Prev  

34. Surah Saba' سورة سبأ

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الْحَمْدُ لِلَّهِ الَّذِي لَهُ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ وَلَهُ الْحَمْدُ فِي الْآخِرَةِ ۚ وَهُوَ الْحَكِيمُ الْخَبِيرُ
Alhamdu lillahi allatheelahu ma fee assamawati wamafee al-ardi walahu alhamdu fee al-akhiratiwahuwa alhakeemu alkhabeer

Hausa
 
Gődiya ta tabbata ga Allah, wanda Yake abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasă Năsa ne, kuma shĩ ne Mai hikima, Mai labartawa.

Ayah  34:2  الأية
يَعْلَمُ مَا يَلِجُ فِي الْأَرْضِ وَمَا يَخْرُجُ مِنْهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ السَّمَاءِ وَمَا يَعْرُجُ فِيهَا ۚ وَهُوَ الرَّحِيمُ الْغَفُورُ
YaAAlamu ma yaliju fee al-ardiwama yakhruju minha wama yanzilu mina assama-iwama yaAAruju feeha wahuwa arraheemualghafoor

Hausa
 
Yă san abin da yake shiga a cikin ƙasă da abin da yake fita daga gare ta, da abin da yake sauka daga sama da abin da yake hawa a cikinta, kuma Shĩ ne Mai jin ƙai, Mai găfara.

Ayah  34:3  الأية
وَقَالَ الَّذِينَ كَفَرُوا لَا تَأْتِينَا السَّاعَةُ ۖ قُلْ بَلَىٰ وَرَبِّي لَتَأْتِيَنَّكُمْ عَالِمِ الْغَيْبِ ۖ لَا يَعْزُبُ عَنْهُ مِثْقَالُ ذَرَّةٍ فِي السَّمَاوَاتِ وَلَا فِي الْأَرْضِ وَلَا أَصْغَرُ مِن ذَٰلِكَ وَلَا أَكْبَرُ إِلَّا فِي كِتَابٍ مُّبِينٍ
Waqala allatheena kafaroo lata/teena assaAAatu qul bala warabbeelata/tiyannakum AAalimi alghaybi la yaAAzubu AAanhumithqalu tharratin fee assamawatiwala fee al-ardi wala asgharu min thalikawala akbaru illa fee kitabin mubeen

Hausa
 
Kuma waɗanda suka kăfirta suka ce: "Să'a bă ză ta zo mana ba." Ka ce: "Kayya! Na rantse da Ubangijĩna, lalle, ză ta ző muku." Masanin gaibi, gwargwadon zarra bă ta nĩsanta daga gare Shi a cikin sammai kuma bă ta nĩsanta a cikin ƙasă, kuma băbu mafi ƙaranci daga wancan kuma băbu mafi girma făce yană a cikin Littăfi bayyananne.

Ayah  34:4  الأية
لِّيَجْزِيَ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ ۚ أُولَٰئِكَ لَهُم مَّغْفِرَةٌ وَرِزْقٌ كَرِيمٌ
Liyajziya allatheena amanoowaAAamiloo assalihati ola-ika lahummaghfiratun warizqun kareem

Hausa
 
Dőmin Ya săkă wa waɗanda suka yi ĩmăni kuma suka aikata ayyukan ƙwarai. Waɗancan suna da wata găfara da wani arziki mai karimci.

Ayah  34:5  الأية
وَالَّذِينَ سَعَوْا فِي آيَاتِنَا مُعَاجِزِينَ أُولَٰئِكَ لَهُمْ عَذَابٌ مِّن رِّجْزٍ أَلِيمٌ
Wallatheena saAAaw fee ayatinamuAAajizeena ola-ika lahum AAathabun minrijzin aleem

Hausa
 
Kuma waɗanda suka yi măkirci ga ăyőyinMu, sună măsu gajiyarwa, waɗannan sună da wata azăba daga azăba mai raɗaɗi.

Ayah  34:6  الأية
وَيَرَى الَّذِينَ أُوتُوا الْعِلْمَ الَّذِي أُنزِلَ إِلَيْكَ مِن رَّبِّكَ هُوَ الْحَقَّ وَيَهْدِي إِلَىٰ صِرَاطِ الْعَزِيزِ الْحَمِيدِ
Wayara allatheena ootooalAAilma allathee onzila ilayka min rabbika huwa alhaqqawayahdee ila sirati alAAazeezi alhameed

Hausa
 
Kuma waɗanda aka bai wa ilmi sună ganin abin nan da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka, shi ne gaskiya, kuma yană shiryarwa zuwa ga hanyar Mabuwăyi, Gődadde.

Ayah  34:7  الأية
وَقَالَ الَّذِينَ كَفَرُوا هَلْ نَدُلُّكُمْ عَلَىٰ رَجُلٍ يُنَبِّئُكُمْ إِذَا مُزِّقْتُمْ كُلَّ مُمَزَّقٍ إِنَّكُمْ لَفِي خَلْقٍ جَدِيدٍ
Waqala allatheena kafaroo halnadullukum AAala rajulin yunabbi-okum ithamuzziqtum kulla mumazzaqin innakum lafee khalqin jadeed

Hausa
 
Kuma waɗanda suka kăfirta suka ce: "Shin ză mu nũna muku wani namiji wanda yake gaya muku wai idan an tsattsăge ku, kőwace irin tsattsăgẽwa, lalle kũ, tabbas, kună a cikin wata halitta săbuwa.?"

