« Prev

57. Surah Al-Hadîd سورة الحديد

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
سَبَّحَ لِلَّهِ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۖ وَهُوَ الْعَزِيزُ الْحَكِيمُ
Hausa
 
Abin da ke cikin sammai da ƙasa yă yi tasbĩhi ga Allah. Kuma Shĩ ne Mabuwăyi, Mai hikima.

Ayah   57:2   الأية
لَهُ مُلْكُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۖ يُحْيِي وَيُمِيتُ ۖ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ
Hausa
 
Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa: Yană răyarwa kuma Yană kashẽwa, kuma Shĩ Mai ikon yi ne a kan kőme.

Ayah   57:3   الأية
هُوَ الْأَوَّلُ وَالْآخِرُ وَالظَّاهِرُ وَالْبَاطِنُ ۖ وَهُوَ بِكُلِّ شَيْءٍ عَلِيمٌ
Hausa
 
Shĩ ne Na farko, Na ƙarshe, Bayyananne, Bőyayye, kuma Shĩ Masani ne ga dukkan kőme.

Ayah   57:4   الأية
هُوَ الَّذِي خَلَقَ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ فِي سِتَّةِ أَيَّامٍ ثُمَّ اسْتَوَىٰ عَلَى الْعَرْشِ ۚ يَعْلَمُ مَا يَلِجُ فِي الْأَرْضِ وَمَا يَخْرُجُ مِنْهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ السَّمَاءِ وَمَا يَعْرُجُ فِيهَا ۖ وَهُوَ مَعَكُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ ۚ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ بَصِيرٌ
Hausa
 
Shĩ ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin wasu kwănuka shida, sa'an nan Ya daidaitu a kan Al'arshi, Yană sanin abin da ke shiga cikin ƙasa da abin da ke fita daga gare ta, da abin da ke sauka daga sama da abin da ke hawa cikinta, kuma Shĩ yană tareda ku duk inda kuka kasance. Kuma Allah Mai gani ne ga abin da kuke aikatăwa.

Ayah   57:5   الأية
لَّهُ مُلْكُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ وَإِلَى اللَّهِ تُرْجَعُ الْأُمُورُ
Hausa
 
Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma zuwa gare Shĩ (Allah) kawai ake mayar da al'amura.

Ayah   57:6   الأية
يُولِجُ اللَّيْلَ فِي النَّهَارِ وَيُولِجُ النَّهَارَ فِي اللَّيْلِ ۚ وَهُوَ عَلِيمٌ بِذَاتِ الصُّدُورِ
Hausa
 
Yană shigar da dare a cikin yini, kuma Yană shigar da yini a cikin dare, kuma Shi Masani ne ga abin da yake a cikin ƙirăza.

Ayah   57:7   الأية
آمِنُوا بِاللَّهِ وَرَسُولِهِ وَأَنفِقُوا مِمَّا جَعَلَكُم مُّسْتَخْلَفِينَ فِيهِ ۖ فَالَّذِينَ آمَنُوا مِنكُمْ وَأَنفَقُوا لَهُمْ أَجْرٌ كَبِيرٌ
Hausa
 
Ku yi ĩmăni da Allah da ManzonSa, kuma ku ciyar daga abin da Allah Ya wakilta ku a cikinsa (na dũkiya). To, waɗannan da suka yi ĩmăni daga cikinku, kuma suka ciyar, sună da wani sakamako mai girma.

Ayah   57:8   الأية
وَمَا لَكُمْ لَا تُؤْمِنُونَ بِاللَّهِ ۙ وَالرَّسُولُ يَدْعُوكُمْ لِتُؤْمِنُوا بِرَبِّكُمْ وَقَدْ أَخَذَ مِيثَاقَكُمْ إِن كُنتُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
 
kuma me ya same ku, bă ză ku yi ĩmăni ba da Allah, alhăli kuwa manzonSa na kiran ku dőmin ku yi ĩmăni da Ubangijinku, kuma lalle Allah Ya karɓi alkawarinku (cẽwa ză ku bauta Masa)? (Ku bauta Masa) idan kun kasance măsu ĩmăni.

Ayah   57:9   الأية
هُوَ الَّذِي يُنَزِّلُ عَلَىٰ عَبْدِهِ آيَاتٍ بَيِّنَاتٍ لِّيُخْرِجَكُم مِّنَ الظُّلُمَاتِ إِلَى النُّورِ ۚ وَإِنَّ اللَّهَ بِكُمْ لَرَءُوفٌ رَّحِيمٌ
Hausa
 
Shĩ ne wanda ke sassaukar da ăyőyi bayyanannu ga BăwanSa, dőmin Ya fitar da ku daga duffai zuwa ga haske, kuma lalle Allah haƙĩƙa Mai tausayi ne gare ku, Mai jin ƙai.

