« Prev

81. Surah At-Takwîr سورة التكوير

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
إِذَا الشَّمْسُ كُوِّرَتْ
Hausa
 
Idan rãna aka shafe haskenta

Ayah   81:2   الأية
وَإِذَا النُّجُومُ انكَدَرَتْ
Hausa
 
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

Ayah   81:3   الأية
وَإِذَا الْجِبَالُ سُيِّرَتْ
Hausa
 
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

Ayah   81:4   الأية
وَإِذَا الْعِشَارُ عُطِّلَتْ
Hausa
 
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

Ayah   81:5   الأية
وَإِذَا الْوُحُوشُ حُشِرَتْ
Hausa
 
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

Ayah   81:6   الأية
وَإِذَا الْبِحَارُ سُجِّرَتْ
Hausa
 
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

Ayah   81:7   الأية
وَإِذَا النُّفُوسُ زُوِّجَتْ
Hausa
 
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

Ayah   81:8   الأية
وَإِذَا الْمَوْءُودَةُ سُئِلَتْ
Hausa
 
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

Ayah   81:9   الأية
بِأَيِّ ذَنبٍ قُتِلَتْ
Hausa
 
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

Ayah   81:10   الأية
وَإِذَا الصُّحُفُ نُشِرَتْ
Hausa
 
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

Ayah   81:11   الأية
وَإِذَا السَّمَاءُ كُشِطَتْ
Hausa
 
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

Ayah   81:12   الأية
وَإِذَا الْجَحِيمُ سُعِّرَتْ
Hausa
 
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

Ayah   81:13   الأية
وَإِذَا الْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ
Hausa
 
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

Ayah   81:14   الأية
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا أَحْضَرَتْ
Hausa
 
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

Ayah   81:15   الأية
فَلَا أُقْسِمُ بِالْخُنَّسِ
Hausa
 
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

Ayah   81:16   الأية
الْجَوَارِ الْكُنَّسِ
Hausa
 
Mãsu gudu suna ɓũya.

Ayah   81:17   الأية
وَاللَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ
Hausa
 
Da dare idan ya bãyar da bãya.

Ayah   81:18   الأية
وَالصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ
Hausa
 
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

Ayah   81:19   الأية
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
Hausa
 
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

Ayah   81:20   الأية
ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي الْعَرْشِ مَكِينٍ
Hausa
 
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

Ayah   81:21   الأية
مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ
Hausa
 
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

Ayah   81:22   الأية
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ
Hausa
 
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

Ayah   81:23   الأية
وَلَقَدْ رَآهُ بِالْأُفُقِ الْمُبِينِ
Hausa
 
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

Ayah   81:24   الأية
وَمَا هُوَ عَلَى الْغَيْبِ بِضَنِينٍ
Hausa
 
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

Ayah   81:25   الأية
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَانٍ رَّجِيمٍ
Hausa
 
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

Ayah   81:26   الأية
فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ
Hausa
 
Shin, a inã zã ku tafi?

Ayah   81:27   الأية
إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَ
Hausa
 
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

Ayah   81:28   الأية
لِمَن شَاءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ
Hausa
 
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

Ayah   81:29   الأية
وَمَا تَشَاءُونَ إِلَّا أَن يَشَاءَ اللَّهُ رَبُّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us