Ayah  34:8  الأية
أَفْتَرَىٰ عَلَى اللهِ كَذِبًا أَم بِهِ جِنَّةٌ ۗ بَلِ الَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِالْآخِرَةِ فِي الْعَذَابِ وَالضَّلَالِ الْبَعِيدِ
Aftara AAala Allahi kathibanam bihi jinnatun bali allatheena la yu/minoona bil-akhiratifee alAAathabi waddalali albaAAeed

Hausa
 
"Ya ƙăga ƙarya ga Allah ne kő kuwa akwai wata hauka a gare shi?" Ă'a, waɗanda ba su yi ĩmăni da Lăhira ba, sună a cikin azăba da ɓăta mai nĩsa.

Ayah  34:9  الأية
أَفَلَمْ يَرَوْا إِلَىٰ مَا بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَمَا خَلْفَهُم مِّنَ السَّمَاءِ وَالْأَرْضِ ۚ إِن نَّشَأْ نَخْسِفْ بِهِمُ الْأَرْضَ أَوْ نُسْقِطْ عَلَيْهِمْ كِسَفًا مِّنَ السَّمَاءِ ۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً لِّكُلِّ عَبْدٍ مُّنِيبٍ
Afalam yaraw ila ma baynaaydeehim wama khalfahum mina assama-i wal-ardiin nasha/ nakhsif bihimu al-arda aw nusqitAAalayhim kisafan mina assama-i inna fee thalikalaayatan likulli AAabdin muneeb

Hausa
 
Ashe fa, ba su yi dũbi ba zuwa ga abin da ke a gaba gare su da abin da ke a băyansu daga sama da ƙasă? idan Mun so, sai Mu shăfe ƙasă da su, kő kuma Mu kăyar da wani ɓaɓɓake daga sama a kansu. Lalle, a cikin wancan akwai ăyă ga dukan băwă mai maida al'amarinsa ga Allah.

Ayah  34:10  الأية
وَلَقَدْ آتَيْنَا دَاوُودَ مِنَّا فَضْلًا ۖ يَا جِبَالُ أَوِّبِي مَعَهُ وَالطَّيْرَ ۖ وَأَلَنَّا لَهُ الْحَدِيدَ
Walaqad atayna dawoodaminna fadlan ya jibalu awwibeemaAAahu wattayra waalanna lahu alhadeed

Hausa
 
Kuma lalle, haƙĩƙa, Mun bai wa Dăwũda wata falala dagagare Mu. Yă duwatsu, ku konkőma sautin tasbihi tăre da shi kuma da tsuntsăye. Kuma Muka tausasa masa baƙin ƙarfe.

Ayah  34:11  الأية
أَنِ اعْمَلْ سَابِغَاتٍ وَقَدِّرْ فِي السَّرْدِ ۖ وَاعْمَلُوا صَالِحًا ۖ إِنِّي بِمَا تَعْمَلُونَ بَصِيرٌ
Ani iAAmal sabighatin waqaddirfee assardi waAAmaloo salihan inneebima taAAmaloona baseer

Hausa
 
Ka aikata sulkuna kuma ka ƙaddara lissăfi ga tsărawa, kuma ka aikata aikin ƙwarai. Lalle NĩMai gani ne ga abin da kuke aikatăwa.

Ayah  34:12  الأية
وَلِسُلَيْمَانَ الرِّيحَ غُدُوُّهَا شَهْرٌ وَرَوَاحُهَا شَهْرٌ ۖ وَأَسَلْنَا لَهُ عَيْنَ الْقِطْرِ ۖ وَمِنَ الْجِنِّ مَن يَعْمَلُ بَيْنَ يَدَيْهِ بِإِذْنِ رَبِّهِ ۖ وَمَن يَزِغْ مِنْهُمْ عَنْ أَمْرِنَا نُذِقْهُ مِنْ عَذَابِ السَّعِيرِ
Walisulaymana arreehaghuduwwuha shahrun warawahuha shahrunwaasalna lahu AAayna alqitri wamina aljinni manyaAAmalu bayna yadayhi bi-ithni rabbihi waman yazighminhum AAan amrina nuthiqhu min AAathabi assaAAeer

Hausa
 
Kuma ga Sulaimăn, Mun hőre masa iska, tafiyarta ta safiya daidai da wata, kuma ta maraice daidai da wata. Kuma Muka gudănar masa da marmaron gaci, kuma daga aljannu (Muka hőre masa) waɗanda ke aiki a gaba gare shi, da iznin Ubangijinsa. Wanda ya karkata daga cikinsu, daga umurninMu, sai Mu ɗanɗana masa daga azăbar sa'ĩr.

Ayah  34:13  الأية
يَعْمَلُونَ لَهُ مَا يَشَاءُ مِن مَّحَارِيبَ وَتَمَاثِيلَ وَجِفَانٍ كَالْجَوَابِ وَقُدُورٍ رَّاسِيَاتٍ ۚ اعْمَلُوا آلَ دَاوُودَ شُكْرًا ۚ وَقَلِيلٌ مِّنْ عِبَادِيَ الشَّكُورُ
YaAAmaloona lahu ma yashao minmahareeba watamatheela wajifanin kaljawabiwaqudoorin rasiyatin iAAmaloo ala dawoodashukran waqaleelun min AAibadiya ashshakoor

Hausa
 
Sună aikata masa abin da yake so, na masallatai da mutummutumai da akussa kamar kududdufai, da tukwăne kafaffu. Ku aikata gődiya, yă ɗiyan Dăwũda, kuma kaɗan ne mai gődiya daga băyĩNa.