Ayah   57:10   الأية
وَمَا لَكُمْ أَلَّا تُنفِقُوا فِي سَبِيلِ اللَّهِ وَلِلَّهِ مِيرَاثُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ لَا يَسْتَوِي مِنكُم مَّنْ أَنفَقَ مِن قَبْلِ الْفَتْحِ وَقَاتَلَ ۚ أُولَٰئِكَ أَعْظَمُ دَرَجَةً مِّنَ الَّذِينَ أَنفَقُوا مِن بَعْدُ وَقَاتَلُوا ۚ وَكُلًّا وَعَدَ اللَّهُ الْحُسْنَىٰ ۚ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ خَبِيرٌ
Hausa
 
Kuma me ya săme ku, bă ză ku ciyar ba dőmin ɗaukaka kalmar Allah, alhăli kuwa gădon sammai da ƙasă na Allah ne? Wanda ya ciyar a gabănin cin nasara, kuma ya yi yăƙi daga cikinku, bă ya zama daidai (da wanda bai yi haka ba). waɗancan ne mafĩfĩta girman daraja bisa ga waɗanda suka ciyar daga băya kuma suka yi yăƙi. Kuma dukansu Allah Ya yi musu wa'adi da (sakamako) mai kyau, kuma Allah Masani ne ga abin da kuke aikatăwa.

Ayah   57:11   الأية
مَّن ذَا الَّذِي يُقْرِضُ اللَّهَ قَرْضًا حَسَنًا فَيُضَاعِفَهُ لَهُ وَلَهُ أَجْرٌ كَرِيمٌ
Hausa
 
Wăne ne wanda zai ranta wa Allah rance mai kyau dőmin Allah Ya ninka masa shi (a dũniya)kuma Yană da wani sakamako na karimci (a Lăhira)?

Ayah   57:12   الأية
يَوْمَ تَرَى الْمُؤْمِنِينَ وَالْمُؤْمِنَاتِ يَسْعَىٰ نُورُهُم بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَبِأَيْمَانِهِم بُشْرَاكُمُ الْيَوْمَ جَنَّاتٌ تَجْرِي مِن تَحْتِهَا الْأَنْهَارُ خَالِدِينَ فِيهَا ۚ ذَٰلِكَ هُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ
Hausa
 
Rănar da ză ka ga mũminai maza da mũminai mătă haskensu nă tafiya a gaba gare su, da kuma dăma gare su. (Ană ce musu) "Bushărarku a yau, ita ce gidajen Aljanna." Ruwa na gudăna daga ƙarƙashinsu sună măsu dawwama a cikinsu. Wannan, shĩ ne babban rabo mai girma.

Ayah   57:13   الأية
يَوْمَ يَقُولُ الْمُنَافِقُونَ وَالْمُنَافِقَاتُ لِلَّذِينَ آمَنُوا انظُرُونَا نَقْتَبِسْ مِن نُّورِكُمْ قِيلَ ارْجِعُوا وَرَاءَكُمْ فَالْتَمِسُوا نُورًا فَضُرِبَ بَيْنَهُم بِسُورٍ لَّهُ بَابٌ بَاطِنُهُ فِيهِ الرَّحْمَةُ وَظَاهِرُهُ مِن قِبَلِهِ الْعَذَابُ
Hausa
 
Rănar da munafikai maza da munăfikai mătă ke cẽwa waɗanda suka yi ĩmăni: "Ku dũbẽ mu, mu yi makămashi daga haskenku!" A ce (musu): "Ku kőma a băyanku, dőmin ku nẽmo wani haske." Sai a danne a tsakăninsu da wani găru yană da wani ƙyaure, a cikinsa nan rahama take, kuma a băyansa daga wajensa azaba take.

Ayah   57:14   الأية
يُنَادُونَهُمْ أَلَمْ نَكُن مَّعَكُمْ ۖ قَالُوا بَلَىٰ وَلَٰكِنَّكُمْ فَتَنتُمْ أَنفُسَكُمْ وَتَرَبَّصْتُمْ وَارْتَبْتُمْ وَغَرَّتْكُمُ الْأَمَانِيُّ حَتَّىٰ جَاءَ أَمْرُ اللَّهِ وَغَرَّكُم بِاللَّهِ الْغَرُورُ
Hausa
 
Sună kiran su, "Ashe, bă tăre muke da ku ba?" Su ce: "Ĩ, amma kũ, kun fitini kanku, kuma kun yi jiran wata masĩfa, kuma kunyi shakka, kuma waɗansu gũrace-gũrace sun rũɗe ku, har umurnin Allah ya jẽ muku, kumamarũɗi ya rũɗe ku game da Allah."

