Muhawara Hausa
 



Hukuncin wanda yayi Sallah ba zuwa ga Alqibla ba A mantuwa
 
Kacici-ka-cicin Addini, Hukunce-hukuncen Hukuncin wanda yayi Sallah ba zuwa ga Alqibla ba A mantuwa

Tambaya: Meye hukuncin mutumin da yayi sallah, sai bayan ya gama sannan ya fahimci cewa wannan sallah da yayi ba Alqibla ya fuskanta ba?

Amsa: yana daga cikin sharadin sallah mutum ya fuskanci Alqibla matukar ba wata matsala aka samu ba wadda zata hanashi hakan, inhar ko mutum yaki fuskantar Alqibla alhalin yana da dama toh sallarsa batacciya ce, sabida Allah yace ''Ka juya da fuskarka zuwa ga masallaci Tsararre'' (Baqara 144). Da umarnin da annabi(Sallallahu alaihi wasallam) yayi yace ''Sannan ka fuskanci alQibla kayi kabbara) Bukhari 6667.

Maluman sun tafi akan cewa wanda yayi sallah ba zuwa ga Alqibla ba da gangan ko a halin mantuwa zai sake, sabida bai cika sharadinta ba, an tambayi maluman 'Lajnatudda'imah' kan hukuncin matafiyi da ya isa gari, yayi sallah ba zuwa ga alqibla ba, kuma bai tambaya ba, baiyi bincike ba, suka bada amsar cewa zai sake wannan sallar, sabida rashin bincike da baiyi ba, ko kokari wurin gano alqiblar, (Lajnatudda'imah Majmu'ah ta biyu 5/294).

Da haka, ya wajaba akan wanda yayi sallah ba zuwa ga Alqibla ba yana mai mantuwa ya sake sallansa, amma in ya rasa gane Alqibla sabida rashin wanda zai tambaya, ko kuma wasu dalilai, toh mafi yawan Malamai suna akan bazai sake ba. kuma hakan shine daidai......... Allahu A'alam.

Maraba Da watan Ramadan Watan Albarka

Maraba Da watan Ramadan Watan Albarka

Assalaamu Alaikum Warahmatullahi Wabarkaatuh 'yan'uwa Musulmai ina tayaku murnan Shigarmu wannan wata ta ramadana Mai Albarka. Ina rokon Allah Ya azurtamu dayin aikin alkhairi acikinta, kuma Yasa ayyukanmu su zamto karbabbu, Allah kuma ya yaye mana duk bala'I da musibu da suke addabarmu Yasa Mugama Lafiya.

Bayan Haka inaso in dan jaa hankalinmu ne kan wasu lamura da ya dace muyi acikin wannan wata mai albarka, da kuma abinda ya dace mu kiyaye. Babban abinda wannan wata ta kunsa na ibada itace azumin watan ramadan wanda wannan farilla ce kuma tana daga cikin rukunan musulunci guda biyar. Wadda duk wanda Allah yabashi iko dolene a gareshi yayi wannan azumi. sannan bayan azumi sai tsayuwar dare da ake kira 'tarawihi' shi kuma wannan 'sunnah ce mai karfi' wadda akeso musulmi Ya kiyayeta acikin wannan wata kuma yayita tare da jama'a acikin masallaci sai dai in akwai uzuri. Wannan sallah raka'a 'goma sha daya ce' kaman yanda ya tabbata a hadisin Aisha(R.A) tace :'Manzon Allah ya kasance baya karawa akan raka'a sha daya a sallan dare acikin ramadan ko a wajensa' tsayawa kan raka'a sha daya shi zaifi samar wa mutum natsuwa sosai sannan kuma hakan zai taimaka masa wurin kauce wa tsabanin malamai ga masu Ganin ana iya yin har ashirin da daya, sannan bayan wa'innan ibadu biyu na azumi da tarawihi anaso mutum ya yawaita karanta Alqur'ani mai girma, domin wannan watace ta Qur'ani, sannan karatun qur'ani a wannan wata tana kawo wa mutum lada matuka domin kaman yanda muka sani ne duk wata aikin lada a ramadan ana ninkata. Sannan kuma da halartar majalisin da ake karatun Qur'anin, ko tafsirinsa domin yin tadabburi da Qur'anin da sanin ma'anoninsa. Sannan kuma sai yawaita salatin annabi da zikirori. Ya kamata musulmi ya kasance a kowani lokacinsa ya jike bakinsa da salatin annabi, da kuma zikirori ingantattu wanda suka tabbata. Hakan zai taimakawa mutum da kare kansa da yawan surutai da basu da amfani ko kuma shiga wata hayaaniya. Sannan kuma ya kamata musulmi ya kaurace wa duk wata tsabon Allah, duk abinda zai zamanto cewa tsabon Allah ne toh ya zama wajibi mutum ya kauce mata. Domin azumi bawai kawai kamewa daga abinci ko abin sha bane, A'a ta kunshi kamewa daga duk tsabon Allah, ta maganar banza, ko zage zage, ko gulma, ko kallace kallace da sauransu. Sai mu kiyaye 'yan'uwa. Muyi duk abinda mukasan zai jawo mana yardar Allah, mukauce wa duk abinda zai janyo mana fushinsa. Sannan kada ya zamto bayan gushewar ramadan mudawo muci gaba da ayyukanmu marasa kyau, ya kamata koda bayan ramadan ne muci gaba Da ayyuka ta ibada da biyayya ga Allah da mukeyi acikin ramadan. Ina fatan Allah ya sadamu da alkhairansa. Wassakamu alaikum.