Ayah  34:14  الأية
فَلَمَّا قَضَيْنَا عَلَيْهِ الْمَوْتَ مَا دَلَّهُمْ عَلَىٰ مَوْتِهِ إِلَّا دَابَّةُ الْأَرْضِ تَأْكُلُ مِنسَأَتَهُ ۖ فَلَمَّا خَرَّ تَبَيَّنَتِ الْجِنُّ أَن لَّوْ كَانُوا يَعْلَمُونَ الْغَيْبَ مَا لَبِثُوا فِي الْعَذَابِ الْمُهِينِ
Falamma qadaynaAAalayhi almawta ma dallahum AAala mawtihi illadabbatu al-ardi ta/kulu minsaatahu falammakharra tabayyanati aljinnu an law kanoo yaAAlamoonaalghayba ma labithoo fee alAAathabi almuheen

Hausa
 
Sa'an nan a lőkacin da Muka hukunta mutuwa a kansa băbu abin da ya ja hankalinsu, a kan mutuwarsa, făce dabbar ƙasa (gara) wadda take cin sandarsa. To a lőkacin da ya făɗi, sai aljannu suka bayyana (ga mutăne) cẽwa dă sun kasance sun san gaibi, dă ba su zauna ba a cikin azăba mai wulăkantarwa.

Ayah  34:15  الأية
لَقَدْ كَانَ لِسَبَإٍ فِي مَسْكَنِهِمْ آيَةٌ ۖ جَنَّتَانِ عَن يَمِينٍ وَشِمَالٍ ۖ كُلُوا مِن رِّزْقِ رَبِّكُمْ وَاشْكُرُوا لَهُ ۚ بَلْدَةٌ طَيِّبَةٌ وَرَبٌّ غَفُورٌ
Laqad kana lisaba-in fee maskanihim ayatunjannatani AAan yameenin washimalin kuloo min rizqirabbikum washkuroo lahu baldatun tayyibatunwarabbun ghafoor

Hausa
 
Lalle, haƙĩƙa, akwai ăyă ga saba'ăwa a cikin mazauninsu: gőnakin lambu biyu, dama da hagu. "Ku ci daga arzikin Ubangijinku, kuma ku yi gődiya gare shi. Gari mai dăɗin zama, da Ubangiji Mai găfara."

Ayah  34:16  الأية
فَأَعْرَضُوا فَأَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ سَيْلَ الْعَرِمِ وَبَدَّلْنَاهُم بِجَنَّتَيْهِمْ جَنَّتَيْنِ ذَوَاتَيْ أُكُلٍ خَمْطٍ وَأَثْلٍ وَشَيْءٍ مِّن سِدْرٍ قَلِيلٍ
FaaAAradoo faarsalna AAalayhimsayla alAAarimi wabaddalnahum bijannatayhim jannatayni thawatayokulin khamtin waathlin washay-in min sidrin qaleel

Hausa
 
Sai suka bijire sabőda haka Muka saki Mălălin Arimi (dam) a kansu, kuma Muka musanya musu gőnakinsu biyu da waɗansu gőnaki biyu măsu 'ya'yan ităce kaɗan: talăkiya da gőriba da wani abu na magarya kaɗan.

Ayah  34:17  الأية
ذَٰلِكَ جَزَيْنَاهُم بِمَا كَفَرُوا ۖ وَهَلْ نُجَازِي إِلَّا الْكَفُورَ
Thalika jazaynahum bimakafaroo wahal nujazee illa alkafoor

Hausa
 
Wancan, da shi Muka yi musu sakamako sabőda kăfircinsu. Kuma lalle, bă Mu yi wa kőwa irin wannan sakamako, făce kafirai.

Ayah  34:18  الأية
وَجَعَلْنَا بَيْنَهُمْ وَبَيْنَ الْقُرَى الَّتِي بَارَكْنَا فِيهَا قُرًى ظَاهِرَةً وَقَدَّرْنَا فِيهَا السَّيْرَ ۖ سِيرُوا فِيهَا لَيَالِيَ وَأَيَّامًا آمِنِينَ
WajaAAalna baynahum wabayna alquraallatee barakna feeha quran thahiratanwaqaddarna feeha assayra seeroo feehalayaliya waayyaman amineen

Hausa
 
Kuma Muka sanya, a tsakaninsu da tsakănin garũruwan da Muka Sanya albarka a cikinsu, waɗansu garũruwa măsuganin jũna kuma Muka ƙaddara tafiya a cikinsu, "Ku yi tafiya a cikinsu, darũruwa da rănaiku, kună amintattu."

