1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
يَا أَيُّهَا النَّبِيُّ لِمَ تُحَرِّمُ مَا أَحَلَّ اللهُ لَكَ ۖ تَبْتَغِي
مَرْضَاتَ أَزْوَاجِكَ ۚ وَاللهُ غَفُورٌ رَّحِيمٌ
Ya ayyuha annabiyyulima tuharrimu ma ahalla Allahu lakatabtaghee mardata
azwajika wallahughafoorun raheem
Hausa
Yã kai Annabi! Don me kake haramta abin da Allah Ya halatta maka, kanã nẽman
yardar mãtanka, alhãli kuwa Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
|
Ayah 66:2 الأية
قَدْ فَرَضَ اللهُ لَكُمْ تَحِلَّةَ أَيْمَانِكُمْ ۚ وَاللهُ مَوْلَاكُمْ ۖ
وَهُوَ الْعَلِيمُ الْحَكِيمُ
Qad farada Allahu lakum tahillataaymanikum wallahu mawlakum wahuwaalAAaleemu
alhakeem
Hausa
Haƙĩƙa Allah ya faralta muku warware rantsuwõyinku, kuma Allah ne Mataimakinku
kuma shĩ ne Masani, Mai hikima.
|
Ayah 66:3 الأية
وَإِذْ أَسَرَّ النَّبِيُّ إِلَىٰ بَعْضِ أَزْوَاجِهِ حَدِيثًا فَلَمَّا نَبَّأَتْ
بِهِ وَأَظْهَرَهُ اللهُ عَلَيْهِ عَرَّفَ بَعْضَهُ وَأَعْرَضَ عَن بَعْضٍ ۖ
فَلَمَّا نَبَّأَهَا بِهِ قَالَتْ مَنْ أَنبَأَكَ هَٰذَا ۖ قَالَ نَبَّأَنِيَ
الْعَلِيمُ الْخَبِيرُ
Wa-ith asarra annabiyyu ilabaAAdi azwajihi hadeethan falammanabbaat bihi
waathharahu Allahu AAalayhiAAarrafa baAAdahu waaAArada AAan baAAdinfalamma
nabbaaha bihi qalat man anbaaka hathaqala nabbaaniya alAAaleemu alkhabeer
Hausa
Kuma a sã'ilin da Annabi ya asirta wani lãbãri zuwa ga sãshen mãtansa, to, a
lõkacin da ta bã da lãbari da shi. Kuma Allah Ya bayyana shi a gare shi, ya
sanar da sãshensa kuma ya kau da kai daga wani sãshe. To, a lõkacin da ya bã ta
lãbãri da shi, ta ce: "Wãne ne ya gaya maka wannan?" Ya ce: "Masani, Mai
labartãwa, Ya gaya mini."
|
Ayah 66:4 الأية
إِن تَتُوبَا إِلَى اللهِ فَقَدْ صَغَتْ قُلُوبُكُمَا ۖ وَإِن تَظَاهَرَا
عَلَيْهِ فَإِنَّ اللهَ هُوَ مَوْلَاهُ وَجِبْرِيلُ وَصَالِحُ الْمُؤْمِنِينَ ۖ
وَالْمَلَائِكَةُ بَعْدَ ذَٰلِكَ ظَهِيرٌ
In tatooba ila Allahifaqad saghat quloobukuma wa-in tathaharaAAalayhi fa-inna
Allaha huwa mawlahu wajibreelu wasalihualmu/mineena walmala-ikatu baAAda thalika
thaheer
Hausa
Idan kũ biyu kuka tũba zuwa ga Allah, to, haƙĩƙa zukãtanku sun karkata. Kuma
idan kun taimaki jũna a kansa to, lalle Allah Shĩ ne Mataimakinsa, da Jibrĩlu da
sãlihan mũminai. Kuma malã'iku a bãyan wancan, mataimaka ne.
