First Ayah 1 الأية الأوليبِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
يَسْأَلُونَكَ عَنِ الْأَنفَالِ ۖ قُلِ الْأَنفَالُ لِلَّهِ وَالرَّسُولِ ۖ
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَصْلِحُوا ذَاتَ بَيْنِكُمْ ۖ وَأَطِيعُوا اللَّهَ
وَرَسُولَهُ إِن كُنتُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
Suna tambayar ka ga ganĩma. ka ce: "Ganĩma ta Allah daManzonSa ce. Sai ku bi
Allah da taƙawa, kuma ku gyăra abin da yake a tsakăninku, kuma ku yi ɗă'a ga
Allah da ManzonSa, idan kun kasance mũminai."
|
Ayah 8:2 الأية
إِنَّمَا الْمُؤْمِنُونَ الَّذِينَ إِذَا ذُكِرَ اللَّهُ وَجِلَتْ قُلُوبُهُمْ
وَإِذَا تُلِيَتْ عَلَيْهِمْ آيَاتُهُ زَادَتْهُمْ إِيمَانًا وَعَلَىٰ رَبِّهِمْ
يَتَوَكَّلُونَ
Hausa
Abin sani kawai, nũminai sũ ne waɗanda suke idan an ambaci, Allah, zukătansu su
firgita, kuma idan an karanta ăyőyinSa a kansu, su ƙără musu wani ĩmăni, kuma ga
Ubangijinsu suke dőgara.
|
Ayah 8:3 الأية
الَّذِينَ يُقِيمُونَ الصَّلَاةَ وَمِمَّا رَزَقْنَاهُمْ يُنفِقُونَ
Hausa
Waɗanda suke tsayar da salla, kuma daga abin da Muka azũrtă su sună ciyarwa.
|
Ayah 8:4 الأية
أُولَٰئِكَ هُمُ الْمُؤْمِنُونَ حَقًّا ۚ لَّهُمْ دَرَجَاتٌ عِندَ رَبِّهِمْ
وَمَغْفِرَةٌ وَرِزْقٌ كَرِيمٌ
Hausa
Waɗannan sũ ne mũminai da gaskiya. Sună da darajőji a wurin Ubangijinsu, da wata
găfara da arziki na karimci.
|
Ayah 8:5 الأية
كَمَا أَخْرَجَكَ رَبُّكَ مِن بَيْتِكَ بِالْحَقِّ وَإِنَّ فَرِيقًا مِّنَ
الْمُؤْمِنِينَ لَكَارِهُونَ
Hausa
Kamar yadda Ubangijinka Ya fitar da kai daga gidanka da gaskiya, alhăli kuwa
lalle wani ɓangare na mũminai, haƙĩƙa, sună ƙyăma.
|
Ayah 8:6 الأية
يُجَادِلُونَكَ فِي الْحَقِّ بَعْدَمَا تَبَيَّنَ كَأَنَّمَا يُسَاقُونَ إِلَى
الْمَوْتِ وَهُمْ يَنظُرُونَ
Hausa
Sună jăyayya da kai a cikin (sha'anin) gaskiya a băyan tă bayYană, kamar dai
lalle ană kőra su zuwa ga mutuwa ne alhăli kuwa sună kallo.
|
Ayah 8:7 الأية
وَإِذْ يَعِدُكُمُ اللَّهُ إِحْدَى الطَّائِفَتَيْنِ أَنَّهَا لَكُمْ وَتَوَدُّونَ
أَنَّ غَيْرَ ذَاتِ الشَّوْكَةِ تَكُونُ لَكُمْ وَيُرِيدُ اللَّهُ أَن يُحِقَّ
الْحَقَّ بِكَلِمَاتِهِ وَيَقْطَعَ دَابِرَ الْكَافِرِينَ
Hausa
Kuma a lőkacin da Allah Yake yi muku alkawari da ɗayan ƙungiya biyu, cẽwa lalle
ita tăku ce: kuma kună gũrin cẽwa lalle ƙungiya wadda bă ta da ƙaya ta kasance
gare ku, kuma Allah Yană nufin Ya tabbatar da gaskiya da kalmőminSa, kuma Ya
kătse ƙarshen kăfirai;
|
Ayah 8:8 الأية
لِيُحِقَّ الْحَقَّ وَيُبْطِلَ الْبَاطِلَ وَلَوْ كَرِهَ الْمُجْرِمُونَ
Hausa
Dőmin Ya tabbatar da gaskiya, kuma Ya ɓăta ƙarya, kuma kődă măsu laifi sun ƙi.
|
Ayah 8:9 الأية
إِذْ تَسْتَغِيثُونَ رَبَّكُمْ فَاسْتَجَابَ لَكُمْ أَنِّي مُمِدُّكُم بِأَلْفٍ
مِّنَ الْمَلَائِكَةِ مُرْدِفِينَ
Hausa
A lőkacin da kuke nẽman Ubangijinku tairnako, sai Ya karɓa muku cẽwa: "Lalle ne
Nĩ, Mai taimakon ku ne da dubu daga mală'iku, jẽre."
|
Ayah 8:10 الأية
وَمَا جَعَلَهُ اللَّهُ إِلَّا بُشْرَىٰ وَلِتَطْمَئِنَّ بِهِ قُلُوبُكُمْ ۚ وَمَا
النَّصْرُ إِلَّا مِنْ عِندِ اللَّهِ ۚ إِنَّ اللَّهَ عَزِيزٌ حَكِيمٌ
Hausa
Kuma Allah bai sanya shi ba făce Dőmin bishăra, kuma dőmin zukătanku su natsu da
shi, kuma taimakon, bai zama ba făce daga wurin Allah; Lalle ne Allah Mabuwăyi
ne, Mai hikima.
|
Ayah 8:11 الأية
إِذْ يُغَشِّيكُمُ النُّعَاسَ أَمَنَةً مِّنْهُ وَيُنَزِّلُ عَلَيْكُم مِّنَ
السَّمَاءِ مَاءً لِّيُطَهِّرَكُم بِهِ وَيُذْهِبَ عَنكُمْ رِجْزَ الشَّيْطَانِ
وَلِيَرْبِطَ عَلَىٰ قُلُوبِكُمْ وَيُثَبِّتَ بِهِ الْأَقْدَامَ
Hausa
A lőkacin da (Allah) Yake rufe ku da gyangyaɗi, ɗőmin aminci daga gare Shi, kuma
Yană saukar da ruwa daga sama, a kanku, dőmin Ya tsarkake ku da shi, kuma Ya
tafiyar da ƙazantar Shaiɗan daga barinku, kuma dőmin Ya ɗaure a kan zukătanku,
kuma Ya tabbatar da ƙafăfu da shi.