Ayah  34:19  الأية
فَقَالُوا رَبَّنَا بَاعِدْ بَيْنَ أَسْفَارِنَا وَظَلَمُوا أَنفُسَهُمْ فَجَعَلْنَاهُمْ أَحَادِيثَ وَمَزَّقْنَاهُمْ كُلَّ مُمَزَّقٍ ۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَاتٍ لِّكُلِّ صَبَّارٍ شَكُورٍ
Faqaloo rabbana baAAidbayna asfarina wathalamoo anfusahumfajaAAalnahum ahadeetha wamazzaqnahum kullamumazzaqin inna fee thalika laayatin likullisabbarin shakoor

Hausa
 
Sai suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka nĩsantar da tsakănin tafiyőyinmu," kuma suka zălunci kansu, sabőda haka Muka sanya su lăbăran hĩra kuma Muka kekkẽce su kőwace, irin kekkẽcewa. Lalle a cikin wancan akwai ăyőyi ga dukan mai yawan haƙuri, mai yawan gődiya.

Ayah  34:20  الأية
وَلَقَدْ صَدَّقَ عَلَيْهِمْ إِبْلِيسُ ظَنَّهُ فَاتَّبَعُوهُ إِلَّا فَرِيقًا مِّنَ الْمُؤْمِنِينَ
Walaqad saddaqa AAalayhim ibleesu thannahufattabaAAoohu illa fareeqan mina almu/mineen

Hausa
 
Kuma lalle, haƙĩƙa, Iblĩs ya gaskata zatonsa a kansu, sai suka bi shi făce wani ɓangare na mũminai.

Ayah  34:21  الأية
وَمَا كَانَ لَهُ عَلَيْهِم مِّن سُلْطَانٍ إِلَّا لِنَعْلَمَ مَن يُؤْمِنُ بِالْآخِرَةِ مِمَّنْ هُوَ مِنْهَا فِي شَكٍّ ۗ وَرَبُّكَ عَلَىٰ كُلِّ شَيْءٍ حَفِيظٌ
Wama kana lahu AAalayhim minsultanin illa linaAAlama man yu/minu bil-akhiratimimman huwa minha fee shakkin warabbuka AAala kullishay-in hafeeth

Hausa
 
Kuma bă ya da wani dalĩli a kansu făce dai dőmin Mu san wanda yake yin ĩmăni da Lăhira daga wanda yake a cikin shakka daga gare ta. Kuma Ubangijinka, a kan kőme, Mai tsaro ne.

Ayah  34:22  الأية
قُلِ ادْعُوا الَّذِينَ زَعَمْتُم مِّن دُونِ اللهِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ فِي السَّمَاوَاتِ وَلَا فِي الْأَرْضِ وَمَا لَهُمْ فِيهِمَا مِن شِرْكٍ وَمَا لَهُ مِنْهُم مِّن ظَهِيرٍ
Quli odAAoo allatheena zaAAamtum mindooni Allahi la yamlikoona mithqala tharratinfee assamawati wala fee al-ardiwama lahum feehima min shirkin wama lahuminhum min thaheer

Hausa
 
Ka ce: "Ku kirăyi waɗanda kuka riya (cẽwa abũbuwan bautăwa ne) baicin Allah, bă su Mallakar ma'aunin zarra a cikin sammai, kuma bă su Mallakarsa a cikin ƙasa kuma bă su da wani rabon tărẽwa a cikinsu (sammai da ƙasa),kuma bă Shi da wani mataimaki daga gare su.

Ayah  34:23  الأية
وَلَا تَنفَعُ الشَّفَاعَةُ عِندَهُ إِلَّا لِمَنْ أَذِنَ لَهُ ۚ حَتَّىٰ إِذَا فُزِّعَ عَن قُلُوبِهِمْ قَالُوا مَاذَا قَالَ رَبُّكُمْ ۖ قَالُوا الْحَقَّ ۖ وَهُوَ الْعَلِيُّ الْكَبِيرُ
Wala tanfaAAu ashshafaAAatuAAindahu illa liman athina lahu hattaitha fuzziAAa AAan quloobihim qaloo matha qalarabbukum qaloo alhaqqa wahuwa alAAaliyyu alkabeer

Hausa
 
"Kuma wani cẽto bă ya amfăni a wurinSa face fa ga wanda Ya yi izni a gare shi. Har a lőkacin da aka kuranye tsőro daga zukătansu, sai su ce, 'Mẽne ne Ubangijinku Ya ce?' Suka ce: 'Gaskiya', kuma shi ne Maɗaukaki, Mai girma,"

Ayah  34:24  الأية
قُلْ مَن يَرْزُقُكُم مِّنَ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۖ قُلِ اللهُ ۖ وَإِنَّا أَوْ إِيَّاكُمْ لَعَلَىٰ هُدًى أَوْ فِي ضَلَالٍ مُّبِينٍ
Qul man yarzuqukum mina assamawatiwal-ardi quli Allahu wa-inna aw iyyakumlaAAala hudan aw fee dalalin mubeen

Hausa
 
Ka ce: "Wăne ne yake azurta ku daga sama da ƙasa?" Ka ce: "Allah kuma lalle mũ kő ku, wani yană a kan shiriya, kő yana a cikin ɓata bayyananniya."

Ayah  34:25  الأية
قُل لَّا تُسْأَلُونَ عَمَّا أَجْرَمْنَا وَلَا نُسْأَلُ عَمَّا تَعْمَلُونَ
Qul la tus-aloona AAammaajramna wala nus-alu AAamma taAAmaloon

Hausa
 
Ka ce: "Bă ză a tambaye ku ba ga abin da muka aikata daga laifi, kuma bă ză a tambaye mu daga abin da kuke aikatawa ba."