|
Ayah 66:5 الأية
عَسَىٰ رَبُّهُ إِن طَلَّقَكُنَّ أَن يُبْدِلَهُ أَزْوَاجًا خَيْرًا مِّنكُنَّ
مُسْلِمَاتٍ مُّؤْمِنَاتٍ قَانِتَاتٍ تَائِبَاتٍ عَابِدَاتٍ سَائِحَاتٍ ثَيِّبَاتٍ
وَأَبْكَارًا
AAasa rabbuhu in tallaqakunnaan yubdilahu azwajan khayran minkunna
muslimatinmu/minatin qanitatin ta-ibatinAAabidatin sa-ihatin thayyibatinwaabkara
Hausa
Mai yiwuwa ne Ubangijinsa, idan ya sake ku, Ya musanya masa waɗansu mãtan aure
mafiya alhẽri daga gare ku, Musulmai mũminai mãsu tawãli'u, mãsu tũba, mãsu
ibãda, mãsu, azumi, zawarõri da 'yammãta.
|
Ayah 66:6 الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا قُوا أَنفُسَكُمْ وَأَهْلِيكُمْ نَارًا وَقُودُهَا
النَّاسُ وَالْحِجَارَةُ عَلَيْهَا مَلَائِكَةٌ غِلَاظٌ شِدَادٌ لَّا يَعْصُونَ
اللهَ مَا أَمَرَهُمْ وَيَفْعَلُونَ مَا يُؤْمَرُونَ
Ya ayyuha allatheena amanooqoo anfusakum waahleekum naran waqooduha
annasuwalhijaratu AAalayha mala-ikatunghilathun shidadun la yaAAsoonaAllaha ma
amarahum wayafAAaloona mayu/maroon
Hausa
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kãre wa kanku (da iyãlinku wata wuta
makãmashinta mutãne da duwãtsu ne. A kanta akwai waɗansu malã'iku mãsu kauri,
mãsu ƙarfi. Bã su sãɓã wa Allah ga abin da Ya umurce su, kuma sunã aikata abin
da ake umunin su.
|
Ayah 66:7 الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ كَفَرُوا لَا تَعْتَذِرُوا الْيَوْمَ ۖ إِنَّمَا تُجْزَوْنَ
مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
Ya ayyuha allatheenakafaroo la taAAtathiroo alyawma innamatujzawna ma kuntum
taAAmaloon
Hausa
Yã kũ waɗanda suka kãfirta ! Kada ku kãwo wani uzuri a yau. Anã yi muku
sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa kawai ne.
|
Ayah 66:8 الأية
يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا تُوبُوا إِلَى اللهِ تَوْبَةً نَّصُوحًا عَسَىٰ
رَبُّكُمْ أَن يُكَفِّرَ عَنكُمْ سَيِّئَاتِكُمْ وَيُدْخِلَكُمْ جَنَّاتٍ تَجْرِي
مِن تَحْتِهَا الْأَنْهَارُ يَوْمَ لَا يُخْزِي اللهُ النَّبِيَّ وَالَّذِينَ
آمَنُوا مَعَهُ ۖ نُورُهُمْ يَسْعَىٰ بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَبِأَيْمَانِهِمْ
يَقُولُونَ رَبَّنَا أَتْمِمْ لَنَا نُورَنَا وَاغْفِرْ لَنَا ۖ إِنَّكَ عَلَىٰ
كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ
Ya ayyuha allatheena amanootooboo ila Allahi tawbatan nasoohanAAasa rabbukum an
yukaffira AAankum sayyi-atikumwayudkhilakum jannatin tajree min tahtihaal-anharu
yawma la yukhzee Allahu annabiyyawallatheena amanoo maAAahu nooruhum yasAAabayna
aydeehim wabi-aymanihim yaqooloona rabbanaatmim lana noorana waghfir lanainnaka
AAala kulli shay-in qadeer
Hausa
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku kõma zuwa ga Allah kõmawar gaskiya. Mai yiwuwa
Ubangjinku Ya kankare muku miyãgun ayyukanku kuma Ya shigar da ku a gidãjen
Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashinsu a rãnar da Allah bã Ya kunyatar da
Annabi da wadanda suka yi ĩmãni tãre da shi. Haskensu yanã tafiya a gaba gare su
da jihõhin dãmansu, sunã cẽwa, "Yã Ubangijiumu! Ka cika mana haskenmu, kuma Ka
yi mana gãfara. Lalle Kai, a kan dukkan kõme, Yã kai Mai ikon yi ne."
