1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ
Wallayli itha yaghsha
Hausa
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
|
Ayah 92:2 الأية
وَالنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ
Wannahari itha tajalla
Hausa
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
|
Ayah 92:3 الأية
وَمَا خَلَقَ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ
Wama khalaqa aththakarawal-ontha
Hausa
Da abin da ya halitta namiji da mace.
|
Ayah 92:4 الأية
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ
Inna saAAyakum lashatta
Hausa
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
|
Ayah 92:5 الأية
فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَاتَّقَىٰ
Faamma man aAAta wattaqa
Hausa
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
|
Ayah 92:6 الأية
وَصَدَّقَ بِالْحُسْنَىٰ
Wasaddaqa bilhusna
Hausa
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
|
Ayah 92:7 الأية
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْيُسْرَىٰ
Fasanuyassiruhu lilyusra
Hausa
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
|
Ayah 92:8 الأية
وَأَمَّا مَن بَخِلَ وَاسْتَغْنَىٰ
Waamma man bakhila wastaghna
Hausa
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
|
Ayah 92:9 الأية
وَكَذَّبَ بِالْحُسْنَىٰ
Wakaththaba bilhusna
Hausa
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
|
Ayah 92:10 الأية
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْعُسْرَىٰ
Fasanuyassiruhu lilAAusra
Hausa
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
|
Ayah 92:11 الأية
وَمَا يُغْنِي عَنْهُ مَالُهُ إِذَا تَرَدَّىٰ
Wama yughnee AAanhu maluhu ithataradda
Hausa
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
|
Ayah 92:12 الأية
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ
Inna AAalayna lalhuda
Hausa
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
|
Ayah 92:13 الأية
وَإِنَّ لَنَا لَلْآخِرَةَ وَالْأُولَىٰ
Wa-inna lana lal-akhirata wal-oola
Hausa
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
|
Ayah 92:14 الأية
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّىٰ
Faanthartukum naran talaththa
Hausa
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
|
Ayah 92:15 الأية
لَا يَصْلَاهَا إِلَّا الْأَشْقَى
La yaslaha illaal-ashqa
Hausa
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
|
Ayah 92:16 الأية
الَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Allathee kaththaba watawalla
Hausa
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
|
Ayah 92:17 الأية
وَسَيُجَنَّبُهَا الْأَتْقَى
Wasayujannabuha al-atqa
Hausa
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
|
Ayah 92:18 الأية
الَّذِي يُؤْتِي مَالَهُ يَتَزَكَّىٰ
Allathee yu/tee malahuyatazakka
Hausa
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa ,alhãli yana tsarkaka.
|
Ayah 92:19 الأية
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَىٰ
Wama li-ahadin AAindahu minniAAmatin tujza
Hausa
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
|
Ayah 92:20 الأية
إِلَّا ابْتِغَاءَ وَجْهِ رَبِّهِ الْأَعْلَىٰ
Illa ibtighaa wajhi rabbihial-aAAla
Hausa
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
|
Ayah 92:21 الأية
وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ
Walasawfa yarda
Hausa
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi) .
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|