|
Ayah 8:12 الأية
إِذْ يُوحِي رَبُّكَ إِلَى الْمَلَائِكَةِ أَنِّي مَعَكُمْ فَثَبِّتُوا الَّذِينَ
آمَنُوا ۚ سَأُلْقِي فِي قُلُوبِ الَّذِينَ كَفَرُوا الرُّعْبَ فَاضْرِبُوا فَوْقَ
الْأَعْنَاقِ وَاضْرِبُوا مِنْهُمْ كُلَّ بَنَانٍ
Hausa
A lőkacin da Ubangijinka Yake yin wahayi zuwa ga Mală'iku cẽwa: "Lalle ne Ni,
Ină tăre da ku, sai ku tabbatar da waɗanda suka yi ĩmăni: Ză Ni jẽfa tsőro a
cikin zukătan waɗanda suka kăfirta, sai ku yi dũka bisa ga wuyőyi kuma ku yi
dũka daga gare su ga dukkan yătsu .
|
Ayah 8:13 الأية
ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمْ شَاقُّوا اللَّهَ وَرَسُولَهُ ۚ وَمَن يُشَاقِقِ اللَّهَ
وَرَسُولَهُ فَإِنَّ اللَّهَ شَدِيدُ الْعِقَابِ
Hausa
Wancan ne, dőmin lalle ne sũ, sună săɓa wa Allah da ManzonSa. Kuma wanda ya săɓa
wa Allah da ManzonSa, to, lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne.
|
Ayah 8:14 الأية
ذَٰلِكُمْ فَذُوقُوهُ وَأَنَّ لِلْكَافِرِينَ عَذَابَ النَّارِ
Hausa
Wancan ne: "Ku ɗanɗane shi, kuma lalle ne akwai azăbar wuta ga kăfirai."
|
Ayah 8:15 الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِذَا لَقِيتُمُ الَّذِينَ كَفَرُوا زَحْفًا فَلَا
تُوَلُّوهُمُ الْأَدْبَارَ
Hausa
Yă kũ wacɗanda suka yiĩmăni! Idan kun haɗu da waɗanda suka kăfirta ga yăƙi, to,
kada ku jũya musu băyayyakinku.
|
Ayah 8:16 الأية
وَمَن يُوَلِّهِمْ يَوْمَئِذٍ دُبُرَهُ إِلَّا مُتَحَرِّفًا لِّقِتَالٍ أَوْ
مُتَحَيِّزًا إِلَىٰ فِئَةٍ فَقَدْ بَاءَ بِغَضَبٍ مِّنَ اللَّهِ وَمَأْوَاهُ
جَهَنَّمُ ۖ وَبِئْسَ الْمَصِيرُ
Hausa
Kuma duka wanda ya jũya musu băyansa a yinin nan, făce wanda ya karkata dőmin
kőɗayya, kő kuwa wanda ya jẽ dőmin haɗuwa da wata ƙungiya, to, lalle ne ya kőma
da fushi daga Allah, kuma matattararsa Jahannama, kuma tir da makőma ita!
|
Ayah 8:17 الأية
فَلَمْ تَقْتُلُوهُمْ وَلَٰكِنَّ اللَّهَ قَتَلَهُمْ ۚ وَمَا رَمَيْتَ إِذْ
رَمَيْتَ وَلَٰكِنَّ اللَّهَ رَمَىٰ ۚ وَلِيُبْلِيَ الْمُؤْمِنِينَ مِنْهُ بَلَاءً
حَسَنًا ۚ إِنَّ اللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٌ
Hausa
To, bă kũ ne kuka kashe su ba; kuma amma Allah ne Ya kashe su: kuma ba ka yi
jĩfa ba a lőkacin da ka yi jĩfa; kuma amma Allah ne Ya yi jĩfar. Kuma dőminYa
jarraba Musulmi da jarrabăwa mai kyau daga gare shi. Kuma Allah Mai ji ne,
Masani.
|
Ayah 8:18 الأية
ذَٰلِكُمْ وَأَنَّ اللَّهَ مُوهِنُ كَيْدِ الْكَافِرِينَ
Hausa
Wancan ne, kuma lalle ne, Allah Mai raunana kaidin kăfirai ne.
|
Ayah 8:19 الأية
إِن تَسْتَفْتِحُوا فَقَدْ جَاءَكُمُ الْفَتْحُ ۖ وَإِن تَنتَهُوا فَهُوَ خَيْرٌ
لَّكُمْ ۖ وَإِن تَعُودُوا نَعُدْ وَلَن تُغْنِيَ عَنكُمْ فِئَتُكُمْ شَيْئًا
وَلَوْ كَثُرَتْ وَأَنَّ اللَّهَ مَعَ الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
Idan kun yi alfănun cin nasara to lalle nasarar tă je muku, kuma idan kun hanu,
to Shi ne Mafi alhẽri a gare ku, kuma idan kun kőma ză Mu kőma, kuma jama'arku
bă ză ta wadătar muku da kőme ba, kő dă tă yi yawa. Kuma lalle ne cẽwa Allah
Yană tăre da mũminai!
|
Ayah 8:20 الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا أَطِيعُوا اللَّهَ وَرَسُولَهُ وَلَا تَوَلَّوْا
عَنْهُ وَأَنتُمْ تَسْمَعُونَ
Hausa
Yă ku waɗanda suka yi ĩmăni! Ku yi ɗă'a ga Allah da ManzonSa, kuma kada ku jũya
daga barinSa, alhăli kună ji.
|
Ayah 8:21 الأية
وَلَا تَكُونُوا كَالَّذِينَ قَالُوا سَمِعْنَا وَهُمْ لَا يَسْمَعُونَ
Hausa
Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka ce: "Mun ji, alhăli kuwa sũ bă su ji."
