Muhawara Hausa
 



ARBA'UNA HAADITH (33) HADISI NA TALATIN DA UKU
 
Al'Adun Musulmi Da Darajoji ARBA'UNA HAADITH (33) HADISI NA TALATIN DA UKU

An karbo daga Abdullahi dan Abbas (R.A) ya ce, Manzon Allah Annabi (S.A.W). ya ce, ''Da za'a bai wa mutune dukkan da'awarsu, da wadansu sun yi da'awar dukiyar wadansu da jininsu' sai dai hujja tana kan mai da'awa, rantsuwa kuma a kan wanda ya yi musu.''(1) Baihaki ne ya rawito shi a cikin litaffinsa sunan (J 10/sh 252). Wani sashi na hadisin yana cikin Bukhari da Muslim.

SHARHI; Ma'ana, da duk da'awar da mutane za su yi, za'a dauka a ba su wannan abin da suka yi da'awa, misali in sun ce kaza namu ne, a ba su, ba tare da shaida ba, ba tare da an bincike ba, ''...... da wadansu sun yi da'awar dukiyar wadansu.....'' Da sun yi da'awar jinin wasu, sai Annabi (S.A.W). y ace ''...... sai dai hujja tana kan mai da'awa.....'' 

Ma'ana, ana neman mai da'awa da ita, wanda kuma ake nema day a yi rantsuwa, shi ne wanda ya yi musu, abin nufi idan na zo n ace motar da wane yake kawa tawa ce, to a shari'ance kafin ya hana ni, wannan abin da na kawo shaida. Idan na kawo shaidu suka tabbatar da wannan taw ace, dole a karbe wannan mota a ba ni, a shari'ance. Shi kuma in ya yi nikari, y ace sam! Duk da shaidar nan da na zio da ita bai yarda ba, to sai ya yi rantsuwa, don a tabbatar da haka ne. wato dai kullum mai da'awa shi ne ake bin bashin dalili idan mutum ya yi da'awar kaza haramun ne, shi za'a ce ya kawo dalilinsa, idan mutum ya yi da'awar halacci a cikin abin da asalinsa haramci ne, to wannan shi za a nemi ya kawo dalili.

Wannan hadisi asalinsa mai girma nes kwarai da gaske, yana shiga babuka da dama, musamman ma babin day a shafi hadddi, babin day a shafi rigingimu a tsakanin mutane da rigimar dukiya. Hadisi dai yana shiga babi da daman a fikihu da babin ma'amaloli.

(FASSARA DA SHARHI DA GA BAKIN GARIGAYI SHEIK JA'AFAR MAHAMUD ADAM {R} ).

 Posted By Aka Sanya A Tuesday, May 09 @ 04:49:08 PDT Da MediaHausaTeam



Comments 💬 التعليقات
 

For Your Membership Comments And Registered Debates Please, See Below Or Register Here :-: للحصول على تعليقات عضويتك و مناقشات الأعضاء انظر من فضلك أدناه أو سجّل هنا

Hanyoyin da ke da alaƙa

· Ƙari Game da Al'Adun Musulmi Da Darajoji
· Labarai By MediaHausaTeam


Mafi Karanta Labari Game da Al'Adun Musulmi Da Darajoji:
Sahabban Manzon Allah (SAW) Kamar Yadda Hadisai Suka Bayyana Su


Matsalar Magana

Matsakaicin Maki: 0
Kurioi: 0

Don Allah a Ɗauki Na Biyu Ka Zabi Wannan Labarin:

Madalla
Mai kyau sosai
Mai kyau
Na yau da kullum
Bad


Zabuka


 Mawallafin Aboki Mawallafin Aboki





Ya Danganta Kanun Labarai

Al'Adun Musulmi Da Darajoji



"ARBA'UNA HAADITH (33) HADISI NA TALATIN DA UKU" | Shiga/ Ƙirƙiri Asusu | 0 Lafiyata


Malakacin Bayanan na Mai aikawa. Ba Mu Da Alhaki Don Abubuwan da Suke ciki. A halin yanzu, Muna gayyatar masu karatu su ba da rahoton duk wani abu na cin zarafi, rashin dacewa da / ko abun ciki na Islama



Babu Sharhi Ta da Aka Bada izini Don Marasa Suna, Da fatan za a Yi rijista
 

Muhawara Hausa
Asusu Gare Ku
Babban Shafi  | Labarun Hausa  | Muhawara Hausa  | Ƙungiyar Hausa  | Saƙonninku Na Sirri  | Samiya Goma  | Batutuwa  | Takardun Labari  | Cagiya  | Yakan Yi Bitar  | Bincike  | Mujallan  | Ma\'ajiyar Takardu  | Shafin Yanar Gizo  | Saukewa  | Shawarce Mu


Ẹsin Islam الدين الإسلامي Religion of Islam Addinin Musulunci Agama Islam Religión del Islam 伊斯兰教 Dini ya Kiislamu Религия Ислам Religião do Islã イスラム教 Esin Islam 이슬람의 종교 Portal African Muslim Website - Arabic English African Islamic Website For World News, Fatwas, Audios, Videos, Muslim News, Articles, Radio, Audio, Video, Quran, Hadith, TV Channels, Fatwas, Muslim News, Newspapers, Magazines Headlines, Forums, College, Schools, Universities, Mosques, Quranic, Sunnah, Fiqh, Prayers, Salat, Ramadan, Vidoes, Books, Fasting, PDFs On EsinIslam.Com And IslamAfrica.Com