Ayah   57:15   الأية
فَالْيَوْمَ لَا يُؤْخَذُ مِنكُمْ فِدْيَةٌ وَلَا مِنَ الَّذِينَ كَفَرُوا ۚ مَأْوَاكُمُ النَّارُ ۖ هِيَ مَوْلَاكُمْ ۖ وَبِئْسَ الْمَصِيرُ
Hausa
 
"To, a yau bă ză a karɓi fansa daga gare ku ba. Kuma bă ză a karɓa daga waɗanda suka kăfirta ba. Makőmarku wută ce, ita ce mai dacẽwa da ku, kuma makőmarku ɗin nan tă mũnana."

Ayah   57:16   الأية
أَلَمْ يَأْنِ لِلَّذِينَ آمَنُوا أَن تَخْشَعَ قُلُوبُهُمْ لِذِكْرِ اللَّهِ وَمَا نَزَلَ مِنَ الْحَقِّ وَلَا يَكُونُوا كَالَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ مِن قَبْلُ فَطَالَ عَلَيْهِمُ الْأَمَدُ فَقَسَتْ قُلُوبُهُمْ ۖ وَكَثِيرٌ مِّنْهُمْ فَاسِقُونَ
Hausa
 
Shin, lőkaci bai yi ba ga wa ɗanda suka yi ĩmănĩ zukătansu su yi tawălu'i ga ambaton Allah da abin da ya sauka daga gaskiya? Kada su kasance kamar waɗanda aka bai wa littăfi a gabănin haka, sai zămani ya yi tsawo a kansu, sabőda haka zukătansu suka ƙẽƙashe, kuma masu yawa daga cikinsu făsiƙai ne.

Ayah   57:17   الأية
اعْلَمُوا أَنَّ اللَّهَ يُحْيِي الْأَرْضَ بَعْدَ مَوْتِهَا ۚ قَدْ بَيَّنَّا لَكُمُ الْآيَاتِ لَعَلَّكُمْ تَعْقِلُونَ
Hausa
 
Ku sani cẽwa Allah Yană răyar da ƙasă a băyan mutuwarta. Lalle Mun bayyanamuku ăyőyi da fatan ză ku yi hankali.

Ayah   57:18   الأية
إِنَّ الْمُصَّدِّقِينَ وَالْمُصَّدِّقَاتِ وَأَقْرَضُوا اللَّهَ قَرْضًا حَسَنًا يُضَاعَفُ لَهُمْ وَلَهُمْ أَجْرٌ كَرِيمٌ
Hausa
 
Lalle măsu gaskatăwa maza da măsu gaskatăwa mătă, kuma suka ranta wa Allah rance mai kyau, ană riɓanya musu, kuma suna da wani sakamako na karimci.

Ayah   57:19   الأية
وَالَّذِينَ آمَنُوا بِاللَّهِ وَرُسُلِهِ أُولَٰئِكَ هُمُ الصِّدِّيقُونَ ۖ وَالشُّهَدَاءُ عِندَ رَبِّهِمْ لَهُمْ أَجْرُهُمْ وَنُورُهُمْ ۖ وَالَّذِينَ كَفَرُوا وَكَذَّبُوا بِآيَاتِنَا أُولَٰئِكَ أَصْحَابُ الْجَحِيمِ
Hausa
 
Kuma waɗanda suka yi ĩmăni da Allah da MazanninSa waɗannan sũ ne kamălar gaskatăwa kuma su ne măsu shahăda awurin Ubangjinsu. sună da sakamakonsu da haskensu. waɗanda suka kafirta kuma suka ƙaryata game da ăyőyinMu, waɗannan su ne'yan Jahĩm.