|
Ayah 8:22 الأية
إِنَّ شَرَّ الدَّوَابِّ عِندَ اللَّهِ الصُّمُّ الْبُكْمُ الَّذِينَ لَا
يَعْقِلُونَ
Hausa
Lalle ne, mafi sharrin dabbőbi a wurin Allah, sũ ne kurăme, bẽbăye, waɗanda bă,
su yin hankali.
|
Ayah 8:23 الأية
وَلَوْ عَلِمَ اللَّهُ فِيهِمْ خَيْرًا لَّأَسْمَعَهُمْ ۖ وَلَوْ أَسْمَعَهُمْ
لَتَوَلَّوا وَّهُم مُّعْرِضُونَ
Hausa
Dă Allah Yă san wani alhẽri a cikinsu, dă Yă jiyar da su, kuma kő da Yăjiyar da
su, haƙĩƙa,dă sun jũya , alhăli sũ, sună măsu hinjirẽwa.
|
Ayah 8:24 الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اسْتَجِيبُوا لِلَّهِ وَلِلرَّسُولِ إِذَا
دَعَاكُمْ لِمَا يُحْيِيكُمْ ۖ وَاعْلَمُوا أَنَّ اللَّهَ يَحُولُ بَيْنَ الْمَرْءِ
وَقَلْبِهِ وَأَنَّهُ إِلَيْهِ تُحْشَرُونَ
Hausa
Yă ku waɗanda suka yi ĩmăni! Ku karɓa wa Allah, kuma ku karɓa wa Manzo, idan Ya
kirăye ku zuwa ga abin da Yake răyar da ku; Kuma ku sani cẽwa Allah Yană
shămakacẽwa a tsakănin mutum da zũciyarsa, kuma lalle ne Shĩ, a zuwa gare Shi
ake tăra ku.
|
Ayah 8:25 الأية
وَاتَّقُوا فِتْنَةً لَّا تُصِيبَنَّ الَّذِينَ ظَلَمُوا مِنكُمْ خَاصَّةً ۖ
وَاعْلَمُوا أَنَّ اللَّهَ شَدِيدُ الْعِقَابِ
Hausa
Kuma ku ji tsőron fitina wadda bă ta sămun waɗanda suka yi zălunci daga gare ku
kẽɓe, kuma ku sani, lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne.
|
Ayah 8:26 الأية
وَاذْكُرُوا إِذْ أَنتُمْ قَلِيلٌ مُّسْتَضْعَفُونَ فِي الْأَرْضِ تَخَافُونَ أَن
يَتَخَطَّفَكُمُ النَّاسُ فَآوَاكُمْ وَأَيَّدَكُم بِنَصْرِهِ وَرَزَقَكُم مِّنَ
الطَّيِّبَاتِ لَعَلَّكُمْ تَشْكُرُونَ
Hausa
Ku tuna a lőkacin da kuke kaɗan, waɗanda ake raunanarwă a cikin ƙasa kună tsőron
mutăne su cafe ku, sai Ya tattara ku (a wurin natsuwa, Maɗina), kuma Ya ƙarfafă
ku da taimakonSa kuma Ya azurtă ku daga abũbuwa măsu dăɗi; Tsammăninku, kună
gődẽwa.
|
Ayah 8:27 الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا لَا تَخُونُوا اللَّهَ وَالرَّسُولَ وَتَخُونُوا
أَمَانَاتِكُمْ وَأَنتُمْ تَعْلَمُونَ
Hausa
Yă kũ waɗanda suka yi ĩmăni! Kada ku yaudari Allah da ManzonSa, kuma ku yaudari
amănőninku, alhăli kuwa kună sane.
|
Ayah 8:28 الأية
وَاعْلَمُوا أَنَّمَا أَمْوَالُكُمْ وَأَوْلَادُكُمْ فِتْنَةٌ وَأَنَّ اللَّهَ
عِندَهُ أَجْرٌ عَظِيمٌ
Hausa
Kuma ku sani cẽwa abin sani kawai, dũkiyőyinku da 'ya'yanku, wata fitina ce,
kuma lalle ne Allah, a wurinSa, akwai ijăra mai girma.
|
Ayah 8:29 الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِن تَتَّقُوا اللَّهَ يَجْعَل لَّكُمْ فُرْقَانًا
وَيُكَفِّرْ عَنكُمْ سَيِّئَاتِكُمْ وَيَغْفِرْ لَكُمْ ۗ وَاللَّهُ ذُو الْفَضْلِ
الْعَظِيمِ
Hausa
Ya kũ waɗanda suka yi ĩmăni! Idan kun bi Allah da taƙawa, zai sanyă muku
mararraba (da tsőro) kuma Ya kankare ƙanănan zunubanku daga barinku. Kuma Ya
găfartă muku. Kuma Allah ne Ma'abũcin falală Mai girma.
|
Ayah 8:30 الأية
وَإِذْ يَمْكُرُ بِكَ الَّذِينَ كَفَرُوا لِيُثْبِتُوكَ أَوْ يَقْتُلُوكَ أَوْ
يُخْرِجُوكَ ۚ وَيَمْكُرُونَ وَيَمْكُرُ اللَّهُ ۖ وَاللَّهُ خَيْرُ الْمَاكِرِينَ
Hausa
Kuma a lőkacin da waɗanda suka kăfirta sukẽ yin măkirci game da kai, dőmin su
tabbatar da kai, kő kuwa su kashe ka, kő kuwa su fitar da kai, sună măkirci kuma
Allah Yană mayar musa da măkirci kuma Allah ne Mafificin măsu măkirci.
|
Ayah 8:31 الأية
وَإِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِمْ آيَاتُنَا قَالُوا قَدْ سَمِعْنَا لَوْ نَشَاءُ
لَقُلْنَا مِثْلَ هَٰذَا ۙ إِنْ هَٰذَا إِلَّا أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ
Hausa
Kuma idan aka karanta, ăyőyinMu a kansu, sukan ce: "Lalle ne mun ji dă muna so,
haƙĩƙa, da mun faɗi irin wannan; wannan bai zama ba făce tătsunăyőyin mutănen
farko."
