Prev  

55. Surah Ar-Rahmân سورة الرحمن

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الرَّحْمَٰنُ
Arrahman

Hausa
 
(Allah) Mai rahama.

Ayah  55:2  الأية
عَلَّمَ الْقُرْآنَ
AAallama alqur-an

Hausa
 
Yã sanar da Alƙur'ani.

Ayah  55:3  الأية
خَلَقَ الْإِنسَانَ
Khalaqa al-insan

Hausa
 
Yã halitta mutum.

Ayah  55:4  الأية
عَلَّمَهُ الْبَيَانَ
AAallamahu albayan

Hausa
 
Yã sanar da shi bayãni (magana).

Ayah  55:5  الأية
الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ بِحُسْبَانٍ
Ashshamsu walqamaru bihusban

Hausa
 
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.

Ayah  55:6  الأية
وَالنَّجْمُ وَالشَّجَرُ يَسْجُدَانِ
Wannajmu washshajaru yasjudan

Hausa
 
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.

Ayah  55:7  الأية
وَالسَّمَاءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ الْمِيزَانَ
Wassamaa rafaAAahawawadaAAa almeezan

Hausa
 
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.

Ayah  55:8  الأية
أَلَّا تَطْغَوْا فِي الْمِيزَانِ
Alla tatghaw fee almeezan

Hausa
 
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.

Ayah  55:9  الأية
وَأَقِيمُوا الْوَزْنَ بِالْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا الْمِيزَانَ
Waaqeemoo alwazna bilqisti walatukhsiroo almeezan

Hausa
 
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.

Ayah  55:10  الأية
وَالْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ
Wal-arda wadaAAahalil-anam

Hausa
 
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.

Ayah  55:11  الأية
فِيهَا فَاكِهَةٌ وَالنَّخْلُ ذَاتُ الْأَكْمَامِ
Feeha fakihatun wannakhluthatu al-akmam

Hausa
 
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.

Ayah  55:12  الأية
وَالْحَبُّ ذُو الْعَصْفِ وَالرَّيْحَانُ
Walhabbu thoo alAAasfiwarrayhan

Hausa
 
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.

Ayah  55:13  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:14  الأية
خَلَقَ الْإِنسَانَ مِن صَلْصَالٍ كَالْفَخَّارِ
Khalaqa al-insana min salsalinkalfakhkhar

Hausa
 
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.

Ayah  55:15  الأية
وَخَلَقَ الْجَانَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍ
Wakhalaqa aljanna min marijinmin nar

Hausa
 
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.

Ayah  55:16  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:17  الأية
رَبُّ الْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ الْمَغْرِبَيْنِ
Rabbu almashriqayni warabbu almaghribayn

Hausa
 
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.

Ayah  55:18  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:19  الأية
مَرَجَ الْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ
Maraja albahrayni yaltaqiyan

Hausa
 
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.

Ayah  55:20  الأية
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لَّا يَبْغِيَانِ
Baynahuma barzakhun la yabghiyan

Hausa
 
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.

Ayah  55:21  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:22  الأية
يَخْرُجُ مِنْهُمَا اللُّؤْلُؤُ وَالْمَرْجَانُ
Yakhruju minhuma allu/luo walmarjan

Hausa
 
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.

Ayah  55:23  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththibani

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:24  الأية
وَلَهُ الْجَوَارِ الْمُنشَآتُ فِي الْبَحْرِ كَالْأَعْلَامِ
Walahu aljawari almunshaatufee albahri kal-aAAlam

Hausa
 
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.

Ayah  55:25  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:26  الأية
كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍ
Kullu man AAalayha fan

Hausa
 
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.

Ayah  55:27  الأية
وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ
Wayabqa wajhu rabbika thooaljalali wal-ikram

Hausa
 
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.

Ayah  55:28  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:29  الأية
يَسْأَلُهُ مَن فِي السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِي شَأْنٍ
Yas-aluhu man fee assamawatiwal-ardi kulla yawmin huwa fee sha/n

Hausa
 
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.

Ayah  55:30  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:31  الأية
سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ الثَّقَلَانِ
Sanafrughu lakum ayyuha aththaqalan

Hausa
 
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!

Ayah  55:32  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:33  الأية
يَا مَعْشَرَ الْجِنِّ وَالْإِنسِ إِنِ اسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا مِنْ أَقْطَارِ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ فَانفُذُوا ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَانٍ
Ya maAAshara aljinni wal-insiini istataAAtum an tanfuthoo min aqtari assamawatiwal-ardi fanfuthoo la tanfuthoonailla bisultan

Hausa
 
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.