Ayah  34:26  الأية
قُلْ يَجْمَعُ بَيْنَنَا رَبُّنَا ثُمَّ يَفْتَحُ بَيْنَنَا بِالْحَقِّ وَهُوَ الْفَتَّاحُ الْعَلِيمُ
Qul yajmaAAu baynana rabbunathumma yaftahu baynana bilhaqqiwahuwa alfattahu alAAaleem

Hausa
 
Ka ce: "Ubangijinmu zai tăra tsakăninmu, sa'an nan Ya yi hukunci a tsakaninmu da gaskiya. Kuma Shĩ ne Mahukunci, Masani."

Ayah  34:27  الأية
قُلْ أَرُونِيَ الَّذِينَ أَلْحَقْتُم بِهِ شُرَكَاءَ ۖ كَلَّا ۚ بَلْ هُوَ اللهُ الْعَزِيزُ الْحَكِيمُ
Qul arooniya allatheena alhaqtumbihi shurakaa kalla bal huwa AllahualAAazeezu alhakeem

Hausa
 
Ka ce: "Ku nũna mini waɗanda kuka riskar da Shi, su zama abőkan tărayya. Ă'a, Shĩ ne Allah, Mabuwăyi, Mai hikima."

Ayah  34:28  الأية
وَمَا أَرْسَلْنَاكَ إِلَّا كَافَّةً لِّلنَّاسِ بَشِيرًا وَنَذِيرًا وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَ النَّاسِ لَا يَعْلَمُونَ
Wama arsalnaka illa kaffatanlinnasi basheeran wanatheeran walakinnaakthara annasi la yaAAlamoon

Hausa
 
Kuma ba Mu aika ka ba făce zuwa ga mutăne gabă ɗaya, kană mai băyar da bushăra kuma mai gargaɗi, kuma amma mafi yawan mutăne ba su sani ba.

Ayah  34:29  الأية
وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا الْوَعْدُ إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ
Wayaqooloona mata hathaalwaAAdu in kuntum sadiqeen

Hausa
 
Sună cẽwa, "Yaushe ne wannan wa'adi zai auku idan kun kasance măsu gaskiya?"

Ayah  34:30  الأية
قُل لَّكُم مِّيعَادُ يَوْمٍ لَّا تَسْتَأْخِرُونَ عَنْهُ سَاعَةً وَلَا تَسْتَقْدِمُونَ
Qul lakum meeAAadu yawmin latasta/khiroona AAanhu saAAatan wala tastaqdimoon

Hausa
 
Ka ce: "Kună da mi'ădin wani yini wanda bă ku jinkirta daga gare shi kő da sa'a ɗaya, kuma bă ku gabăta."

Ayah  34:31  الأية
وَقَالَ الَّذِينَ كَفَرُوا لَن نُّؤْمِنَ بِهَٰذَا الْقُرْآنِ وَلَا بِالَّذِي بَيْنَ يَدَيْهِ ۗ وَلَوْ تَرَىٰ إِذِ الظَّالِمُونَ مَوْقُوفُونَ عِندَ رَبِّهِمْ يَرْجِعُ بَعْضُهُمْ إِلَىٰ بَعْضٍ الْقَوْلَ يَقُولُ الَّذِينَ اسْتُضْعِفُوا لِلَّذِينَ اسْتَكْبَرُوا لَوْلَا أَنتُمْ لَكُنَّا مُؤْمِنِينَ
Waqala allatheena kafaroo lannu/mina bihatha alqur-ani wala billatheebayna yadayhi walaw tara ithi aththalimoonamawqoofoona AAinda rabbihim yarjiAAu baAAduhum ilabaAAdin alqawla yaqoolu allatheena istudAAifoolillatheena istakbaroo lawla antum lakunnamu/mineen

Hausa
 
Kuma waɗanda suka kăfirta suka ce: "Bă ză mu yi ĩmanida wannan Alƙur'ăni ba, kuma bă ză mu yi ĩmani da abin da yakea gabăninsa ba (na waɗansu littattafan sama)." Kuma dă kă gani a lőkacin da azzălumai suke abin tsayarwa wurin Ubangijinka, sashensu na mayar wa săshe maganar maraunana (mabiya) suke cẽwa makangara (shũgabanni) "Ba dőminku ba, lalle, dă mun kasance mũminai."

Ayah  34:32  الأية
قَالَ الَّذِينَ اسْتَكْبَرُوا لِلَّذِينَ اسْتُضْعِفُوا أَنَحْنُ صَدَدْنَاكُمْ عَنِ الْهُدَىٰ بَعْدَ إِذْ جَاءَكُم ۖ بَلْ كُنتُم مُّجْرِمِينَ
Qala allatheena istakbaroolillatheena istudAAifoo anahnu sadadnakumAAani alhuda baAAda ith jaakum bal kuntummujrimeen

Hausa
 
Makangara suka ce wa maraunana, "Ashe, mũ ne muka kange ku daga shiriya a băyan ya zo muku? Ă,a' kun dai kasance măsu laifi."