|
Ayah 8:32 الأية
وَإِذْ قَالُوا اللَّهُمَّ إِن كَانَ هَٰذَا هُوَ الْحَقَّ مِنْ عِندِكَ فَأَمْطِرْ
عَلَيْنَا حِجَارَةً مِّنَ السَّمَاءِ أَوِ ائْتِنَا بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
Hausa
A lőkacin da suka ce: "Yă Allah! Idan wannan ya kasancc shĩ ne gaskiya daga
wurinKa, sai Ka yi ruwan duwătsu, a kanmu, daga sama, kő kuwa Kaző mana da wata
azăba, mai raɗaɗi."
|
Ayah 8:33 الأية
وَمَا كَانَ اللَّهُ لِيُعَذِّبَهُمْ وَأَنتَ فِيهِمْ ۚ وَمَا كَانَ اللَّهُ
مُعَذِّبَهُمْ وَهُمْ يَسْتَغْفِرُونَ
Hausa
Kuma Allah bai kasance Yană yi musu azăba ba alhăli kuwa kai kană cikinsu, kuma
Allah bai kasance Mai yi musu azăba ba alhăli kuwa sună yin istigfări.
|
Ayah 8:34 الأية
وَمَا لَهُمْ أَلَّا يُعَذِّبَهُمُ اللَّهُ وَهُمْ يَصُدُّونَ عَنِ الْمَسْجِدِ
الْحَرَامِ وَمَا كَانُوا أَوْلِيَاءَهُ ۚ إِنْ أَوْلِيَاؤُهُ إِلَّا الْمُتَّقُونَ
وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ
Hausa
Kuma mẽne ne a gare su da Allah ba zai yi musu azăba ba, alhăli kuwa sũ, sună
kangẽwa daga Masallaci Mai alfarma kuma ba su kasance majiɓintanSa ba? Băbu
majiɓintanSa făce măsu taƙawa. Kuma mafi yawansu ba su sani ba.
|
Ayah 8:35 الأية
وَمَا كَانَ صَلَاتُهُمْ عِندَ الْبَيْتِ إِلَّا مُكَاءً وَتَصْدِيَةً ۚ فَذُوقُوا
الْعَذَابَ بِمَا كُنتُمْ تَكْفُرُونَ
Hausa
Kuma sallarsu a wurin ¦ăkin ba ta kasance ba făce shẽwa da yăyă; sai ku ɗanɗani
azăba sabőda abin da kuka kasance kună yi na kăfirci.
|
Ayah 8:36 الأية
إِنَّ الَّذِينَ كَفَرُوا يُنفِقُونَ أَمْوَالَهُمْ لِيَصُدُّوا عَن سَبِيلِ
اللَّهِ ۚ فَسَيُنفِقُونَهَا ثُمَّ تَكُونُ عَلَيْهِمْ حَسْرَةً ثُمَّ يُغْلَبُونَ
ۗ وَالَّذِينَ كَفَرُوا إِلَىٰ جَهَنَّمَ يُحْشَرُونَ
Hausa
Lalle ne waɗanda suka kăfirta, sună ciyar da dũkiyőyinsu, dőmin su kange daga
hanyar Allah; to, ză a su ciyar da ita, sa' an nan kuma ta kasance nadăma a
kansu, sa'an nan kuma a rinjăye su. Kuma waɗanda suka kăfirta zuwa ga Jahannama
ake tăra su;
|
Ayah 8:37 الأية
لِيَمِيزَ اللَّهُ الْخَبِيثَ مِنَ الطَّيِّبِ وَيَجْعَلَ الْخَبِيثَ بَعْضَهُ
عَلَىٰ بَعْضٍ فَيَرْكُمَهُ جَمِيعًا فَيَجْعَلَهُ فِي جَهَنَّمَ ۚ أُولَٰئِكَ هُمُ
الْخَاسِرُونَ
Hausa
Dőmin Allah Ya rarrabe mummũna daga mai kyau, kuma Ya sanya mummũnan, săshensa a
kan săshe, sa'an nan Ya shirga shi gabă daya, sa'an nan Ya sanyă shi a cikin
Jahannama. Waɗannan sũ ne măsu hasăra.
|
Ayah 8:38 الأية
قُل لِّلَّذِينَ كَفَرُوا إِن يَنتَهُوا يُغْفَرْ لَهُم مَّا قَدْ سَلَفَ وَإِن
يَعُودُوا فَقَدْ مَضَتْ سُنَّتُ الْأَوَّلِينَ
Hausa
Ka ce wa waɗanda suka kăfirta, idan sun hanu, ză a găfarta musu abin da ya riga
ya shige, kuma idan sun kőma, to, hanyar kăfiran farko, haƙĩƙa, ta shũɗe.
|
Ayah 8:39 الأية
وَقَاتِلُوهُمْ حَتَّىٰ لَا تَكُونَ فِتْنَةٌ وَيَكُونَ الدِّينُ كُلُّهُ لِلَّهِ ۚ
فَإِنِ انتَهَوْا فَإِنَّ اللَّهَ بِمَا يَعْمَلُونَ بَصِيرٌ
Hausa
Kuma ku yăƙe su har wata fitina bă ză ta kasance ba, kuma addini dukansa ya
kasance na Allah. To, idan sun hanu to lalle ne, Allah ia abin da kuke aikatăwa
Mai gani ne.
|
Ayah 8:40 الأية
وَإِن تَوَلَّوْا فَاعْلَمُوا أَنَّ اللَّهَ مَوْلَاكُمْ ۚ نِعْمَ الْمَوْلَىٰ
وَنِعْمَ النَّصِيرُ
Hausa
Kuma idan sun jũya, to, ku sani cẽwa lalle Allah ne Majiɓincinku: Mădalla da
Majiɓinci, kuma mădalla da Mai taimako, Shĩ.
|
Ayah 8:41 الأية
وَاعْلَمُوا أَنَّمَا غَنِمْتُم مِّن شَيْءٍ فَأَنَّ لِلَّهِ خُمُسَهُ
وَلِلرَّسُولِ وَلِذِي الْقُرْبَىٰ وَالْيَتَامَىٰ وَالْمَسَاكِينِ وَابْنِ
السَّبِيلِ إِن كُنتُمْ آمَنتُم بِاللَّهِ وَمَا أَنزَلْنَا عَلَىٰ عَبْدِنَا
يَوْمَ الْفُرْقَانِ يَوْمَ الْتَقَى الْجَمْعَانِ ۗ وَاللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيْءٍ
قَدِيرٌ
Hausa
Kuma ka sani, abin sani kawai, abin da kuka sămi ganĩma daga wani abu, to, lalle
ne Allah Yană da humusinsa kuma da Manzo, kuma da măsu zumunta, da marăyu da
miskĩnai da ɗan hanya, idan kun kasance kun yi ĩmăni da Allah da abin da Muka
saukar a kan băwanMu a Rănar Rarrabẽwa, a Rănar da jama'a biyu suka haɗu, kuma
Allah ne, a kan kőwane abu, Mai ĩkon yi.
