« Prev

55. Surah Ar-Rahmân سورة الرحمن

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الرَّحْمَٰنُ
Hausa
 
(Allah) Mai rahama.

Ayah   55:2   الأية
عَلَّمَ الْقُرْآنَ
Hausa
 
Yã sanar da Alƙur'ani.

Ayah   55:3   الأية
خَلَقَ الْإِنسَانَ
Hausa
 
Yã halitta mutum.

Ayah   55:4   الأية
عَلَّمَهُ الْبَيَانَ
Hausa
 
Yã sanar da shi bayãni (magana).

Ayah   55:5   الأية
الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ بِحُسْبَانٍ
Hausa
 
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.

Ayah   55:6   الأية
وَالنَّجْمُ وَالشَّجَرُ يَسْجُدَانِ
Hausa
 
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.

Ayah   55:7   الأية
وَالسَّمَاءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ الْمِيزَانَ
Hausa
 
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.

Ayah   55:8   الأية
أَلَّا تَطْغَوْا فِي الْمِيزَانِ
Hausa
 
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.

Ayah   55:9   الأية
وَأَقِيمُوا الْوَزْنَ بِالْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا الْمِيزَانَ
Hausa
 
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.

Ayah   55:10   الأية
وَالْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ
Hausa
 
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.

Ayah   55:11   الأية
فِيهَا فَاكِهَةٌ وَالنَّخْلُ ذَاتُ الْأَكْمَامِ
Hausa
 
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.

Ayah   55:12   الأية
وَالْحَبُّ ذُو الْعَصْفِ وَالرَّيْحَانُ
Hausa
 
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.

Ayah   55:13   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:14   الأية
خَلَقَ الْإِنسَانَ مِن صَلْصَالٍ كَالْفَخَّارِ
Hausa
 
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.

Ayah   55:15   الأية
وَخَلَقَ الْجَانَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍ
Hausa
 
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.

Ayah   55:16   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:17   الأية
رَبُّ الْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ الْمَغْرِبَيْنِ
Hausa
 
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.

Ayah   55:18   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:19   الأية
مَرَجَ الْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ
Hausa
 
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.

Ayah   55:20   الأية
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لَّا يَبْغِيَانِ
Hausa
 
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.

Ayah   55:21   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:22   الأية
يَخْرُجُ مِنْهُمَا اللُّؤْلُؤُ وَالْمَرْجَانُ
Hausa
 
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.

Ayah   55:23   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:24   الأية
وَلَهُ الْجَوَارِ الْمُنشَآتُ فِي الْبَحْرِ كَالْأَعْلَامِ
Hausa
 
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.

Ayah   55:25   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:26   الأية
كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍ
Hausa
 
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.

Ayah   55:27   الأية
وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ
Hausa
 
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.

Ayah   55:28   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:29   الأية
يَسْأَلُهُ مَن فِي السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِي شَأْنٍ
Hausa
 
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.

Ayah   55:30   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:31   الأية
سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ الثَّقَلَانِ
Hausa
 
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!

Ayah   55:32   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:33   الأية
يَا مَعْشَرَ الْجِنِّ وَالْإِنسِ إِنِ اسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا مِنْ أَقْطَارِ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ فَانفُذُوا ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَانٍ
Hausa
 
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.

Ayah   55:34   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:35   الأية
يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلَا تَنتَصِرَانِ
Hausa
 
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?

Ayah   55:36   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:37   الأية
فَإِذَا انشَقَّتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَالدِّهَانِ
Hausa
 
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.

Ayah   55:38   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:39   الأية
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُسْأَلُ عَن ذَنبِهِ إِنسٌ وَلَا جَانٌّ
Hausa
 
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.

Ayah   55:40   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:41   الأية
يُعْرَفُ الْمُجْرِمُونَ بِسِيمَاهُمْ فَيُؤْخَذُ بِالنَّوَاصِي وَالْأَقْدَامِ
Hausa
 
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.

Ayah   55:42   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:43   الأية
هَٰذِهِ جَهَنَّمُ الَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا الْمُجْرِمُونَ
Hausa
 
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.

Ayah   55:44   الأية
يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ آنٍ
Hausa
 
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.

Ayah   55:45   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:46   الأية
وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ جَنَّتَانِ
Hausa
 
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.

Ayah   55:47   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:48   الأية
ذَوَاتَا أَفْنَانٍ
Hausa
 
Mãsu rassan itãce.

Ayah   55:49   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:50   الأية
فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ
Hausa
 
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.

Ayah   55:51   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:52   الأية
فِيهِمَا مِن كُلِّ فَاكِهَةٍ زَوْجَانِ
Hausa
 
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.

Ayah   55:53   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:54   الأية
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ فُرُشٍ بَطَائِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍ ۚ وَجَنَى الْجَنَّتَيْنِ دَانٍ
Hausa
 
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.

Ayah   55:55   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:56   الأية
فِيهِنَّ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ
Hausa
 
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.

Ayah   55:57   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:58   الأية
كَأَنَّهُنَّ الْيَاقُوتُ وَالْمَرْجَانُ
Hausa
 
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.

Ayah   55:59   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:60   الأية
هَلْ جَزَاءُ الْإِحْسَانِ إِلَّا الْإِحْسَانُ
Hausa
 
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.

Ayah   55:61   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:62   الأية
وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ
Hausa
 
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.

Ayah   55:63   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:64   الأية
مُدْهَامَّتَانِ
Hausa
 
Mãsu duhun inuwa.

Ayah   55:65   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:66   الأية
فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ
Hausa
 
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.

Ayah   55:67   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:68   الأية
فِيهِمَا فَاكِهَةٌ وَنَخْلٌ وَرُمَّانٌ
Hausa
 
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.

Ayah   55:69   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:70   الأية
فِيهِنَّ خَيْرَاتٌ حِسَانٌ
Hausa
 
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.

Ayah   55:71   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:72   الأية
حُورٌ مَّقْصُورَاتٌ فِي الْخِيَامِ
Hausa
 
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.

Ayah   55:73   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:74   الأية
لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ
Hausa
 
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.

Ayah   55:75   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:76   الأية
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍ وَعَبْقَرِيٍّ حِسَانٍ
Hausa
 
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.

Ayah   55:77   الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah   55:78   الأية
تَبَارَكَ اسْمُ رَبِّكَ ذِي الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ
Hausa
 
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka. 
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us