Prev  

35. Surah Fâtir or Al­Malâ'ikah سورة فاطر

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الْحَمْدُ لِلَّهِ فَاطِرِ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ جَاعِلِ الْمَلَائِكَةِ رُسُلًا أُولِي أَجْنِحَةٍ مَّثْنَىٰ وَثُلَاثَ وَرُبَاعَ ۚ يَزِيدُ فِي الْخَلْقِ مَا يَشَاءُ ۚ إِنَّ اللهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ
Alhamdu lillahi fatiri assamawatiwal-ardi jaAAili almala-ikatirusulan olee ajnihatin mathna wathulathawarubaAAa yazeedu fee alkhalqi ma yashaoinna Allaha AAala kulli shay-in qadeer

Hausa
 
Gődiya ta tabbata ga Allah, Mai făra halittar sammai da ƙasă, Mai sanya mală'iku manzanni măsu fukăfukai, bibbiyu, da uku-uku da hurhuɗu. Yană ƙărăwar abin da Ya ke so a cikin halittar. Lalle Allah Mai ĩkon yi ne a kan kőme.

Ayah  35:2  الأية
مَّا يَفْتَحِ اللهُ لِلنَّاسِ مِن رَّحْمَةٍ فَلَا مُمْسِكَ لَهَا ۖ وَمَا يُمْسِكْ فَلَا مُرْسِلَ لَهُ مِن بَعْدِهِ ۚ وَهُوَ الْعَزِيزُ الْحَكِيمُ
Ma yaftahi Allahu linnasimin rahmatin fala mumsika laha wamayumsik fala mursila lahu min baAAdihi wahuwa alAAazeezu alhakeem

Hausa
 
Abin da Allah Ya buɗa wa mutăne daga rahama, to, băbu mai riƙewa a gare shi, kuma abin da Ya riƙe, to, băbu mai saki a gare shi, waninSa, kuma Shĩ ne Mabuwăyi, Mai hikima.

Ayah  35:3  الأية
يَا أَيُّهَا النَّاسُ اذْكُرُوا نِعْمَتَ اللهِ عَلَيْكُمْ ۚ هَلْ مِنْ خَالِقٍ غَيْرُ اللهِ يَرْزُقُكُم مِّنَ السَّمَاءِ وَالْأَرْضِ ۚ لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ ۖ فَأَنَّىٰ تُؤْفَكُونَ
Ya ayyuha annasuothkuroo niAAmata Allahi AAalaykum hal min khaliqinghayru Allahi yarzuqukum mina assama-i wal-ardila ilaha illa huwa faanna tu/fakoon

Hausa
 
Yă kũ mutăne! Ku tuna ni'imar Allah a kanku. Shin, akwai wani mai halitta wanin Allah da zai azurta ku daga sama da, ƙasă? Băbu wani abin bautăwa, făce Shi. To, yăya ake karkatar da ku?

Ayah  35:4  الأية
وَإِن يُكَذِّبُوكَ فَقَدْ كُذِّبَتْ رُسُلٌ مِّن قَبْلِكَ ۚ وَإِلَى اللهِ تُرْجَعُ الْأُمُورُ
Wa-in yukaththibooka faqad kuththibatrusulun min qablika wa-ila Allahi turjaAAu al-omoor

Hausa
 
Kuma idan sun ƙaryata ka, to, lalle, an ƙaryata waɗansu Manzanni a gabăninka, kuma zuwa ga Allah ake mayar da al'amura.

Ayah  35:5  الأية
يَا أَيُّهَا النَّاسُ إِنَّ وَعْدَ اللهِ حَقٌّ ۖ فَلَا تَغُرَّنَّكُمُ الْحَيَاةُ الدُّنْيَا ۖ وَلَا يَغُرَّنَّكُم بِاللهِ الْغَرُورُ
Ya ayyuha annasuinna waAAda Allahi haqqun falataghurrannakumu alhayatu addunya walayaghurrannakum billahi algharoor

Hausa
 
Yă kũ mutăne! Lalle wa'adin Allah gaskiya ne, sabőda haka kada răyuwar dũniya ta rũɗar da ku, kuma kada marũɗi ya rũɗe ku game da Allah.