|
Ayah 8:42 الأية
إِذْ أَنتُم بِالْعُدْوَةِ الدُّنْيَا وَهُم بِالْعُدْوَةِ الْقُصْوَىٰ وَالرَّكْبُ
أَسْفَلَ مِنكُمْ ۚ وَلَوْ تَوَاعَدتُّمْ لَاخْتَلَفْتُمْ فِي الْمِيعَادِ ۙ
وَلَٰكِن لِّيَقْضِيَ اللَّهُ أَمْرًا كَانَ مَفْعُولًا لِّيَهْلِكَ مَنْ هَلَكَ
عَن بَيِّنَةٍ وَيَحْيَىٰ مَنْ حَيَّ عَن بَيِّنَةٍ ۗ وَإِنَّ اللَّهَ لَسَمِيعٌ
عَلِيمٌ
Hausa
A lőkacin da kuke a găɓa ta kusa sũ kuma sună a găɓa tanẽsa, kuma ăyarin yana a
wuri mafi gangarăwa daga gare ku, kuma dă kun yi wa jũna wa'adi, dă kun săɓa ga
wa'adin; kuma amma dőmin Allah Ya hukunta abin da yake ya kasance abin aikatăwa.
Dőmin wanda yake halaka ya halaka daga shaida, kuma mai răyuwa ya răyu daga
shaida, kuma lalle Allah ne, haƙĩƙa, Mai ji Masani.
|
Ayah 8:43 الأية
إِذْ يُرِيكَهُمُ اللَّهُ فِي مَنَامِكَ قَلِيلًا ۖ وَلَوْ أَرَاكَهُمْ كَثِيرًا
لَّفَشِلْتُمْ وَلَتَنَازَعْتُمْ فِي الْأَمْرِ وَلَٰكِنَّ اللَّهَ سَلَّمَ ۗ
إِنَّهُ عَلِيمٌ بِذَاتِ الصُّدُورِ
Hausa
A lőkacin da Allah Yake nũna maka sũ sună kaɗan, a cikin barcinka, kuma dă Ya
nũna maka su sună da, yawa, lalle ne dă kun ji tsőro, kuma lalle ne dă kun yi
jăyayya a cikin al'amarin, kuma amma Allah Yă tsare ku: Lalle Shĩ ne Masani ga
abin da yake a cikin ƙirăza.
|
Ayah 8:44 الأية
وَإِذْ يُرِيكُمُوهُمْ إِذِ الْتَقَيْتُمْ فِي أَعْيُنِكُمْ قَلِيلًا
وَيُقَلِّلُكُمْ فِي أَعْيُنِهِمْ لِيَقْضِيَ اللَّهُ أَمْرًا كَانَ مَفْعُولًا ۗ
وَإِلَى اللَّهِ تُرْجَعُ الْأُمُورُ
Hausa
Kuma a lőkacin da Yake nũna muku su, a lőkacin da kuka haɗu, a cikin idanunku
sună kaɗan, kuma Ya ƙarantar da ku a cikin idanunsu dőmin Allah Ya hukunta wani
al'amari wanda ya kasance abin aikatăwa. Kuma zuwa ga Allah ake mayar da
al'umurra.
|
Ayah 8:45 الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِذَا لَقِيتُمْ فِئَةً فَاثْبُتُوا وَاذْكُرُوا
اللَّهَ كَثِيرًا لَّعَلَّكُمْ تُفْلِحُونَ
Hausa
Yă ku waɗanda suka yi ĩmăni! Idan kun haɗu da wata ƙungiyar yăƙi, to, ku
tabbata, kuma ku ambaci Allah da yawa, tsammăninku kună cin nasara.
|
Ayah 8:46 الأية
وَأَطِيعُوا اللَّهَ وَرَسُولَهُ وَلَا تَنَازَعُوا فَتَفْشَلُوا وَتَذْهَبَ
رِيحُكُمْ ۖ وَاصْبِرُوا ۚ إِنَّ اللَّهَ مَعَ الصَّابِرِينَ
Hausa
Kuma ku yi ɗă'a ga Allah da ManzonSa, kuma kada ku yi jăyayya har ku raunana
kuma iskarku ta tafi, kuma ku yi haƙuri. Lalle ne Allah Yană tăre da măsu
haƙuri.
|
Ayah 8:47 الأية
وَلَا تَكُونُوا كَالَّذِينَ خَرَجُوا مِن دِيَارِهِم بَطَرًا وَرِئَاءَ النَّاسِ
وَيَصُدُّونَ عَن سَبِيلِ اللَّهِ ۚ وَاللَّهُ بِمَا يَعْمَلُونَ مُحِيطٌ
Hausa
Kada ku kasance kamar waɗanda suka fita daga gidăjensu , sună măsu alfahari da
yin riya ga mutăne, kuma sună kangẽwa daga hanyar Allah. Kuma Allah ne ga abin
da suke aikatăwa Mai kẽwayẽwa.
|
Ayah 8:48 الأية
وَإِذْ زَيَّنَ لَهُمُ الشَّيْطَانُ أَعْمَالَهُمْ وَقَالَ لَا غَالِبَ لَكُمُ
الْيَوْمَ مِنَ النَّاسِ وَإِنِّي جَارٌ لَّكُمْ ۖ فَلَمَّا تَرَاءَتِ الْفِئَتَانِ
نَكَصَ عَلَىٰ عَقِبَيْهِ وَقَالَ إِنِّي بَرِيءٌ مِّنكُمْ إِنِّي أَرَىٰ مَا لَا
تَرَوْنَ إِنِّي أَخَافُ اللَّهَ ۚ وَاللَّهُ شَدِيدُ الْعِقَابِ
Hausa
Kuma a lőkacin da Shaiɗan ya ƙawăce musu ayyukansu, kuma ya ce: "Băbu marinjayi
a gareku a yau daga mutăne, kuma nĩ maƙwabci ne gare ku." To, a lőkacin da
ƙungiya biyu suka haɗu, ya kőma a kan digădigansa, kuma ya ce: "Lalle ne nĩ
barrantacce ne daga gare ku! Nĩ ină ganin abin da bă ku gani; ni ină tsőron
Allah: Kuma Allah Mai tsananin uƙũba ne."
