First Ayah 1 الأية الأوليبِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الرَّحْمَٰنُ
Hausa
(Allah) Mai rahama.
|
Ayah 55:2 الأية
عَلَّمَ الْقُرْآنَ
Hausa
Yã sanar da Alƙur'ani.
|
Ayah 55:3 الأية
خَلَقَ الْإِنسَانَ
Hausa
Yã halitta mutum.
|
Ayah 55:4 الأية
عَلَّمَهُ الْبَيَانَ
Hausa
Yã sanar da shi bayãni (magana).
|
Ayah 55:5 الأية
الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ بِحُسْبَانٍ
Hausa
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.
|
Ayah 55:6 الأية
وَالنَّجْمُ وَالشَّجَرُ يَسْجُدَانِ
Hausa
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.
|
Ayah 55:7 الأية
وَالسَّمَاءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ الْمِيزَانَ
Hausa
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.
|
Ayah 55:8 الأية
أَلَّا تَطْغَوْا فِي الْمِيزَانِ
Hausa
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.
|
Ayah 55:9 الأية
وَأَقِيمُوا الْوَزْنَ بِالْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا الْمِيزَانَ
Hausa
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.
|
Ayah 55:10 الأية
وَالْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ
Hausa
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.
|
Ayah 55:11 الأية
فِيهَا فَاكِهَةٌ وَالنَّخْلُ ذَاتُ الْأَكْمَامِ
Hausa
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.
|
Ayah 55:12 الأية
وَالْحَبُّ ذُو الْعَصْفِ وَالرَّيْحَانُ
Hausa
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.
|
Ayah 55:13 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:14 الأية
خَلَقَ الْإِنسَانَ مِن صَلْصَالٍ كَالْفَخَّارِ
Hausa
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.
|
Ayah 55:15 الأية
وَخَلَقَ الْجَانَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍ
Hausa
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.
|
Ayah 55:16 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:17 الأية
رَبُّ الْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ الْمَغْرِبَيْنِ
Hausa
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
|
Ayah 55:18 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:19 الأية
مَرَجَ الْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ
Hausa
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
|
Ayah 55:20 الأية
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لَّا يَبْغِيَانِ
Hausa
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
|
Ayah 55:21 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:22 الأية
يَخْرُجُ مِنْهُمَا اللُّؤْلُؤُ وَالْمَرْجَانُ
Hausa
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
|
Ayah 55:23 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:24 الأية
وَلَهُ الْجَوَارِ الْمُنشَآتُ فِي الْبَحْرِ كَالْأَعْلَامِ
Hausa
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan
duwãtsu.
|
Ayah 55:25 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:26 الأية
كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍ
Hausa
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.
|
Ayah 55:27 الأية
وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ
Hausa
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.
|
Ayah 55:28 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:29 الأية
يَسْأَلُهُ مَن فِي السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِي شَأْنٍ
Hausa
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin
wani sha'ani.
|
Ayah 55:30 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:31 الأية
سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ الثَّقَلَانِ
Hausa
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!
|
Ayah 55:32 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:33 الأية
يَا مَعْشَرَ الْجِنِّ وَالْإِنسِ إِنِ اسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا مِنْ أَقْطَارِ
السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ فَانفُذُوا ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَانٍ
Hausa
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã
to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.
|
Ayah 55:34 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:35 الأية
يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلَا تَنتَصِرَانِ
Hausa
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã
ku nẽmi taimako ba?
|
Ayah 55:36 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:37 الأية
فَإِذَا انشَقَّتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَالدِّهَانِ
Hausa
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.
|
Ayah 55:38 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:39 الأية
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُسْأَلُ عَن ذَنبِهِ إِنسٌ وَلَا جَانٌّ
Hausa
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.
|
Ayah 55:40 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:41 الأية
يُعْرَفُ الْمُجْرِمُونَ بِسِيمَاهُمْ فَيُؤْخَذُ بِالنَّوَاصِي وَالْأَقْدَامِ
Hausa
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da
sãwãyensu.
|
Ayah 55:42 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:43 الأية
هَٰذِهِ جَهَنَّمُ الَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا الْمُجْرِمُونَ
Hausa
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.
|
Ayah 55:44 الأية
يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ آنٍ
Hausa
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.
|
Ayah 55:45 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:46 الأية
وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ جَنَّتَانِ
Hausa
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.
|
Ayah 55:47 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:48 الأية
ذَوَاتَا أَفْنَانٍ
Hausa
Mãsu rassan itãce.
|
Ayah 55:49 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:50 الأية
فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ
Hausa
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.
|
Ayah 55:51 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:52 الأية
فِيهِمَا مِن كُلِّ فَاكِهَةٍ زَوْجَانِ
Hausa
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.
|
Ayah 55:53 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:54 الأية
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ فُرُشٍ بَطَائِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍ ۚ وَجَنَى
الْجَنَّتَيْنِ دَانٍ
Hausa
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma
nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.
|
Ayah 55:55 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:56 الأية
فِيهِنَّ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ
Hausa
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai
ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.
|
Ayah 55:57 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:58 الأية
كَأَنَّهُنَّ الْيَاقُوتُ وَالْمَرْجَانُ
Hausa
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.
|
Ayah 55:59 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:60 الأية
هَلْ جَزَاءُ الْإِحْسَانِ إِلَّا الْإِحْسَانُ
Hausa
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.
|
Ayah 55:61 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:62 الأية
وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ
Hausa
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.
|
Ayah 55:63 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:64 الأية
مُدْهَامَّتَانِ
Hausa
Mãsu duhun inuwa.
|
Ayah 55:65 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:66 الأية
فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ
Hausa
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.
|
Ayah 55:67 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:68 الأية
فِيهِمَا فَاكِهَةٌ وَنَخْلٌ وَرُمَّانٌ
Hausa
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.
|
Ayah 55:69 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:70 الأية
فِيهِنَّ خَيْرَاتٌ حِسَانٌ
Hausa
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.
|
Ayah 55:71 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:72 الأية
حُورٌ مَّقْصُورَاتٌ فِي الْخِيَامِ
Hausa
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.
|
Ayah 55:73 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:74 الأية
لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ
Hausa
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.
|
Ayah 55:75 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:76 الأية
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍ وَعَبْقَرِيٍّ حِسَانٍ
Hausa
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.
|
Ayah 55:77 الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
|
Ayah 55:78 الأية
تَبَارَكَ اسْمُ رَبِّكَ ذِي الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ
Hausa
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|