Ayah  35:6  الأية
إِنَّ الشَّيْطَانَ لَكُمْ عَدُوٌّ فَاتَّخِذُوهُ عَدُوًّا ۚ إِنَّمَا يَدْعُو حِزْبَهُ لِيَكُونُوا مِنْ أَصْحَابِ السَّعِيرِ
Inna ashshaytana lakumAAaduwwun fattakhithoohu AAaduwwan innamayadAAoo hizbahu liyakoonoo min as-habi assaAAeer

Hausa
 
Lalle Shaiɗan maƙiyi ne a gare ku, sai ku riƙe shi maƙiyi. Yană kiran ƙungiyarsa kawai ne, dőmin su kasance 'yan sa'ir.

Ayah  35:7  الأية
الَّذِينَ كَفَرُوا لَهُمْ عَذَابٌ شَدِيدٌ ۖ وَالَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُم مَّغْفِرَةٌ وَأَجْرٌ كَبِيرٌ
Allatheena kafaroo lahum AAathabunshadeedun wallatheena amanoo waAAamiloo assalihatilahum maghfiratun waajrun kabeer

Hausa
 
Waɗanda suka kăfirta suna da azăba mai tsanani kuma waɗanda suka yi ĩmăni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sună da wata găfara da sakamako mai girma.

Ayah  35:8  الأية
أَفَمَن زُيِّنَ لَهُ سُوءُ عَمَلِهِ فَرَآهُ حَسَنًا ۖ فَإِنَّ اللهَ يُضِلُّ مَن يَشَاءُ وَيَهْدِي مَن يَشَاءُ ۖ فَلَا تَذْهَبْ نَفْسُكَ عَلَيْهِمْ حَسَرَاتٍ ۚ إِنَّ اللهَ عَلِيمٌ بِمَا يَصْنَعُونَ
Afaman zuyyina lahu soo-o AAamalihi faraahuhasanan fa-inna Allaha yudillu man yashaowayahdee man yashao fala tathhab nafsukaAAalayhim hasaratin inna Allaha AAaleemunbima yasnaAAoon

Hausa
 
Shin to, wanda aka ƙawăta masa aikinsa, har ya gan shi mai kyau (yană daidai da waninsa)? Sabőda haka, lalle, Allah Yană ɓatar da wanda Yake so, kuma Yană shiryar da wanda Yake so, sabőda haka kada ranka ya halaka a kansu dômin baƙin ciki. Lalle Allah Masani ne ga abin da suke sană'antawa.

Ayah  35:9  الأية
وَاللهُ الَّذِي أَرْسَلَ الرِّيَاحَ فَتُثِيرُ سَحَابًا فَسُقْنَاهُ إِلَىٰ بَلَدٍ مَّيِّتٍ فَأَحْيَيْنَا بِهِ الْأَرْضَ بَعْدَ مَوْتِهَا ۚ كَذَٰلِكَ النُّشُورُ
Wallahu allathee arsalaarriyaha fatutheeru sahaban fasuqnahuila baladin mayyitin faahyayna bihi al-ardabaAAda mawtiha kathalika annushoor

Hausa
 
Kuma Allah ne Ya aika da iskőki har su mőtsar da girgije, sa'an nan Mu kőra shi zuwa ga gari matacce, sa'an nan Mu răyar da ƙasă game da shi a bayan mutuwarta. Kamar wancan ne Tăshin ˇiyăma yake.