Ayah  34:33  الأية
وَقَالَ الَّذِينَ اسْتُضْعِفُوا لِلَّذِينَ اسْتَكْبَرُوا بَلْ مَكْرُ اللَّيْلِ وَالنَّهَارِ إِذْ تَأْمُرُونَنَا أَن نَّكْفُرَ بِاللهِ وَنَجْعَلَ لَهُ أَندَادًا ۚ وَأَسَرُّوا النَّدَامَةَ لَمَّا رَأَوُا الْعَذَابَ وَجَعَلْنَا الْأَغْلَالَ فِي أَعْنَاقِ الَّذِينَ كَفَرُوا ۚ هَلْ يُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كَانُوا يَعْمَلُونَ
Waqala allatheena istudAAifoolillatheena istakbaroo bal makru allayli wannahariith ta/muroonana an nakfura billahiwanajAAala lahu andadan waasarroo annadamatalamma raawoo alAAathaba wajaAAalna al-aghlalafee aAAnaqi allatheena kafaroo hal yujzawna illama kanoo yaAAmaloon

Hausa
 
Kuma maraunana suka ce wa makangara. "Ă'a, (ku tuna) măkircin dare da na răna a lőkacin da kuke umurnin mu da mu kăfirta da Allah, kuma mu sanya Masa abőkan tărayya." Kuma suka assirtar da nadăma a lőkacin da suka ga azăba. Kuma Muka sanya ƙuƙumma a cikin wuyőyin waɗanda suka kăfirta. Lalle, bă ză a yi musu sakamako ba făce da abin da suka kasance sună aikatăwa.

Ayah  34:34  الأية
وَمَا أَرْسَلْنَا فِي قَرْيَةٍ مِّن نَّذِيرٍ إِلَّا قَالَ مُتْرَفُوهَا إِنَّا بِمَا أُرْسِلْتُم بِهِ كَافِرُونَ
Wama arsalna fee qaryatin minnatheerin illa qala mutrafooha innabima orsiltum bihi kafiroon

Hausa
 
Kuma ba mu aika wani mai gargaɗi ba a cikin wata alƙarya făce mani'imtanta (shũgabanni) sunce, "Lalle mũ, măsu kăfirta ne da abin da aka aiko ku da shi."

Ayah  34:35  الأية
وَقَالُوا نَحْنُ أَكْثَرُ أَمْوَالًا وَأَوْلَادًا وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ
Waqaloo nahnu aktharu amwalanwaawladan wama nahnu bimuAAaththabeen

Hausa
 
Kuma suka ce: "Mũ ne mafiya yawa ga dũkiya da ɗiya, kuma mu ba mu zama waɗanda ake yi wa azăba ba."

Ayah  34:36  الأية
قُلْ إِنَّ رَبِّي يَبْسُطُ الرِّزْقَ لِمَن يَشَاءُ وَيَقْدِرُ وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَ النَّاسِ لَا يَعْلَمُونَ
Qul inna rabbee yabsutu arrizqaliman yashao wayaqdiru walakinna akthara annasila yaAAlamoon

Hausa
 
Ka ce: "Lalle, Ubangijĩna Yană shimfiɗa arziki ga wanda Ya so, kuma Yană ƙuntatăwa, kuma amma mafi yawan mutăne ba su sani ba."

Ayah  34:37  الأية
وَمَا أَمْوَالُكُمْ وَلَا أَوْلَادُكُم بِالَّتِي تُقَرِّبُكُمْ عِندَنَا زُلْفَىٰ إِلَّا مَنْ آمَنَ وَعَمِلَ صَالِحًا فَأُولَٰئِكَ لَهُمْ جَزَاءُ الضِّعْفِ بِمَا عَمِلُوا وَهُمْ فِي الْغُرُفَاتِ آمِنُونَ
Wama amwalukum wala awladukumbillatee tuqarribukum AAindana zulfa illaman amana waAAamila salihan faola-ikalahum jazao addiAAfi bima AAamiloowahum fee alghurufati aminoon

Hausa
 
Kuma dũkiyarku ba ta zamo ba, haka ɗiyanku ba su zamo abin da yake kusantar da ku ba a wurinMu, kusantarwar muƙămi făce wanda, ya yi ĩmăni kuma ya aikata aikin ƙwarai. To, waɗannan sună da sakamakon ninkawa sabőda abin da suka aikata. Kuma su amintattu ne a cikin bẽnăye.

Ayah  34:38  الأية
وَالَّذِينَ يَسْعَوْنَ فِي آيَاتِنَا مُعَاجِزِينَ أُولَٰئِكَ فِي الْعَذَابِ مُحْضَرُونَ
Wallatheena yasAAawna fee ayatinamuAAajizeena ola-ika fee alAAathabi muhdaroon

Hausa
 
Kuma waɗanda suke măkirci a cikin ăyőyinMu, sună nẽman gajiyarwa, waɗannan abin halartăwa ne a cikin azăba.

Ayah  34:39  الأية
قُلْ إِنَّ رَبِّي يَبْسُطُ الرِّزْقَ لِمَن يَشَاءُ مِنْ عِبَادِهِ وَيَقْدِرُ لَهُ ۚ وَمَا أَنفَقْتُم مِّن شَيْءٍ فَهُوَ يُخْلِفُهُ ۖ وَهُوَ خَيْرُ الرَّازِقِينَ
Qul inna rabbee yabsutu arrizqaliman yashao min AAibadihi wayaqdiru lahu wamaanfaqtum min shay-in fahuwa yukhlifuhu wahuwa khayru arraziqeen

Hausa
 
Ka ce: "Lalle, Ubangijĩna Yană shimfida arziki ga wanda Ya so daga băyinSa, kuma Yană ƙuntatăwa a gare shi, kuma abin da kuka ciyar daga wani abu, to, Shĩ ne zai musanya shi, kuma Shĩ ne Mafi fĩcin măsu azurtawa."