Ayah   57:20   الأية
اعْلَمُوا أَنَّمَا الْحَيَاةُ الدُّنْيَا لَعِبٌ وَلَهْوٌ وَزِينَةٌ وَتَفَاخُرٌ بَيْنَكُمْ وَتَكَاثُرٌ فِي الْأَمْوَالِ وَالْأَوْلَادِ ۖ كَمَثَلِ غَيْثٍ أَعْجَبَ الْكُفَّارَ نَبَاتُهُ ثُمَّ يَهِيجُ فَتَرَاهُ مُصْفَرًّا ثُمَّ يَكُونُ حُطَامًا ۖ وَفِي الْآخِرَةِ عَذَابٌ شَدِيدٌ وَمَغْفِرَةٌ مِّنَ اللَّهِ وَرِضْوَانٌ ۚ وَمَا الْحَيَاةُ الدُّنْيَا إِلَّا مَتَاعُ الْغُرُورِ
Hausa
 
Ku sani cẽwa răyuwar dũniya wăsă ɗai ce da shagala da ƙawa da alafahri a tsakăninku da găsar wadăta ta dũkiya da ɗiya, kamar misălin shũka wadda yabanyarta ta băyar da sha'awa ga manőma, sa'an nan ta ƙẽƙashe, har ka ganta tă zama rawaya sa'an nan ta kőma rauno. Kuma, alămra akwai azăba mai tsanani da găfara daga Allah da yarda. Kuma răyuwar dũniya ba ta zama ba făce ɗan jin dăɗin rũɗi kawai.

Ayah   57:21   الأية
سَابِقُوا إِلَىٰ مَغْفِرَةٍ مِّن رَّبِّكُمْ وَجَنَّةٍ عَرْضُهَا كَعَرْضِ السَّمَاءِ وَالْأَرْضِ أُعِدَّتْ لِلَّذِينَ آمَنُوا بِاللَّهِ وَرُسُلِهِ ۚ ذَٰلِكَ فَضْلُ اللَّهِ يُؤْتِيهِ مَن يَشَاءُ ۚ وَاللَّهُ ذُو الْفَضْلِ الْعَظِيمِ
Hausa
 
Ku yi tsẽre zuwa ga (nẽman) găfara daga Ubangjinku, da Aljanna făɗinta kamar făɗin samă da ƙasă ne, an yi tattalinta dőmin waɗanda suka yi ĩmăni da Allah da ManzanninSa. Wannan falalar Allah ce, Yană băyar da ita ga wanda Ya so. Kuma Allah Mai falala ne Mai girma.

Ayah   57:22   الأية
مَا أَصَابَ مِن مُّصِيبَةٍ فِي الْأَرْضِ وَلَا فِي أَنفُسِكُمْ إِلَّا فِي كِتَابٍ مِّن قَبْلِ أَن نَّبْرَأَهَا ۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى اللَّهِ يَسِيرٌ
Hausa
 
Wata masifa bă ză ta auku ba a cikin ƙasă kő a cikin rayukanku făce tană a cikin littăfi a gabănin Mu halitta ta. Lalle wannan, ga Allah, mai sauƙi ne.

Ayah   57:23   الأية
لِّكَيْلَا تَأْسَوْا عَلَىٰ مَا فَاتَكُمْ وَلَا تَفْرَحُوا بِمَا آتَاكُمْ ۗ وَاللَّهُ لَا يُحِبُّ كُلَّ مُخْتَالٍ فَخُورٍ
Hausa
 
Dőmin kada ku yi baƙin ciki a kan abin da ya kuɓuce muku, kuma kada ku yi mumar alfahari da abin da Ya bă ku. Kuma Allah bă Ya son dukkan mai tăƙama, mai alfahari.

Ayah   57:24   الأية
الَّذِينَ يَبْخَلُونَ وَيَأْمُرُونَ النَّاسَ بِالْبُخْلِ ۗ وَمَن يَتَوَلَّ فَإِنَّ اللَّهَ هُوَ الْغَنِيُّ الْحَمِيدُ
Hausa
 
Watau, waɗanda ke yin rőwa, kuma sună umumin mutăne da yin rőwa. Kuma wanda ya jũya băya, to, lalle Allah, Shĩ ne kaɗai Mawadăci, Gődadde.

Ayah   57:25   الأية
لَقَدْ أَرْسَلْنَا رُسُلَنَا بِالْبَيِّنَاتِ وَأَنزَلْنَا مَعَهُمُ الْكِتَابَ وَالْمِيزَانَ لِيَقُومَ النَّاسُ بِالْقِسْطِ ۖ وَأَنزَلْنَا الْحَدِيدَ فِيهِ بَأْسٌ شَدِيدٌ وَمَنَافِعُ لِلنَّاسِ وَلِيَعْلَمَ اللَّهُ مَن يَنصُرُهُ وَرُسُلَهُ بِالْغَيْبِ ۚ إِنَّ اللَّهَ قَوِيٌّ عَزِيزٌ
Hausa
 
Haƙĩƙa, lalle Mun aiko ManzanninMu da hujjőji bayyanannu, kuma Muka saukar da Littăfi da sikẽli tăre da su dőmin mutăne su tsayu da ădalci, kuma Mun saukar da baƙin ƙarfe, a cikinsa akwai cutarwa mai tsanani da amfăni ga mutăne, kuma dőmin Allah Ya san mai taimakonSa da ManzanninSa a fake. Lalle ne Allah Mai ƙarfi ne, Mabuwăyi.