|
Ayah 66:9 الأية
يَا أَيُّهَا النَّبِيُّ جَاهِدِ الْكُفَّارَ وَالْمُنَافِقِينَ وَاغْلُظْ
عَلَيْهِمْ ۚ وَمَأْوَاهُمْ جَهَنَّمُ ۖ وَبِئْسَ الْمَصِيرُ
Ya ayyuha annabiyyu jahidialkuffara walmunafiqeena waghluthAAalayhim wama/wahum
jahannamu wabi/sa almaseer
Hausa
Yã kai Annabi! Ka yãki kãfirai da munãfwkai. Kuma ka tsananta a kansu. Kuma
matattararsu Jahannama ce, kuma tir da makoma, ita.
|
Ayah 66:10 الأية
ضَرَبَ اللهُ مَثَلًا لِّلَّذِينَ كَفَرُوا امْرَأَتَ نُوحٍ وَامْرَأَتَ لُوطٍ ۖ
كَانَتَا تَحْتَ عَبْدَيْنِ مِنْ عِبَادِنَا صَالِحَيْنِ فَخَانَتَاهُمَا فَلَمْ
يُغْنِيَا عَنْهُمَا مِنَ اللهِ شَيْئًا وَقِيلَ ادْخُلَا النَّارَ مَعَ
الدَّاخِلِينَ
Daraba Allahu mathalan lillatheenakafaroo imraata noohin wamraata lootin
kanatatahta AAabdayni min AAibadina salihaynifakhanatahuma falam yughniya
AAanhumamina Allahi shay-an waqeela odkhula annaramaAAa addakhileen
Hausa
Allah Ya buga wani misãli dõmin waɗanda suka kãfirta : mãtar Nũhu da mãtar Lũɗu,
sun kasance a ƙarƙashin wasu bãyi biyu daga bãyinMu sãlihai, saisuka yaudare su,
sabõda haka ba su wadãtar musu da kõme daga Allah ba. Kuma aka ce: "Ku shiga, kũ
biyu, wutã tãre da mãsu shiga."
|
Ayah 66:11 الأية
وَضَرَبَ اللهُ مَثَلًا لِّلَّذِينَ آمَنُوا امْرَأَتَ فِرْعَوْنَ إِذْ قَالَتْ
رَبِّ ابْنِ لِي عِندَكَ بَيْتًا فِي الْجَنَّةِ وَنَجِّنِي مِن فِرْعَوْنَ
وَعَمَلِهِ وَنَجِّنِي مِنَ الْقَوْمِ الظَّالِمِينَ
Wadaraba Allahu mathalan lillatheenaamanoo imraata firAAawna ith qalat rabbiibni
lee AAindaka baytan fee aljannati wanajjinee min firAAawnawaAAamalihi wanajjinee
mina alqawmi aththalimeen
Hausa
Kuma Allah Ya buga wani misãli dõmin waɗanda suka yi ĩmãni; matar Fir'auna,
sa'ad da ta ce "Ya Ubangiji! Ka gina mini wani gida a wurinKa a cikin Aljanna.
Kuma Ka tsĩrar da ni daga Fir'auna da aikinsa. Kuma Ka tsĩrar da ni daga mutãnen
nan azzãlumai."
|
Ayah 66:12 الأية
وَمَرْيَمَ ابْنَتَ عِمْرَانَ الَّتِي أَحْصَنَتْ فَرْجَهَا فَنَفَخْنَا فِيهِ مِن
رُّوحِنَا وَصَدَّقَتْ بِكَلِمَاتِ رَبِّهَا وَكُتُبِهِ وَكَانَتْ مِنَ
الْقَانِتِينَ
Wamaryama ibnata AAimrana allatee ahsanatfarjaha fanafakhna feehi min
roohinawasaddaqat bikalimati rabbiha wakutubihi wakanatmina alqaniteen
Hausa
Da Maryama ɗiyar Imrãna wadda ta tsare farjinta, sai Muka hũra a cikinsa daga
rũhinMu. Kuma ta gaskata game da ãyõyin Ubangijinta da LittattafanSa alhãli kuwa
ta kasance daga mãsu tawãli'u.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|