Ayah  34:40  الأية
وَيَوْمَ يَحْشُرُهُمْ جَمِيعًا ثُمَّ يَقُولُ لِلْمَلَائِكَةِ أَهَٰؤُلَاءِ إِيَّاكُمْ كَانُوا يَعْبُدُونَ
Wayawma yahshuruhum jameeAAan thummayaqoolu lilmala-ikati ahaola-i iyyakumkanoo yaAAbudoon

Hausa
 
Kuma rănar da Allah Ya ke tăra su gabă ɗaya, sa'an nan Ya ce wa Mală'iku, "Shin, waɗannan kũ ne suka kasance sună bauta wa?"

Ayah  34:41  الأية
قَالُوا سُبْحَانَكَ أَنتَ وَلِيُّنَا مِن دُونِهِم ۖ بَلْ كَانُوا يَعْبُدُونَ الْجِنَّ ۖ أَكْثَرُهُم بِهِم مُّؤْمِنُونَ
Qaloo subhanaka anta waliyyunamin doonihim bal kanoo yaAAbudoona aljinna aktharuhumbihim mu/minoon

Hausa
 
Sukace: "Tsarki ya tabbata a gare Ka. Kai ne Majiɓincinmu, bă su ba. Ă'a,sun kasance sună bauta wa aljannu. Mafi yawansu, da sũ suka yi ĩmani."

Ayah  34:42  الأية
فَالْيَوْمَ لَا يَمْلِكُ بَعْضُكُمْ لِبَعْضٍ نَّفْعًا وَلَا ضَرًّا وَنَقُولُ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا ذُوقُوا عَذَابَ النَّارِ الَّتِي كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ
Falyawma la yamliku baAAdukumlibaAAdin nafAAan wala darran wanaqoolulillatheena thalamoo thooqoo AAathabaannari allatee kuntum biha tukaththiboon

Hausa
 
Sabőda haka, a yau săshenku bă ya mallakar wani amfăni ga wani săshen, kuma bă ya mallakar wata cũta, kuma Mună cẽwa ga waɗanda suka yi zalunci, Ku ɗanɗani azabar wută wadda "kuka kasance game da ita, kună ƙaryatăwa."

Ayah  34:43  الأية
وَإِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِمْ آيَاتُنَا بَيِّنَاتٍ قَالُوا مَا هَٰذَا إِلَّا رَجُلٌ يُرِيدُ أَن يَصُدَّكُمْ عَمَّا كَانَ يَعْبُدُ آبَاؤُكُمْ وَقَالُوا مَا هَٰذَا إِلَّا إِفْكٌ مُّفْتَرًى ۚ وَقَالَ الَّذِينَ كَفَرُوا لِلْحَقِّ لَمَّا جَاءَهُمْ إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ
Wa-itha tutla AAalayhim ayatunabayyinatin qaloo ma hatha illarajulun yureedu an yasuddakum AAamma kanayaAAbudu abaokum waqaloo ma hathailla ifkun muftaran waqala allatheenakafaroo lilhaqqi lamma jaahum in hathailla sihrun mubeen

Hausa
 
Kuma idan an karanta ăyőyinMu bayyanannu a kansu, sai su ce: "Wannan bai zama ba făce namiji ne yană son ya kange ku daga abin da ubanninku suka kasance sună bauta wa." Kuma su ce: "Wannan bai zama ba făce ƙiren ƙarya da aka ƙăga." Kuma waɗanda suka kăfirta suka ce: ga gaskiya a lőkacin da ta je musu: "Wannan bă kőme ba făce sihiri ne bayyananne."

Ayah  34:44  الأية
وَمَا آتَيْنَاهُم مِّن كُتُبٍ يَدْرُسُونَهَا ۖ وَمَا أَرْسَلْنَا إِلَيْهِمْ قَبْلَكَ مِن نَّذِيرٍ
Wama ataynahum minkutubin yadrusoonaha wama arsalna ilayhimqablaka min natheer

Hausa
 
Kuma ba Mu bă su waɗansu littattafai ba waɗanda suke karătun su, kuma ba Mu aika wani mai gargaɗi ba zuwa gare su a gabăninka!

Ayah  34:45  الأية
وَكَذَّبَ الَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ وَمَا بَلَغُوا مِعْشَارَ مَا آتَيْنَاهُمْ فَكَذَّبُوا رُسُلِي ۖ فَكَيْفَ كَانَ نَكِيرِ
Wakaththaba allatheena minqablihim wama balaghoo miAAshara ma ataynahumfakaththaboo rusulee fakayfa kana nakeer

Hausa
 
Kuma waɗanda suke a gabăninsu, sun ƙaryata ,alhăli kuwa ba su kai ushurin-ushurin abin da Muka bă su ba, sai suka ƙaryata ManzanniNa! To, yăya musũNa (ga maƙaryata) ya kasance?