 Posted By Aka Sanya A Wednesday, October 04 @ 09:49:31 PDT Da MediaHausaTeam



Comments 💬 التعليقات
 

For Your Membership Comments And Registered Debates Please, See Below Or Register Here :-: للحصول على تعليقات عضويتك و مناقشات الأعضاء انظر من فضلك أدناه أو سجّل هنا

Hanyoyin da ke da alaƙa

· Ƙari Game da Kacici-ka-cicin Addini, Hukunce-hukuncen
· Labarai By MediaHausaTeam


Mafi Karanta Labari Game da Kacici-ka-cicin Addini, Hukunce-hukuncen:
Sako daga marigayi Umaru Musa `Yar`aduwa


Matsalar Magana

Matsakaicin Maki: 0
Kurioi: 0

Don Allah a Ɗauki Na Biyu Ka Zabi Wannan Labarin:

Madalla
Mai kyau sosai
Mai kyau
Na yau da kullum
Bad


Zabuka


 Mawallafin Aboki Mawallafin Aboki





Ya Danganta Kanun Labarai

Kacici-ka-cicin Addini, Hukunce-hukuncen



"Hukuncin wanda yayi Sallah ba zuwa ga Alqibla ba A mantuwa" | Shiga/ Ƙirƙiri Asusu | 0 Lafiyata


Malakacin Bayanan na Mai aikawa. Ba Mu Da Alhaki Don Abubuwan da Suke ciki. A halin yanzu, Muna gayyatar masu karatu su ba da rahoton duk wani abu na cin zarafi, rashin dacewa da / ko abun ciki na Islama



Babu Sharhi Ta da Aka Bada izini Don Marasa Suna, Da fatan za a Yi rijista
 

Muhawara Hausa
Asusu Gare Ku
Babban Shafi  | Labarun Hausa  | Muhawara Hausa  | Ƙungiyar Hausa  | Saƙonninku Na Sirri  | Samiya Goma  | Batutuwa  | Takardun Labari  | Cagiya  | Yakan Yi Bitar  | Bincike  | Mujallan  | Ma\'ajiyar Takardu  | Shafin Yanar Gizo  | Saukewa  | Shawarce Mu


Ẹsin Islam الدين الإسلامي Religion of Islam Addinin Musulunci Agama Islam Religión del Islam 伊斯兰教 Dini ya Kiislamu Религия Ислам Religião do Islã イスラム教 Esin Islam 이슬람의 종교 Portal African Muslim Website - Arabic English African Islamic Website For World News, Fatwas, Audios, Videos, Muslim News, Articles, Radio, Audio, Video, Quran, Hadith, TV Channels, Fatwas, Muslim News, Newspapers, Magazines Headlines, Forums, College, Schools, Universities, Mosques, Quranic, Sunnah, Fiqh, Prayers, Salat, Ramadan, Vidoes, Books, Fasting, PDFs On EsinIslam.Com And IslamAfrica.Com