Ayah  35:10  الأية
مَن كَانَ يُرِيدُ الْعِزَّةَ فَلِلَّهِ الْعِزَّةُ جَمِيعًا ۚ إِلَيْهِ يَصْعَدُ الْكَلِمُ الطَّيِّبُ وَالْعَمَلُ الصَّالِحُ يَرْفَعُهُ ۚ وَالَّذِينَ يَمْكُرُونَ السَّيِّئَاتِ لَهُمْ عَذَابٌ شَدِيدٌ ۖ وَمَكْرُ أُولَٰئِكَ هُوَ يَبُورُ
Man kana yureedu alAAizzata falillahialAAizzatu jameeAAan ilayhi yasAAadu alkalimu attayyibuwalAAamalu assalihu yarfaAAuhu wallatheenayamkuroona assayyi-ati lahum AAathabunshadeedun wamakru ola-ika huwa yaboor

Hausa
 
Wanda ya kasance yană nẽman wata izza, to, Allah ne da izza gabă ɗaya. zuwa gare Shi magana mai dăɗi ke hawa, kuma aiki na ƙwarai Yană ɗaukar ta Kuma waɗanda ke yin măkircin mũnanan ayyuka, sună da wata azăba mai tsanani, kuma măkircin waɗannan yană yin tasgaro.

Ayah  35:11  الأية
وَاللهُ خَلَقَكُم مِّن تُرَابٍ ثُمَّ مِن نُّطْفَةٍ ثُمَّ جَعَلَكُمْ أَزْوَاجًا ۚ وَمَا تَحْمِلُ مِنْ أُنثَىٰ وَلَا تَضَعُ إِلَّا بِعِلْمِهِ ۚ وَمَا يُعَمَّرُ مِن مُّعَمَّرٍ وَلَا يُنقَصُ مِنْ عُمُرِهِ إِلَّا فِي كِتَابٍ ۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى اللهِ يَسِيرٌ
Wallahu khalaqakum min turabinthumma min nutfatin thumma jaAAalakum azwajan wamatahmilu min ontha wala tadaAAu illabiAAilmihi wama yuAAammaru min muAAammarin walayunqasu min AAumurihi illa fee kitabin inna thalikaAAala Allahi yaseer

Hausa
 
Kuma Allah ne Ya halitta ku daga turɓăya, sa'an nan daga ɗigon maniyyi, sa'an nan Ya sanya ku surkin maza da mătă. Kuma wata mace bă ta yin ciki, kuma bă ta haihuwa, făce da saninSa, kuma bă ză a răyar da wanda ake răyarwa ba, kuma bă ză a rage tsawon ransa ba făce yană a cikin Littăfi. Lalle, wancan mai sauki ne ga Allah.

Ayah  35:12  الأية
وَمَا يَسْتَوِي الْبَحْرَانِ هَٰذَا عَذْبٌ فُرَاتٌ سَائِغٌ شَرَابُهُ وَهَٰذَا مِلْحٌ أُجَاجٌ ۖ وَمِن كُلٍّ تَأْكُلُونَ لَحْمًا طَرِيًّا وَتَسْتَخْرِجُونَ حِلْيَةً تَلْبَسُونَهَا ۖ وَتَرَى الْفُلْكَ فِيهِ مَوَاخِرَ لِتَبْتَغُوا مِن فَضْلِهِ وَلَعَلَّكُمْ تَشْكُرُونَ
Wama yastawee albahranihatha AAathbun furatun sa-ighun sharabuhuwahatha milhun ojajun wamin kullinta/kuloona lahman tariyyan watastakhrijoona hilyatantalbasoonaha watara alfulka feehi mawakhiralitabtaghoo min fadlihi walaAAallakum tashkuroon

Hausa
 
Kuma kőguna biyu ba su daidaita: Wannan mai ruwan dăɗi, mai zăƙi, mai sauƙin haɗiya kuma wannan mai ruwan gishiri mai zartsi, kuma daga kőwane, kună cin wani nama săbo, kuma kună fitar da kawa wadda kuke tufantarta, kuma kană ganin jirăge a cikinsa sună măsu gudăna, dőmin ku nẽmo daga falalarSa, kuma ɗammăninku ză ku dinga gődẽwa.