|
Ayah 8:49 الأية
إِذْ يَقُولُ الْمُنَافِقُونَ وَالَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٌ غَرَّ هَٰؤُلَاءِ
دِينُهُمْ ۗ وَمَن يَتَوَكَّلْ عَلَى اللَّهِ فَإِنَّ اللَّهَ عَزِيزٌ حَكِيمٌ
Hausa
A lőkacin da munăfukai da waɗanda suke akwai cũtă a cikin zukătansu, suke cẽwa:
"Addĩnin waɗannan yă rũɗe su" Kuma wanda ya dőgara ga Allah, to, lalle ne Allah
Mabuwăyi ne, Mai hikima.
|
Ayah 8:50 الأية
وَلَوْ تَرَىٰ إِذْ يَتَوَفَّى الَّذِينَ كَفَرُوا ۙ الْمَلَائِكَةُ يَضْرِبُونَ
وُجُوهَهُمْ وَأَدْبَارَهُمْ وَذُوقُوا عَذَابَ الْحَرِيقِ
Hausa
Kuma dă kă gani, a lőkacin da Mală'iku suke karɓar răyukan waɗanda suka kăfirta,
sună dukar fuskőkinsu da ɗuwăwunsu, kuma suna cẽwa: "Ku ɗanɗani azăbar Gőbara."
|
Ayah 8:51 الأية
ذَٰلِكَ بِمَا قَدَّمَتْ أَيْدِيكُمْ وَأَنَّ اللَّهَ لَيْسَ بِظَلَّامٍ
لِّلْعَبِيدِ
Hausa
"Wancan sabőda abin da hannăyenku suka gabătar ne. Kuma lalle ne, Allah bai zama
Mai zălunci ba ga, băyinSa."
|
Ayah 8:52 الأية
كَدَأْبِ آلِ فِرْعَوْنَ ۙ وَالَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ ۚ كَفَرُوا بِآيَاتِ اللَّهِ
فَأَخَذَهُمُ اللَّهُ بِذُنُوبِهِمْ ۗ إِنَّ اللَّهَ قَوِيٌّ شَدِيدُ الْعِقَابِ
Hausa
"Kamar al'ădar mutănen Fir'auna da waɗanda suke gabăninsu, sun kăfirta da ăyőyin
Allah, sai Allah Ya kăma su da zunubansu. Lalle Allah ne Mai ƙarfi, Mai tsananin
uƙũba.
|
Ayah 8:53 الأية
ذَٰلِكَ بِأَنَّ اللَّهَ لَمْ يَكُ مُغَيِّرًا نِّعْمَةً أَنْعَمَهَا عَلَىٰ قَوْمٍ
حَتَّىٰ يُغَيِّرُوا مَا بِأَنفُسِهِمْ ۙ وَأَنَّ اللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٌ
Hausa
"Wancan ne, dőmin lalle ne, Allah bai kasance Mai canza wata ni'ima wadda ya
ni'imtar da ita a kan wasu mutăne ba făce sun săke abin da yake ga răyukansu,
kuma dőmin lalle Allah ne Mai jĩ,Masani."
|
Ayah 8:54 الأية
كَدَأْبِ آلِ فِرْعَوْنَ ۙ وَالَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ ۚ كَذَّبُوا بِآيَاتِ
رَبِّهِمْ فَأَهْلَكْنَاهُم بِذُنُوبِهِمْ وَأَغْرَقْنَا آلَ فِرْعَوْنَ ۚ وَكُلٌّ
كَانُوا ظَالِمِينَ
Hausa
Kamar al'adar mutănen Fir'auna da waɗanda suke a gabăninsu, sun ƙaryata game da
ăyőyin Ubangijinsu, sai Muka halaka su, sabőda zunubansu, kuma Muka nutsar da
mutănen Fir'auna. Kuma dukansu sun kasance ne măsu zălunci.
|
Ayah 8:55 الأية
إِنَّ شَرَّ الدَّوَابِّ عِندَ اللَّهِ الَّذِينَ كَفَرُوا فَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
Hausa
Lalle mafi sharrin dabbőbi a wurin Allah, sũ ne waɗanda suka kăfirta, sa'an nan
bă ză su yi ĩmăni ba.
|
Ayah 8:56 الأية
الَّذِينَ عَاهَدتَّ مِنْهُمْ ثُمَّ يَنقُضُونَ عَهْدَهُمْ فِي كُلِّ مَرَّةٍ
وَهُمْ لَا يَتَّقُونَ
Hausa
Waɗanda ka yi ƙullin alkawari da su, daga gare su, sa'an nan kuma sună
warwarewar alkawarinsu a kőwane lőkaci kuma sũ, bă su yin taƙawa.
|
Ayah 8:57 الأية
فَإِمَّا تَثْقَفَنَّهُمْ فِي الْحَرْبِ فَشَرِّدْ بِهِم مَّنْ خَلْفَهُمْ
لَعَلَّهُمْ يَذَّكَّرُونَ
Hausa
To, in dai ka kăma su a cikin yăƙi, sai ka kőre waɗanda suke a băyansu, game da
su, tsammăninsu, ză su dinga tunăwa.
|
Ayah 8:58 الأية
وَإِمَّا تَخَافَنَّ مِن قَوْمٍ خِيَانَةً فَانبِذْ إِلَيْهِمْ عَلَىٰ سَوَاءٍ ۚ
إِنَّ اللَّهَ لَا يُحِبُّ الْخَائِنِينَ
Hausa
Kuma in ka ji tsőron wata yaudara daga wasu mutăne, to, ka jẽfar da alkawarin,
zuwa gare su, a kan daidaita: Lalle ne Allah, bă Ya son mayaudara.
