Prev  

92. Surah Al-Lail سورة الليل

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ
Wallayli itha yaghsha

Hausa
 
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.

Ayah  92:2  الأية
وَالنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ
Wannahari itha tajalla

Hausa
 
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.

Ayah  92:3  الأية
وَمَا خَلَقَ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ
Wama khalaqa aththakarawal-ontha

Hausa
 
Da abin da ya halitta namiji da mace.

Ayah  92:4  الأية
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ
Inna saAAyakum lashatta

Hausa
 
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.

Ayah  92:5  الأية
فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَاتَّقَىٰ
Faamma man aAAta wattaqa

Hausa
 
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.

Ayah  92:6  الأية
وَصَدَّقَ بِالْحُسْنَىٰ
Wasaddaqa bilhusna

Hausa
 
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.

Ayah  92:7  الأية
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْيُسْرَىٰ
Fasanuyassiruhu lilyusra

Hausa
 
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.

Ayah  92:8  الأية
وَأَمَّا مَن بَخِلَ وَاسْتَغْنَىٰ
Waamma man bakhila wastaghna

Hausa
 
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.

Ayah  92:9  الأية
وَكَذَّبَ بِالْحُسْنَىٰ
Wakaththaba bilhusna

Hausa
 
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.

Ayah  92:10  الأية
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْعُسْرَىٰ
Fasanuyassiruhu lilAAusra

Hausa
 
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.

Ayah  92:11  الأية
وَمَا يُغْنِي عَنْهُ مَالُهُ إِذَا تَرَدَّىٰ
Wama yughnee AAanhu maluhu ithataradda

Hausa
 
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).

Ayah  92:12  الأية
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ
Inna AAalayna lalhuda

Hausa
 
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.

Ayah  92:13  الأية
وَإِنَّ لَنَا لَلْآخِرَةَ وَالْأُولَىٰ
Wa-inna lana lal-akhirata wal-oola

Hausa
 
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.

Ayah  92:14  الأية
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّىٰ
Faanthartukum naran talaththa

Hausa
 
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.

Ayah  92:15  الأية
لَا يَصْلَاهَا إِلَّا الْأَشْقَى
La yaslaha illaal-ashqa

Hausa
 
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.

Ayah  92:16  الأية
الَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Allathee kaththaba watawalla

Hausa
 
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.

Ayah  92:17  الأية
وَسَيُجَنَّبُهَا الْأَتْقَى
Wasayujannabuha al-atqa

Hausa
 
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.

Ayah  92:18  الأية
الَّذِي يُؤْتِي مَالَهُ يَتَزَكَّىٰ
Allathee yu/tee malahuyatazakka

Hausa
 
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa ,alhãli yana tsarkaka.

Ayah  92:19  الأية
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَىٰ
Wama li-ahadin AAindahu minniAAmatin tujza

Hausa
 
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.

Ayah  92:20  الأية
إِلَّا ابْتِغَاءَ وَجْهِ رَبِّهِ الْأَعْلَىٰ
Illa ibtighaa wajhi rabbihial-aAAla

Hausa
 
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.

Ayah  92:21  الأية
وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ
Walasawfa yarda

Hausa
 
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi) . 
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us