Ayah  35:13  الأية
يُولِجُ اللَّيْلَ فِي النَّهَارِ وَيُولِجُ النَّهَارَ فِي اللَّيْلِ وَسَخَّرَ الشَّمْسَ وَالْقَمَرَ كُلٌّ يَجْرِي لِأَجَلٍ مُّسَمًّى ۚ ذَٰلِكُمُ اللهُ رَبُّكُمْ لَهُ الْمُلْكُ ۚ وَالَّذِينَ تَدْعُونَ مِن دُونِهِ مَا يَمْلِكُونَ مِن قِطْمِيرٍ
Yooliju allayla fee annahariwayooliju annahara fee allayli wasakhkhara ashshamsawalqamara kullun yajree li-ajalin musamman thalikumuAllahu rabbukum lahu almulku wallatheenatadAAoona min doonihi ma yamlikoona min qitmeer

Hausa
 
Yană shigar da dare a cikin răna, kuma Yană shigar da răna a cikin dare. Kuma Ya hőre rănă da wată kőwannensu yană gudăna zuwa ga ajali ambatacce Wannan Shĩ ne Allah, Ubangijinku, gare Shi mulki yake, kuma waɗanda kuke kira waninSa bă su mallakar kő fătar gurtsun dabĩno.

Ayah  35:14  الأية
إِن تَدْعُوهُمْ لَا يَسْمَعُوا دُعَاءَكُمْ وَلَوْ سَمِعُوا مَا اسْتَجَابُوا لَكُمْ ۖ وَيَوْمَ الْقِيَامَةِ يَكْفُرُونَ بِشِرْكِكُمْ ۚ وَلَا يُنَبِّئُكَ مِثْلُ خَبِيرٍ
In tadAAoohum la yasmaAAoo duAAaakumwalaw samiAAoo ma istajaboo lakum wayawma alqiyamatiyakfuroona bishirkikum wala yunabbi-oka mithlu khabeer

Hausa
 
Idan kun kira su, bă ză su ji kiranku ba, kuma kő sun jiya, bă ză su karɓa muku ba, kuma a Rănar ˇiyăma ză su kăfirce wa shirkinku, kuma băbu mai bă ka lăbări, kamar wanda ya sani.

Ayah  35:15  الأية
يَا أَيُّهَا النَّاسُ أَنتُمُ الْفُقَرَاءُ إِلَى اللهِ ۖ وَاللهُ هُوَ الْغَنِيُّ الْحَمِيدُ
Ya ayyuha annasuantumu alfuqarao ila Allahi wallahuhuwa alghaniyyu alhameed

Hausa
 
Yă kũ mutăne! Kũ ne măsu bukăta zuwa ga Allah, kuma Allah, Shĩ ne Mawadăci, Gődadde.

Ayah  35:16  الأية
إِن يَشَأْ يُذْهِبْكُمْ وَيَأْتِ بِخَلْقٍ جَدِيدٍ
In yasha/ yuthhibkum waya/tibikhalqin jadeed

Hausa
 
Idan Ya so, zai tafi da ku, kuma Ya zo da wata halitta săbuwa.

Ayah  35:17  الأية
وَمَا ذَٰلِكَ عَلَى اللهِ بِعَزِيزٍ
Wama thalika AAala AllahibiAAazeez

Hausa
 
Kuma wancan bai zama mabuwăyi ba ga Allah.

Ayah  35:18  الأية
وَلَا تَزِرُ وَازِرَةٌ وِزْرَ أُخْرَىٰ ۚ وَإِن تَدْعُ مُثْقَلَةٌ إِلَىٰ حِمْلِهَا لَا يُحْمَلْ مِنْهُ شَيْءٌ وَلَوْ كَانَ ذَا قُرْبَىٰ ۗ إِنَّمَا تُنذِرُ الَّذِينَ يَخْشَوْنَ رَبَّهُم بِالْغَيْبِ وَأَقَامُوا الصَّلَاةَ ۚ وَمَن تَزَكَّىٰ فَإِنَّمَا يَتَزَكَّىٰ لِنَفْسِهِ ۚ وَإِلَى اللهِ الْمَصِيرُ
Wala taziru waziratun wizraokhra wa-in tadAAu muthqalatun ila himlihala yuhmal minhu shay-on walaw kana thaqurba innama tunthiru allatheenayakhshawna rabbahum bilghaybi waaqamoo assalatawaman tazakka fa-innama yatazakka linafsihiwa-ila Allahi almaseer