|
Ayah 8:59 الأية
وَلَا يَحْسَبَنَّ الَّذِينَ كَفَرُوا سَبَقُوا ۚ إِنَّهُمْ لَا يُعْجِزُونَ
Hausa
Kuma waɗanda suka kăfirta kada su yi zaton sun tsẽre: Lalle ne sũ, bă ză su
găgara ba.
|
Ayah 8:60 الأية
وَأَعِدُّوا لَهُم مَّا اسْتَطَعْتُم مِّن قُوَّةٍ وَمِن رِّبَاطِ الْخَيْلِ
تُرْهِبُونَ بِهِ عَدُوَّ اللَّهِ وَعَدُوَّكُمْ وَآخَرِينَ مِن دُونِهِمْ لَا
تَعْلَمُونَهُمُ اللَّهُ يَعْلَمُهُمْ ۚ وَمَا تُنفِقُوا مِن شَيْءٍ فِي سَبِيلِ
اللَّهِ يُوَفَّ إِلَيْكُمْ وَأَنتُمْ لَا تُظْلَمُونَ
Hausa
Kuma ku yi tattali, dőminsu, abin da kuka sămi ĩkon yi na wani ƙarfi, kuma da
ajiye dawaki, kună tsoratarwa, game da shi, ga maƙiyin Allah kuma maƙiyinku da
wasu, baicin su, ba ku san su ba, Allah ne Yake sanin su, kuma abin da kuka
ciyar daga wani abu a cikin hanyar Allah, ză a cika muku sakamakonsa, kuma kũ ba
a zăluntar ku.
|
Ayah 8:61 الأية
وَإِن جَنَحُوا لِلسَّلْمِ فَاجْنَحْ لَهَا وَتَوَكَّلْ عَلَى اللَّهِ ۚ إِنَّهُ
هُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُ
Hausa
Kuma idan sun karkata zuwa ga zaman lăfiya, to, ka karkata zuwa gare shi, kuma
ka dőgara ga Allah: Lalle ne Shĩ, Mai ji ne Masani.
|
Ayah 8:62 الأية
وَإِن يُرِيدُوا أَن يَخْدَعُوكَ فَإِنَّ حَسْبَكَ اللَّهُ ۚ هُوَ الَّذِي
أَيَّدَكَ بِنَصْرِهِ وَبِالْمُؤْمِنِينَ
Hausa
Kuma idan sun yi nufin su yaudare ka, to, lalle ma'ishinka Allah ne, Shĩ ne
wanda Ya ƙarfafa ka da taimakonSa, kuma da mũminai.
|
Ayah 8:63 الأية
وَأَلَّفَ بَيْنَ قُلُوبِهِمْ ۚ لَوْ أَنفَقْتَ مَا فِي الْأَرْضِ جَمِيعًا مَّا
أَلَّفْتَ بَيْنَ قُلُوبِهِمْ وَلَٰكِنَّ اللَّهَ أَلَّفَ بَيْنَهُمْ ۚ إِنَّهُ
عَزِيزٌ حَكِيمٌ
Hausa
Kuma Ya sanya sőyayya a tsakănin zukătansu. Dă kă ciyar da abin da yake cikin
ƙasa, gabă ɗaya, dă ba ka sanya sőyayya a tsakănin zukătansu ba, kuma amma Allah
Yă sanya sőyayya a tsakăninsu. Lalle Shi ne Mabuwăyi, Mai hikima.
|
Ayah 8:64 الأية
يَا أَيُّهَا النَّبِيُّ حَسْبُكَ اللَّهُ وَمَنِ اتَّبَعَكَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
Ya kai Annabi! Ma'ishinka Allah ne, kai da wanda ya biye maka daga mũminai.
|
Ayah 8:65 الأية
يَا أَيُّهَا النَّبِيُّ حَرِّضِ الْمُؤْمِنِينَ عَلَى الْقِتَالِ ۚ إِن يَكُن
مِّنكُمْ عِشْرُونَ صَابِرُونَ يَغْلِبُوا مِائَتَيْنِ ۚ وَإِن يَكُن مِّنكُم
مِّائَةٌ يَغْلِبُوا أَلْفًا مِّنَ الَّذِينَ كَفَرُوا بِأَنَّهُمْ قَوْمٌ لَّا
يَفْقَهُونَ
Hausa
Ya kai Annabi! Ka kwaɗaitar da mũminai a kan yăƙi. Idan mutum ashirin măsu
haƙuri sun kasance daga gare ku, ză su rinjăyi mẽtan kuma idan ɗari suka kasance
daga gare ku, ză su rinjăyi dubu daga waɗanda suka kăfirta, dőmin sũ, mutăne ne
bă su fahimta.
|
Ayah 8:66 الأية
الْآنَ خَفَّفَ اللَّهُ عَنكُمْ وَعَلِمَ أَنَّ فِيكُمْ ضَعْفًا ۚ فَإِن يَكُن
مِّنكُم مِّائَةٌ صَابِرَةٌ يَغْلِبُوا مِائَتَيْنِ ۚ وَإِن يَكُن مِّنكُمْ أَلْفٌ
يَغْلِبُوا أَلْفَيْنِ بِإِذْنِ اللَّهِ ۗ وَاللَّهُ مَعَ الصَّابِرِينَ
Hausa
A yanzu Allah Yă sauƙaƙe daga gare ku, kuma Yă sani cẽwa lalle ne akwai măsu
rauni a cikinku. To, idan mutum ɗari, măsu haƙuri, suka kasance daga gare ku, ză
su rinjăyi mẽtan, kuma idan dubu suka kasance daga gare ku, ză su rinjăyi dubu
biyu, da iznin Allah. Kuma Allah Yană tăre da măsu haƙuri.
|
Ayah 8:67 الأية
مَا كَانَ لِنَبِيٍّ أَن يَكُونَ لَهُ أَسْرَىٰ حَتَّىٰ يُثْخِنَ فِي الْأَرْضِ ۚ
تُرِيدُونَ عَرَضَ الدُّنْيَا وَاللَّهُ يُرِيدُ الْآخِرَةَ ۗ وَاللَّهُ عَزِيزٌ
حَكِيمٌ
Hausa
Bă ya kasancewa ga wani annabi, kămammu su kasance a gare shi sai (băyan) yă
zubar da jinainai a cikin ƙasa. Kună nufin sifar dũniya kuma Allah Yanănufin
Lăhira. Kuma Allah ne Mabuwăyi, Mai hikima.