Ayah  34:46  الأية
قُلْ إِنَّمَا أَعِظُكُم بِوَاحِدَةٍ ۖ أَن تَقُومُوا لِلَّهِ مَثْنَىٰ وَفُرَادَىٰ ثُمَّ تَتَفَكَّرُوا ۚ مَا بِصَاحِبِكُم مِّن جِنَّةٍ ۚ إِنْ هُوَ إِلَّا نَذِيرٌ لَّكُم بَيْنَ يَدَيْ عَذَابٍ شَدِيدٍ
Qul innama aAAithukumbiwahidatin an taqoomoo lillahi mathna wafuradathumma tatafakkaroo ma bisahibikum min jinnatin inhuwa illa natheerun lakum bayna yaday AAathabinshadeed

Hausa
 
Ka ce: "Ina yi muku wa'azi ne kawai da kalma guda! watau ku tsayu dőmin Allah, bibbiyu da ɗaiɗai, sa'an nan ku yi tunăni, băbu wata hauka ga ma'abũcinku. Shĩ bai zama ba făce mai gargaɗi ne a gare ku a gaba ga wata azăba mai tsanani.

Ayah  34:47  الأية
قُلْ مَا سَأَلْتُكُم مِّنْ أَجْرٍ فَهُوَ لَكُمْ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَى اللهِ ۖ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيْءٍ شَهِيدٌ
Qul ma saaltukum min ajrin fahuwalakum in ajriya illa AAala Allahi wahuwaAAala kulli shay-in shaheed

Hausa
 
Ka ce: "Abin da na rőƙe ku na wani sakamako, to, amfăninsa năku ne. Ijărata ba ta zama ba făce daga Allah, kuma shi Mahalarci ne a kan dukan kőme."

Ayah  34:48  الأية
قُلْ إِنَّ رَبِّي يَقْذِفُ بِالْحَقِّ عَلَّامُ الْغُيُوبِ
Qul inna rabbee yaqthifu bilhaqqiAAallamu alghuyoob

Hausa
 
Ka ce: "Lalle Ubangijina Yană jẽfa gaskiya.(Shi) Masanin abũbuwan fake ne."

Ayah  34:49  الأية
قُلْ جَاءَ الْحَقُّ وَمَا يُبْدِئُ الْبَاطِلُ وَمَا يُعِيدُ
Qul jaa alhaqqu wamayubdi-o albatilu wama yuAAeed

Hausa
 
Ka ce: "Gaskiya ta zo, kuma ƙarya bă ta iya fara (kome) kuma bă ta iya mayarwa."

Ayah  34:50  الأية
قُلْ إِن ضَلَلْتُ فَإِنَّمَا أَضِلُّ عَلَىٰ نَفْسِي ۖ وَإِنِ اهْتَدَيْتُ فَبِمَا يُوحِي إِلَيَّ رَبِّي ۚ إِنَّهُ سَمِيعٌ قَرِيبٌ
Qul in dalaltu fa-innama adilluAAala nafsee wa-ini ihtadaytu fabima yooheeilayya rabbee innahu sameeAAun qareeb

Hausa
 
Ka ce: "Idan na ɓace, to, ină ɓacẽwa ne kawai a kan kaina. Kuma idan na shiryu, to, sabőda abin da Ubangijina Yake yőwar wahayi ne zuwa a gare ni. Lalle Shĩ Mai ji ne, Makusanci."

Ayah  34:51  الأية
وَلَوْ تَرَىٰ إِذْ فَزِعُوا فَلَا فَوْتَ وَأُخِذُوا مِن مَّكَانٍ قَرِيبٍ
Walaw tara ith faziAAoo falafawta waokhithoo min makanin qareeb

Hausa
 
Kuma dă kă gani, a lőkacin da suka firgita, to, băbu kuɓuta, kuma aka kăma su daga wuri makusanci.

Ayah  34:52  الأية
وَقَالُوا آمَنَّا بِهِ وَأَنَّىٰ لَهُمُ التَّنَاوُشُ مِن مَّكَانٍ بَعِيدٍ
Waqaloo amanna bihiwaanna lahumu attanawushu min makaninbaAAeed

Hausa
 
Kuma suka ce: "Mun yi ĩmăni da Shi." To ină ză su sămu kămăwa daga wuri mai nisa?

Ayah  34:53  الأية
وَقَدْ كَفَرُوا بِهِ مِن قَبْلُ ۖ وَيَقْذِفُونَ بِالْغَيْبِ مِن مَّكَانٍ بَعِيدٍ
Waqad kafaroo bihi min qablu wayaqthifoonabilghaybi min makanin baAAeed

Hausa
 
Kuma lalle sun kăfirta da Shi a gabănin haka, kuma sună jĩfa da jăhilci daga wuri mai nĩsa.

Ayah  34:54  الأية
وَحِيلَ بَيْنَهُمْ وَبَيْنَ مَا يَشْتَهُونَ كَمَا فُعِلَ بِأَشْيَاعِهِم مِّن قَبْلُ ۚ إِنَّهُمْ كَانُوا فِي شَكٍّ مُّرِيبٍ
Waheela baynahum wabayna mayashtahoona kama fuAAila bi-ashyaAAihim min qabluinnahum kanoo fee shakkin mureeb

Hausa
 
Kuma an shămakance a tsakăninsu da tsakănin abin da suke marmari, kamar yadda aka aikata da irin ƙungiyőyinsu a gabăninsu. Lalle sũ sun kasance a cikin shakka mai sanya kőkanto.




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us