Hausa
 
Kuma wani rai mai ɗaukar nauyi, bai ɗaukar nauyin wani rai. Kuma idan ran da aka nauyaya wa kăya ya yi kira (ga wani mataimaki) zuwa ga kăyansa, bă ză a dauki kőme ba daga gare shi, kuma kő dă (wanda ake kiran) yă kasance makusancin zumunta ne. Kană gargaɗi kawai ne ga waɗanda ke tsoron Ubangijinsu a fake, kuma suka tsayar da salla. Kuma wanda ya tsarkake, to, yană tsarkaka ne dőmin kansa. Kuma zuwa ga Allah kawai makőma take.

Ayah  35:19  الأية
وَمَا يَسْتَوِي الْأَعْمَىٰ وَالْبَصِيرُ
Wama yastawee al-aAAma walbaseer

Hausa
 
Kuma makăho bă ya daidaita da mai gani.

Ayah  35:20  الأية
وَلَا الظُّلُمَاتُ وَلَا النُّورُ
Wala aththulumatuwala annoor

Hausa
 
Kuma duffai bă su daidaita, kuma haske bă ya daidaita.

Ayah  35:21  الأية
وَلَا الظِّلُّ وَلَا الْحَرُورُ
Wala aththilluwala alharoor

Hausa
 
Kuma inuwa bă ta daidaita, kuma iskar zăfi bă ta daidaita.

Ayah  35:22  الأية
وَمَا يَسْتَوِي الْأَحْيَاءُ وَلَا الْأَمْوَاتُ ۚ إِنَّ اللهَ يُسْمِعُ مَن يَشَاءُ ۖ وَمَا أَنتَ بِمُسْمِعٍ مَّن فِي الْقُبُورِ
Wama yastawee al-ahyaowala al-amwatu inna Allaha yusmiAAu man yashaowama anta bimusmiAAin man fee alquboor

Hausa
 
Kuma răyayyu bă su daidaita kuma matattu ba su daidaita. Lalle Allah Yană jiyar da wa'azi ga wanda Ya so, kuma ba ka jiyar da waɗanda suke a cikin kaburbura.

Ayah  35:23  الأية
إِنْ أَنتَ إِلَّا نَذِيرٌ
In anta illa natheer

Hausa
 
Ba ka zama ba făce mai gargaɗi kawai.

Ayah  35:24  الأية
إِنَّا أَرْسَلْنَاكَ بِالْحَقِّ بَشِيرًا وَنَذِيرًا ۚ وَإِن مِّنْ أُمَّةٍ إِلَّا خَلَا فِيهَا نَذِيرٌ
Inna arsalnaka bilhaqqibasheeran wanatheeran wa-in min ommatin illa khalafeeha natheer

Hausa
 
Lalle Mũ Mun aike ka da gaskiya, kană mai băyar da bushăra kuma mai gargaɗi. Kuma băbu wata al'umma făce wani mai gargaɗi yă shũɗe a cikinta.

Ayah  35:25  الأية
وَإِن يُكَذِّبُوكَ فَقَدْ كَذَّبَ الَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ جَاءَتْهُمْ رُسُلُهُم بِالْبَيِّنَاتِ وَبِالزُّبُرِ وَبِالْكِتَابِ الْمُنِيرِ
Wa-in yukaththibooka faqad kaththabaallatheena min qablihim jaat-hum rusuluhum bilbayyinatiwabizzuburi wabilkitabi almuneer

Hausa
 
Kuma idan sună ƙaryata ka, to, haƙĩƙa, waɗanda suke a gabăninsu sun ƙaryata. Manzanninsu sun jẽ musu da hujjőji, kuma da takardu, kuma da Littafi mai haske.

