِبَادِ ۖ وَأَحْيَيْنَا بِهِ بَلْدَةً مَّيْتًا ۚ كَذَٰلِكَ الْخُرُوجُ
Hausa
 
Dőmin arziki ga băyi, kuma Muka răyar da ƙasa matacciya game da shi. Kamar wannan ne fitar daga kabari kake.

Ayah   50:12   الأية
كَذَّبَتْ قَبْلَهُمْ قَوْمُ نُوحٍ وَأَصْحَابُ الرَّسِّ وَثَمُودُ
Hausa
 
Mutănen Nũhu sun ƙaryata, a gabăninsu (mutănen yanzu) da ma'abũta Rassi, da Samũdăwa.

Ayah   50:13   الأية
وَعَادٌ وَفِرْعَوْنُ وَإِخْوَانُ لُوطٍ
Hausa
 
Da Ădăwa da Fir'auna da 'yan'uwan Lũɗu.

Ayah   50:14   الأية
وَأَصْحَابُ الْأَيْكَةِ وَقَوْمُ تُبَّعٍ ۚ كُلٌّ كَذَّبَ الرُّسُلَ فَحَقَّ وَعِيدِ
Hausa
 
Da ma'abũta ƙunci da mutănen Tubba'u, kőwanensu ya ƙaryata Manzanni, sai ƙyacẽwaTa ta tabbata.

Ayah   50:15   الأية
أَفَعَيِينَا بِالْخَلْقِ الْأَوَّلِ ۚ بَلْ هُمْ فِي لَبْسٍ مِّنْ خَلْقٍ جَدِيدٍ
Hausa
 
Shin, to, Mun kăsa ne game da halittar farko? Ă'a, su sună a cikin rikici daga halitta săbuwa.

Ayah   50:16   الأية
وَلَقَدْ خَلَقْنَا الْإِنسَانَ وَنَعْلَمُ مَا تُوَسْوِسُ بِهِ نَفْسُهُ ۖ وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنْ حَبْلِ الْوَرِيدِ
Hausa
 
Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun halitta mutum kuma Mun san abin da ransa ke yin waswăsi da shi, kuma Mũ ne mafi kusanta zuwa gare shi daga lakar jannayẽnsa.

Ayah   50:17   الأية
إِذْ يَتَلَقَّى الْمُتَلَقِّيَانِ عَنِ الْيَمِينِ وَعَنِ الشِّمَالِ قَعِيدٌ
Hausa
 
A lőkacin da măsu haɗuwa biyu suke haɗuwa daga dăma, kuma daga hagu akwai wani (mală'ika) zaunanne.

Ayah   50:18   الأية
مَّا يَلْفِظُ مِن قَوْلٍ إِلَّا لَدَيْهِ رَقِيبٌ عَتِيدٌ
Hausa
 
Bă ya lafazi da wata magana făce a lĩƙe da shi akwai mai tsaro halartacce.

Ayah   50:19   الأية
وَجَاءَتْ سَكْرَةُ الْمَوْتِ بِالْحَقِّ ۖ ذَٰلِكَ مَا كُنتَ مِنْهُ تَحِيدُ
Hausa
 
Kuma măyen mutuwa ya jẽ da gaskiya. Wannan shĩ ne abin da ka kasance daga gare shi kană bijirẽwa.

Ayah   50:20   الأية
وَنُفِخَ فِي الصُّورِ ۚ ذَٰلِكَ يَوْمُ الْوَعِيدِ
Hausa
 
Kuma aka hũra a cikin ƙaho. Wancan yinin ƙyacẽwar ne fa.

Ayah   50:21   الأية
وَجَاءَتْ كُلُّ نَفْسٍ مَّعَهَا سَائِقٌ وَشَهِيدٌ
Hausa
 
Kuma kőwane rai ya zo, tăre da shi akwai mai kőra da mai shaida.

Ayah   50:22   الأية
لَّقَدْ كُنتَ فِي غَفْلَةٍ مِّنْ هَٰذَا فَكَشَفْنَا عَنكَ غِطَاءَكَ فَبَصَرُكَ الْيَوْمَ حَدِيدٌ
Hausa
 
(Sai a ce masa): "Lalle ne, haƙĩƙa, ka kasance a cikin gafala daga wannan. To, Mun kuranye maka rufinka, sabőda haka ganinka a yau, mai kaifi ne."