Ayah   57:26   الأية
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا نُوحًا وَإِبْرَاهِيمَ وَجَعَلْنَا فِي ذُرِّيَّتِهِمَا النُّبُوَّةَ وَالْكِتَابَ ۖ فَمِنْهُم مُّهْتَدٍ ۖ وَكَثِيرٌ مِّنْهُمْ فَاسِقُونَ
Hausa
 
Kuma haƙĩƙa, lalle, Mun aiki Nũhu da Ibrahĩm, kuma Muka sanya Annabci da Littĩfi a cikin zuriyarsu; daga cikinsu akwai mai nẽman shiryuwa, kuma măsu yawa daga cikinsu fasiƙai ne.

Ayah   57:27   الأية
ثُمَّ قَفَّيْنَا عَلَىٰ آثَارِهِم بِرُسُلِنَا وَقَفَّيْنَا بِعِيسَى ابْنِ مَرْيَمَ وَآتَيْنَاهُ الْإِنجِيلَ وَجَعَلْنَا فِي قُلُوبِ الَّذِينَ اتَّبَعُوهُ رَأْفَةً وَرَحْمَةً وَرَهْبَانِيَّةً ابْتَدَعُوهَا مَا كَتَبْنَاهَا عَلَيْهِمْ إِلَّا ابْتِغَاءَ رِضْوَانِ اللَّهِ فَمَا رَعَوْهَا حَقَّ رِعَايَتِهَا ۖ فَآتَيْنَا الَّذِينَ آمَنُوا مِنْهُمْ أَجْرَهُمْ ۖ وَكَثِيرٌ مِّنْهُمْ فَاسِقُونَ
Hausa
 
Sa'an nan Muka biyar a băyansu da ManzanninMu; kuma Muka biyar da ĩsă ɗan Maryama, kuma Muka ba shi Linjila kuma Muka sanya tausayi da rahama a cikin zukătan waɗanda suka bĩ shi, da ruhbănanci wanda suka ƙăga, shi, ba Mu rubũta shi ba a kansu, făce dai (Mun rubũta musu nẽman yardar Allah, sa'an nan ba su tsare shi haƙƙin tsarẽwarsa ba, sabőda haka Muka bai wa waɗanda suka yi ĩmăni daga cikinsu sakamakonsu kuma măsu yawa daga cikinsu făsiƙai ne.

Ayah   57:28   الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اتَّقُوا اللَّهَ وَآمِنُوا بِرَسُولِهِ يُؤْتِكُمْ كِفْلَيْنِ مِن رَّحْمَتِهِ وَيَجْعَل لَّكُمْ نُورًا تَمْشُونَ بِهِ وَيَغْفِرْ لَكُمْ ۚ وَاللَّهُ غَفُورٌ رَّحِيمٌ
Hausa
 
Yă kũ waɗanda suka yi ĩmăni! Ku bi Allah da taƙawa, ku yi ĩmăni da ManzonSa Ya bă ku rabo biyu daga rahamarSa, kuma Ya sanya muku wani haske wanda kuke yin tafiya da shi, kuma Ya găfarta muku. Kuma Allah Mai găfara ne, Mai rahama.

Ayah   57:29   الأية
لِّئَلَّا يَعْلَمَ أَهْلُ الْكِتَابِ أَلَّا يَقْدِرُونَ عَلَىٰ شَيْءٍ مِّن فَضْلِ اللَّهِ ۙ وَأَنَّ الْفَضْلَ بِيَدِ اللَّهِ يُؤْتِيهِ مَن يَشَاءُ ۚ وَاللَّهُ ذُو الْفَضْلِ الْعَظِيمِ
Hausa
 
Dőmin kada mutănen Littăfi su san cẽwa lalle bă su da ikon yi ga kőme na falalar Allah, kuma ita falalar ga hannun Allah kawai take, Yană băyar da ita ga wanda Ya so (wannan jăhilci yă hana su ĩmani). Kuma Al1ah Mai falala ne mai girma.
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us