Ayah  35:26  الأية
ثُمَّ أَخَذْتُ الَّذِينَ كَفَرُوا ۖ فَكَيْفَ كَانَ نَكِيرِ
Thumma akhathtu allatheenakafaroo fakayfa kana nakeer

Hausa
 
Sa'an nan Na kăma waɗanda suka kăfirta. To, yăya musũNa yake?

Ayah  35:27  الأية
أَلَمْ تَرَ أَنَّ اللهَ أَنزَلَ مِنَ السَّمَاءِ مَاءً فَأَخْرَجْنَا بِهِ ثَمَرَاتٍ مُّخْتَلِفًا أَلْوَانُهَا ۚ وَمِنَ الْجِبَالِ جُدَدٌ بِيضٌ وَحُمْرٌ مُّخْتَلِفٌ أَلْوَانُهَا وَغَرَابِيبُ سُودٌ
Alam tara anna Allaha anzala mina assama-imaan faakhrajna bihi thamaratin mukhtalifanalwanuha wamina aljibali judadun beedunwahumrun mukhtalifun alwanuha wagharabeebusood

Hausa
 
Ba ka gani ba, lalle Allah Ya saukar da ruwa daga sama? Sai Muka fitar, game da shi,'yă'yan ităce măsu săɓanin launuka kuma daga duwatsu akwai zane-zane, farfaru da jăjăye, măsu săɓanin launin, da măsu launin baƙin ƙarfe, baƙăƙe.

Ayah  35:28  الأية
وَمِنَ النَّاسِ وَالدَّوَابِّ وَالْأَنْعَامِ مُخْتَلِفٌ أَلْوَانُهُ كَذَٰلِكَ ۗ إِنَّمَا يَخْشَى اللهَ مِنْ عِبَادِهِ الْعُلَمَاءُ ۗ إِنَّ اللهَ عَزِيزٌ غَفُورٌ
Wamina annasi waddawabbiwal-anAAami mukhtalifun alwanuhu kathalikainnama yakhsha Allaha min AAibadihialAAulamao inna Allaha AAazeezun ghafoor

Hausa
 
Kuma daga mutăne da dabbőbi da bisăshen gida, măsu săɓănin launinsu kamar wancan. Malamai kawai ke tsőron Allah daga cikin băyinSa. Lalle, Allah, Mabuwăyi ne, Mai găfara.

Ayah  35:29  الأية
إِنَّ الَّذِينَ يَتْلُونَ كِتَابَ اللهِ وَأَقَامُوا الصَّلَاةَ وَأَنفَقُوا مِمَّا رَزَقْنَاهُمْ سِرًّا وَعَلَانِيَةً يَرْجُونَ تِجَارَةً لَّن تَبُورَ
Inna allatheena yatloona kitabaAllahi waaqamoo assalatawaanfaqoo mimma razaqnahum sirran waAAalaniyatanyarjoona tijaratan lan taboor

Hausa
 
Lalle waɗanda ke karătun Littăfin Allah kuma suka tsayar da salla, kuma suka ciyar daga abin da Muka azurta su da shi, a asirce da bayyane, sună fătan (sămun) wani fatauci ne wanda bă ya yin tasgaro.

Ayah  35:30  الأية
لِيُوَفِّيَهُمْ أُجُورَهُمْ وَيَزِيدَهُم مِّن فَضْلِهِ ۚ إِنَّهُ غَفُورٌ شَكُورٌ
Liyuwaffiyahum ojoorahum wayazeedahum min fadlihiinnahu ghafoorun shakoor

Hausa
 
Dőmin (Allah) zai cika musu sakamakonsu, kuma Ya ƙară musu daga falalarSa. Lalle Shi Mai găfara ne, Mai gődiya.