Ayah  55:34  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:35  الأية
يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلَا تَنتَصِرَانِ
Yursalu AAalaykuma shuwathunmin narin wanuhasun fala tantasiran

Hausa
 
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?

Ayah  55:36  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:37  الأية
فَإِذَا انشَقَّتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَالدِّهَانِ
Fa-itha inshaqqati assamaofakanat wardatan kaddihan

Hausa
 
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.

Ayah  55:38  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:39  الأية
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُسْأَلُ عَن ذَنبِهِ إِنسٌ وَلَا جَانٌّ
Fayawma-ithin la yus-alu AAan thanbihiinsun wala jan

Hausa
 
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.

Ayah  55:40  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:41  الأية
يُعْرَفُ الْمُجْرِمُونَ بِسِيمَاهُمْ فَيُؤْخَذُ بِالنَّوَاصِي وَالْأَقْدَامِ
YuAArafu almujrimoona biseemahumfayu/khathu binnawasee wal-aqdam

Hausa
 
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.

Ayah  55:42  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:43  الأية
هَٰذِهِ جَهَنَّمُ الَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا الْمُجْرِمُونَ
Hathihi jahannamu allatee yukaththibubiha almujrimoon

Hausa
 
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.

Ayah  55:44  الأية
يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ آنٍ
Yatoofoona baynaha wabayna hameeminan

Hausa
 
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.

Ayah  55:45  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:46  الأية
وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ جَنَّتَانِ
Waliman khafa maqama rabbihijannatan

Hausa
 
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.

Ayah  55:47  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:48  الأية
ذَوَاتَا أَفْنَانٍ
Thawata afnan

Hausa
 
Mãsu rassan itãce.

Ayah  55:49  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:50  الأية
فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ
Feehima AAaynani tajriyan

Hausa
 
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.

Ayah  55:51  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:52  الأية
فِيهِمَا مِن كُلِّ فَاكِهَةٍ زَوْجَانِ
Feehima min kulli fakihatinzawjan

Hausa
 
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.

Ayah  55:53  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:54  الأية
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ فُرُشٍ بَطَائِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍ ۚ وَجَنَى الْجَنَّتَيْنِ دَانٍ
Muttaki-eena AAala furushin bata-inuhamin istabraqin wajana aljannatayni dan

Hausa
 
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.

Ayah  55:55  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:56  الأية
فِيهِنَّ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ
Feehinna qasiratu attarfilam yatmithhunna insun qablahum wala jan

Hausa
 
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.

Ayah  55:57  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:58  الأية
كَأَنَّهُنَّ الْيَاقُوتُ وَالْمَرْجَانُ
Kaannahunna alyaqootu walmarjan

Hausa
 
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.

Ayah  55:59  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:60  الأية
هَلْ جَزَاءُ الْإِحْسَانِ إِلَّا الْإِحْسَانُ
Hal jazao al-ihsani illaal-ihsan

Hausa
 
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.

Ayah  55:61  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:62  الأية
وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ
Wamin doonihima jannatan

Hausa
 
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.

Ayah  55:63  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:64  الأية
مُدْهَامَّتَانِ
Mudhammatan

Hausa
 
Mãsu duhun inuwa.

Ayah  55:65  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:66  الأية
فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ
Feehima AAaynani naddakhatan

Hausa
 
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.

Ayah  55:67  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:68  الأية
فِيهِمَا فَاكِهَةٌ وَنَخْلٌ وَرُمَّانٌ
Feehima fakihatun wanakhlunwarumman

Hausa
 
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.

Ayah  55:69  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:70  الأية
فِيهِنَّ خَيْرَاتٌ حِسَانٌ
Feehinna khayratun hisan

Hausa
 
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.

Ayah  55:71  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:72  الأية
حُورٌ مَّقْصُورَاتٌ فِي الْخِيَامِ
Hoorun maqsooratun feealkhiyam

Hausa
 
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.

Ayah  55:73  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:74  الأية
لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ
Lam yatmithhunna insun qablahum walajan

Hausa
 
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.

Ayah  55:75  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:76  الأية
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍ وَعَبْقَرِيٍّ حِسَانٍ
Muttaki-eena AAala rafrafin khudrinwaAAabqariyyin hisan

Hausa
 
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.

Ayah  55:77  الأية
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
Fabi-ayyi ala-i rabbikumatukaththiban

Hausa
 
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Ayah  55:78  الأية
تَبَارَكَ اسْمُ رَبِّكَ ذِي الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ
Tabaraka ismu rabbika theealjalali wal-ikram

Hausa
 
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us