|
Ayah 8:68 الأية
لَّوْلَا كِتَابٌ مِّنَ اللَّهِ سَبَقَ لَمَسَّكُمْ فِيمَا أَخَذْتُمْ عَذَابٌ
عَظِيمٌ
Hausa
Bă dőmin wani Littăfi daga Allah ba, wanda ya gabăta , dă azăba mai girma daga
Allah tă shăfe ku a cikin abin da kuka kăma.
|
Ayah 8:69 الأية
فَكُلُوا مِمَّا غَنِمْتُمْ حَلَالًا طَيِّبًا ۚ وَاتَّقُوا اللَّهَ ۚ إِنَّ
اللَّهَ غَفُورٌ رَّحِيمٌ
Hausa
Sabőda haka, ku ci daga abin da kuka sămu ganĩma, Yană halal mai kyau. Kuma ku
bi Allah da taƙawa. Lalle Allah ne Mai găfara, Mai jin ƙai.
|
Ayah 8:70 الأية
يَا أَيُّهَا النَّبِيُّ قُل لِّمَن فِي أَيْدِيكُم مِّنَ الْأَسْرَىٰ إِن يَعْلَمِ
اللَّهُ فِي قُلُوبِكُمْ خَيْرًا يُؤْتِكُمْ خَيْرًا مِّمَّا أُخِذَ مِنكُمْ
وَيَغْفِرْ لَكُمْ ۗ وَاللَّهُ غَفُورٌ رَّحِيمٌ
Hausa
Ya kai Annabi! Ka ce wa wanda yake a cikin hannăyenku daga kămammu: "Idan Allah
Ya san akwai wani alhẽri a cikin zukătanku, zai kawo muku mafi alhẽri daga abin
da aka karɓa daga gare ku, kuma Ya yi muku găfara. Kuma Allah ne Mai găfara, Mai
jin ƙai."
|
Ayah 8:71 الأية
وَإِن يُرِيدُوا خِيَانَتَكَ فَقَدْ خَانُوا اللَّهَ مِن قَبْلُ فَأَمْكَنَ
مِنْهُمْ ۗ وَاللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٌ
Hausa
Kuma idan sun yi nufin yaudararka, to, haƙĩƙa, sun yaudari Allahdaga gabăni sai
Ya băyar da dămă daga gare su: Kuma Allah ne Masani, Mai hikima.
|
Ayah 8:72 الأية
إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَهَاجَرُوا وَجَاهَدُوا بِأَمْوَالِهِمْ وَأَنفُسِهِمْ
فِي سَبِيلِ اللَّهِ وَالَّذِينَ آوَوا وَّنَصَرُوا أُولَٰئِكَ بَعْضُهُمْ
أَوْلِيَاءُ بَعْضٍ ۚ وَالَّذِينَ آمَنُوا وَلَمْ يُهَاجِرُوا مَا لَكُم مِّن
وَلَايَتِهِم مِّن شَيْءٍ حَتَّىٰ يُهَاجِرُوا ۚ وَإِنِ اسْتَنصَرُوكُمْ فِي
الدِّينِ فَعَلَيْكُمُ النَّصْرُ إِلَّا عَلَىٰ قَوْمٍ بَيْنَكُمْ وَبَيْنَهُم
مِّيثَاقٌ ۗ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ بَصِيرٌ
Hausa
Lalle ne waɗanda suka yi ĩmăni, kuma suka yi hijira, kuma suka yi jihădi da
dũkiyőyinsuda răyukansu, a cikin hanyar Allah, da waɗanda suka băyar da masauki,
kuma suka yi taimako. Waɗancan, săshensu waliyyai ne ga săshe. Kuma waɗanda suka
yi ĩmăni kuma ba su yi hijira ba, bă ku da wani abu daga waliccinsu, sai sun yi
hijira. Kuma idan suka nẽme ku taimako a cikin addini, to taimako yă wajaba a
kanku, făce a kan mutăne waɗanda a tsakăninku da tsakăninsu akwai wani alkwari.
Kuma Allah ne, ga abin da kuke aikatăwa, Mai gani.
|
Ayah 8:73 الأية
وَالَّذِينَ كَفَرُوا بَعْضُهُمْ أَوْلِيَاءُ بَعْضٍ ۚ إِلَّا تَفْعَلُوهُ تَكُن
فِتْنَةٌ فِي الْأَرْضِ وَفَسَادٌ كَبِيرٌ
Hausa
Kuma waɗanda suka kăfirta săshensu ne waliyyan săshe, idan ba ku aikata shi ba,
wata fitina ză ta kasance a cikin ƙasa, da fasădi babba.
|
Ayah 8:74 الأية
وَالَّذِينَ آمَنُوا وَهَاجَرُوا وَجَاهَدُوا فِي سَبِيلِ اللَّهِ وَالَّذِينَ
آوَوا وَّنَصَرُوا أُولَٰئِكَ هُمُ الْمُؤْمِنُونَ حَقًّا ۚ لَّهُم مَّغْفِرَةٌ
وَرِزْقٌ كَرِيمٌ
Hausa
Kuma waɗanda suka yi ĩmăni kuma suka yi hijira, kuma suka yi Jihădi, a cikin
hanyar Allah, kuma da waɗanda suka băyar da masauki, kuma suka yi tamiako,
waɗannan sũ ne mũminai da gaskiya, sunăda găfara da wani abinci na karimci.
|
Ayah 8:75 الأية
وَالَّذِينَ آمَنُوا مِن بَعْدُ وَهَاجَرُوا وَجَاهَدُوا مَعَكُمْ فَأُولَٰئِكَ
مِنكُمْ ۚ وَأُولُو الْأَرْحَامِ بَعْضُهُمْ أَوْلَىٰ بِبَعْضٍ فِي كِتَابِ اللَّهِ
ۗ إِنَّ اللَّهَ بِكُلِّ شَيْءٍ عَلِيمٌ
Hausa
Kuma waɗanda suka yi ĩmăni daga băya, kuma suka yi hijira kuma suka yi jihădi
tăre da ku, to, waɗannan daga gare ku suke. Kuma ma'abũta zumunta, săshensu ne
waliyyan săshe a cikin Littăfin Allah. Lalle Allah ne ga dukkan kőme Masani.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|