« Prev
81. Surah At-Takwîr سورة التكوير
Next »
First Ayah 1 الأية الأوليبِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
إِذَا الشَّمْسُ كُوِّرَتْ
Hausa
Idan rãna aka shafe haskenta
|
Ayah 81:2 الأية
وَإِذَا النُّجُومُ انكَدَرَتْ
Hausa
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
|
Ayah 81:3 الأية
وَإِذَا الْجِبَالُ سُيِّرَتْ
Hausa
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
|
Ayah 81:4 الأية
وَإِذَا الْعِشَارُ عُطِّلَتْ
Hausa
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
|
Ayah 81:5 الأية
وَإِذَا الْوُحُوشُ حُشِرَتْ
Hausa
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
|
Ayah 81:6 الأية
وَإِذَا الْبِحَارُ سُجِّرَتْ
Hausa
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
|
Ayah 81:7 الأية
وَإِذَا النُّفُوسُ زُوِّجَتْ
Hausa
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
|
Ayah 81:8 الأية
وَإِذَا الْمَوْءُودَةُ سُئِلَتْ
Hausa
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
|
Ayah 81:9 الأية
بِأَيِّ ذَنبٍ قُتِلَتْ
Hausa
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
|
Ayah 81:10 الأية
وَإِذَا الصُّحُفُ نُشِرَتْ
Hausa
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
|
Ayah 81:11 الأية
وَإِذَا السَّمَاءُ كُشِطَتْ
Hausa
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
|
Ayah 81:12 الأية
وَإِذَا الْجَحِيمُ سُعِّرَتْ
Hausa
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
|
Ayah 81:13 الأية
وَإِذَا الْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ
Hausa
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
|
Ayah 81:14 الأية
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا أَحْضَرَتْ
Hausa
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
|
Ayah 81:15 الأية
فَلَا أُقْسِمُ بِالْخُنَّسِ
Hausa
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
|
Ayah 81:16 الأية
الْجَوَارِ الْكُنَّسِ
Hausa
Mãsu gudu suna ɓũya.
|
Ayah 81:17 الأية
وَاللَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ
Hausa
Da dare idan ya bãyar da bãya.
|
Ayah 81:18 الأية
وَالصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ
Hausa
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
|
Ayah 81:19 الأية
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
Hausa
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga
Allah.
|
Ayah 81:20 الأية
ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي الْعَرْشِ مَكِينٍ
Hausa
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
|
Ayah 81:21 الأية
مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ
Hausa
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
|
Ayah 81:22 الأية
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ
Hausa
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
|
Ayah 81:23 الأية
وَلَقَدْ رَآهُ بِالْأُفُقِ الْمُبِينِ
Hausa
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
|
Ayah 81:24 الأية
وَمَا هُوَ عَلَى الْغَيْبِ بِضَنِينٍ
Hausa
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
|
Ayah 81:25 الأية
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَانٍ رَّجِيمٍ
Hausa
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
|
Ayah 81:26 الأية
فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ
Hausa
Shin, a inã zã ku tafi?
|
Ayah 81:27 الأية
إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَ
Hausa
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
|
Ayah 81:28 الأية
لِمَن شَاءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ
Hausa
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
|
Ayah 81:29 الأية
وَمَا تَشَاءُونَ إِلَّا أَن يَشَاءَ اللَّهُ رَبُّ الْعَالَمِينَ
Hausa
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|
|