Ayah   50:23   الأية
وَقَالَ قَرِينُهُ هَٰذَا مَا لَدَيَّ عَتِيدٌ
Hausa
 
Kuma abőkin haɗinsa ya ce: "Wannan shi ne abin da ke tăre da ni halarce."

Ayah   50:24   الأية
أَلْقِيَا فِي جَهَنَّمَ كُلَّ كَفَّارٍ عَنِيدٍ
Hausa
 
(A ce wa Mală'iku), "Ku jẽfa, a cikin Jahannama, dukan mai yawan kăfirci, mai tsaurin rai."

Ayah   50:25   الأية
مَّنَّاعٍ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ مُّرِيبٍ
Hausa
 
"Mai yawan hanăwa ga alhẽri, mai zălunci, mai shakka."

Ayah   50:26   الأية
الَّذِي جَعَلَ مَعَ اللَّهِ إِلَٰهًا آخَرَ فَأَلْقِيَاهُ فِي الْعَذَابِ الشَّدِيدِ
Hausa
 
"Wanda ya sanya, tăre da Allah wani abin bautăwa na dabam, sabőda haka kujẽfa shi a cikin azăba mai tsanani."

Ayah   50:27   الأية
قَالَ قَرِينُهُ رَبَّنَا مَا أَطْغَيْتُهُ وَلَٰكِن كَانَ فِي ضَلَالٍ بَعِيدٍ
Hausa
 
Abőkin haɗinsa ya ce: "Ya Ubangijinmu! Ban sanya shi girman kai ba, kuma amma ya kasance a cikin ɓata mai nĩsa."

Ayah   50:28   الأية
قَالَ لَا تَخْتَصِمُوا لَدَيَّ وَقَدْ قَدَّمْتُ إِلَيْكُم بِالْوَعِيدِ
Hausa
 
Ya ce: "Kada ku yi husũma a wuriNa, alhăli Na gabătar da ƙyacewa zuwa gare ku."

Ayah   50:29   الأية
مَا يُبَدَّلُ الْقَوْلُ لَدَيَّ وَمَا أَنَا بِظَلَّامٍ لِّلْعَبِيدِ
Hausa
 
"Ba a musanya magana a wuriNa, Kuma Ban zama Mai zălunci ba ga băyiNa."

Ayah   50:30   الأية
يَوْمَ نَقُولُ لِجَهَنَّمَ هَلِ امْتَلَأْتِ وَتَقُولُ هَلْ مِن مَّزِيدٍ
Hausa
 
Rănar da Muke cẽwa ga Jahannama "Shin, kin cika?" Kuma ta ce: "Ashe, akwai wani ƙări?"

Ayah   50:31   الأية
وَأُزْلِفَتِ الْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَ غَيْرَ بَعِيدٍ
Hausa
 
Kuma a kusantar dă Aljanna ga măsu taƙawa, ba da nĩsa ba.

Ayah   50:32   الأية
هَٰذَا مَا تُوعَدُونَ لِكُلِّ أَوَّابٍ حَفِيظٍ
Hausa
 
"Wannan shĩ ne abin da ake yi muku wa'adi da shi ga dukan mai yawan kőmawa ga Allah, mai tsarewar (umurninSa).

Ayah   50:33   الأية
مَّنْ خَشِيَ الرَّحْمَٰنَ بِالْغَيْبِ وَجَاءَ بِقَلْبٍ مُّنِيبٍ
Hausa
 
"Wanda ya ji tsőron Mai rahama a fake, kuma ya zo da wata irin zũciya mai tawakkali."

Ayah   50:34   الأية
ادْخُلُوهَا بِسَلَامٍ ۖ ذَٰلِكَ يَوْمُ الْخُلُودِ
Hausa
 
(A ce musu) "Ku shige ta da aminci, waccan ita ce rănar dawwama."