Ayah  35:31  الأية
وَالَّذِي أَوْحَيْنَا إِلَيْكَ مِنَ الْكِتَابِ هُوَ الْحَقُّ مُصَدِّقًا لِّمَا بَيْنَ يَدَيْهِ ۗ إِنَّ اللهَ بِعِبَادِهِ لَخَبِيرٌ بَصِيرٌ
Wallathee awhaynailayka mina alkitabi huwa alhaqqu musaddiqanlima bayna yadayhi inna Allaha biAAibadihilakhabeerun baseer

Hausa
 
Kuma abin da Muka yi wahayi zuwa gare ka, daga Littăfi,

Ayah  35:32  الأية
ثُمَّ أَوْرَثْنَا الْكِتَابَ الَّذِينَ اصْطَفَيْنَا مِنْ عِبَادِنَا ۖ فَمِنْهُمْ ظَالِمٌ لِّنَفْسِهِ وَمِنْهُم مُّقْتَصِدٌ وَمِنْهُمْ سَابِقٌ بِالْخَيْرَاتِ بِإِذْنِ اللهِ ۚ ذَٰلِكَ هُوَ الْفَضْلُ الْكَبِيرُ
Thumma awrathna alkitaba allatheenaistafayna min AAibadina faminhum thalimunlinafsihi waminhum muqtasidun waminhum sabiqun bilkhayratibi-ithni Allahi thalika huwa alfadlualkabeer

Hausa
 
Sa'an nan Mun gădar da Littăfin, ga waɗanda Muka zăɓa daga băyinMu, sa'an nan daga cikinsu, akwai mai zălunci ga kansa, kuma daga cikinsu akwai mai tsakaităwa, kuma daga cikinsu akwai mai tsẽrẽwa da ayyukan alhẽri da iznin Allah. Waccan ita ce falalar (Allah) mai girma.

Ayah  35:33  الأية
جَنَّاتُ عَدْنٍ يَدْخُلُونَهَا يُحَلَّوْنَ فِيهَا مِنْ أَسَاوِرَ مِن ذَهَبٍ وَلُؤْلُؤًا ۖ وَلِبَاسُهُمْ فِيهَا حَرِيرٌ
Jannatu AAadnin yadkhuloonahayuhallawna feeha min asawira min thahabinwalu/lu-an walibasuhum feeha hareer

Hausa
 
Gidăjen Aljannar zamă sună shigar su. Ană ƙawăce su a cikinsu, da ƙawă ta mundăye daga zĩnăriya da lu'ulu'u, kuma tufăfinsu, a cikinsu alharĩni ne.

Ayah  35:34  الأية
وَقَالُوا الْحَمْدُ لِلَّهِ الَّذِي أَذْهَبَ عَنَّا الْحَزَنَ ۖ إِنَّ رَبَّنَا لَغَفُورٌ شَكُورٌ
Waqaloo alhamdu lillahiallathee athhaba AAanna alhazana innarabbana laghafoorun shakoor

Hausa
 
Kuma suka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah Wanda Ya tafiyar da baƙin ciki daga gare mu. Lalle Ubangijinmu, haƙĩƙa Mai gafarane, Mai godiya."

Ayah  35:35  الأية
الَّذِي أَحَلَّنَا دَارَ الْمُقَامَةِ مِن فَضْلِهِ لَا يَمَسُّنَا فِيهَا نَصَبٌ وَلَا يَمَسُّنَا فِيهَا لُغُوبٌ
Allathee ahallana daraalmuqamati min fadlihi la yamassunafeeha nasabun wala yamassuna feehalughoob

Hausa
 
"Wanda Ya saukar da mu a gidan zamă, daga falalarSa, wata wahala bă ta shăfar mu a cikinsa, kuma wata kăsăwa bă ta shăfar mu a cikinsa."

Ayah  35:36  الأية
وَالَّذِينَ كَفَرُوا لَهُمْ نَارُ جَهَنَّمَ لَا يُقْضَىٰ عَلَيْهِمْ فَيَمُوتُوا وَلَا يُخَفَّفُ عَنْهُم مِّنْ عَذَابِهَا ۚ كَذَٰلِكَ نَجْزِي كُلَّ كَفُورٍ
Wallatheena kafaroo lahum narujahannama la yuqda AAalayhim fayamootoo walayukhaffafu AAanhum min AAathabiha kathalikanajzee kulla kafoor

Hausa
 
Kuma waɗanda suka kăfirta sună da wutar Jahannama, bă a yin hukunci a kansu balle su mutu kuma bă a sauƙaƙa musu daga azăbarta. Kamar haka Muke săka wa kőwane mai yawan kăfirci.