Ayah   50:35   الأية
لَهُم مَّا يَشَاءُونَ فِيهَا وَلَدَيْنَا مَزِيدٌ
Hausa
 
Sună da abin da suke so a cikinta, kuma tăre da Mũ akwai ƙărin ni'ima,

Ayah   50:36   الأية
وَكَمْ أَهْلَكْنَا قَبْلَهُم مِّن قَرْنٍ هُمْ أَشَدُّ مِنْهُم بَطْشًا فَنَقَّبُوا فِي الْبِلَادِ هَلْ مِن مَّحِيصٍ
Hausa
 
Kuma da yawa Muka halakar, a gabăninsu, (mutănen yanzu) ɗaga waɗansu al'ummomi, (waɗanda suke) sũ ne mafi ƙarfin damƙa daga gare su, sa'an nan suka yi bincike a cikin ƙasăshe: 'Kő akwai wurin tsĩra'? ( Babu).

Ayah   50:37   الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَذِكْرَىٰ لِمَن كَانَ لَهُ قَلْبٌ أَوْ أَلْقَى السَّمْعَ وَهُوَ شَهِيدٌ
Hausa
 
Lalle ne, a cikin wancan, akwai tunătarwa ga wanda zũciyarsa ta kasance gare shi, kő kuwa ya jẽfa saurăro, alhăli kuwa yană halarce (da hankalinsa).

Ayah   50:38   الأية
وَلَقَدْ خَلَقْنَا السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا فِي سِتَّةِ أَيَّامٍ وَمَا مَسَّنَا مِن لُّغُوبٍ
Hausa
 
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta sammai da ƙasă da abin da ke a tsakăninsu, a cikin kwănaki shida, alhăli wata'yar wahala ba ta shăfe Mu ba.

Ayah   50:39   الأية
فَاصْبِرْ عَلَىٰ مَا يَقُولُونَ وَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ قَبْلَ طُلُوعِ الشَّمْسِ وَقَبْلَ الْغُرُوبِ
Hausa
 
Sabőda haka, ka yi haƙuri a kan abin da suke fadă, kuma ka yi tasĩhi game da gődẽ wa Ubangijinka (watau ka yi salla) a gabănin fitőwar rănă da gabănin ɓacẽwarta.

Ayah   50:40   الأية
وَمِنَ اللَّيْلِ فَسَبِّحْهُ وَأَدْبَارَ السُّجُودِ
Hausa
 
Kuma daga dare, sai ka yi tasbĩhi a gare Shi da băyan sujada.

Ayah   50:41   الأية
وَاسْتَمِعْ يَوْمَ يُنَادِ الْمُنَادِ مِن مَّكَانٍ قَرِيبٍ
Hausa
 
Kuma ka saurăra a rănar da mai kira ke yin kira daga wuri makusanci.

Ayah   50:42   الأية
يَوْمَ يَسْمَعُونَ الصَّيْحَةَ بِالْحَقِّ ۚ ذَٰلِكَ يَوْمُ الْخُرُوجِ
Hausa
 
Rănar da suke saurăron tsăwa da gaskiya. Wancan shĩ ne yinin fita (daga kabari).

Ayah   50:43   الأية
إِنَّا نَحْنُ نُحْيِي وَنُمِيتُ وَإِلَيْنَا الْمَصِيرُ
Hausa
 
Lalle Mũ ne haƙĩƙa, Mu ne ke răyarwa, kuma Mũ ne ke kashẽwa, kuma zuwa gare Mu kawai ne makőmar take.

Ayah   50:44   الأية
يَوْمَ تَشَقَّقُ الْأَرْضُ عَنْهُمْ سِرَاعًا ۚ ذَٰلِكَ حَشْرٌ عَلَيْنَا يَسِيرٌ
Hausa
 
Rănar da ƙasă ke tsattsăgẽwa daga gare su, sună măsu gaggăwa. Wancan tărăwar mutăne ne, mai sauƙi a gare Mu.

Ayah   50:45   الأية
نَّحْنُ أَعْلَمُ بِمَا يَقُولُونَ ۖ وَمَا أَنتَ عَلَيْهِم بِجَبَّارٍ ۖ فَذَكِّرْ بِالْقُرْآنِ مَن يَخَافُ وَعِيدِ
Hausa
 
Mũ ne mafi sani game da abin da suke faɗi, kuma bă ză ka zama mai tĩlasta su ba. Sabőda haka ka tunatar game da Alƙur'ani, ga wanda ke tsőron ƙyacewaTa.
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us