Ayah  35:37  الأية
وَهُمْ يَصْطَرِخُونَ فِيهَا رَبَّنَا أَخْرِجْنَا نَعْمَلْ صَالِحًا غَيْرَ الَّذِي كُنَّا نَعْمَلُ ۚ أَوَلَمْ نُعَمِّرْكُم مَّا يَتَذَكَّرُ فِيهِ مَن تَذَكَّرَ وَجَاءَكُمُ النَّذِيرُ ۖ فَذُوقُوا فَمَا لِلظَّالِمِينَ مِن نَّصِيرٍ
Wahum yastarikhoona feeharabbana akhrijna naAAmal salihanghayra allathee kunna naAAmalu awa lam nuAAammirkumma yatathakkaru feehi man tathakkara wajaakumuannatheeru fathooqoo fama liththalimeenamin naseer

Hausa
 
Kuma sũ, sună hargőwar nẽman ăgaji a cikinta. (Sună cẽwa) "Yă Ubangijinmu! Ka fitar da mu, mu aikata aiki mai kyau, wanin wanda muka kasance mună aikatăwa." Ashe, kuma, ba Mu răyar da ku ba, abin da mai tunăni zai iya yin tunăni a ciki, kuma mai gargaɗi yă jẽ muku? To, ku ɗanɗana, sabőda haka băbu wani mataimaki, ga azzălumai.

Ayah  35:38  الأية
إِنَّ اللهَ عَالِمُ غَيْبِ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ إِنَّهُ عَلِيمٌ بِذَاتِ الصُّدُورِ
Inna Allaha AAalimu ghaybi assamawatiwal-ardi innahu AAaleemun bithati assudoor

Hausa
 
Lalle Allah ne Masanin gaibin sammai da ƙasă. Lalle Shĩ ne Masani ga abin da yake ainihin zukata.

Ayah  35:39  الأية
هُوَ الَّذِي جَعَلَكُمْ خَلَائِفَ فِي الْأَرْضِ ۚ فَمَن كَفَرَ فَعَلَيْهِ كُفْرُهُ ۖ وَلَا يَزِيدُ الْكَافِرِينَ كُفْرُهُمْ عِندَ رَبِّهِمْ إِلَّا مَقْتًا ۖ وَلَا يَزِيدُ الْكَافِرِينَ كُفْرُهُمْ إِلَّا خَسَارًا
Huwa allathee jaAAalakum khala-ifafee al-ardi faman kafara faAAalayhi kufruhu walayazeedu alkafireena kufruhum AAinda rabbihim illamaqtan wala yazeedu alkafireena kufruhum illakhasara

Hausa
 
Shĩ ne Wanda Ya sanya ku măsu maye wa jună, a cikin ƙasă. To, wanda ya kăfirta, to, kăfircinsa yană a kansa. Kuma kăfircin kăfirai bă ya kăra musu kőme făce baƙin jini, kuma kăfircin kăfirai bă ya kăra musu kőme face hasăra.

Ayah  35:40  الأية
قُلْ أَرَأَيْتُمْ شُرَكَاءَكُمُ الَّذِينَ تَدْعُونَ مِن دُونِ اللهِ أَرُونِي مَاذَا خَلَقُوا مِنَ الْأَرْضِ أَمْ لَهُمْ شِرْكٌ فِي السَّمَاوَاتِ أَمْ آتَيْنَاهُمْ كِتَابًا فَهُمْ عَلَىٰ بَيِّنَتٍ مِّنْهُ ۚ بَلْ إِن يَعِدُ الظَّالِمُونَ بَعْضُهُم بَعْضًا إِلَّا غُرُورًا
Qul araaytum shurakaakumu allatheenatadAAoona min dooni Allahi aroonee matha khalaqoomina al-ardi am lahum shirkun fee assamawatiam ataynahum kitaban fahum AAalabayyinatin minhu bal in yaAAidu aththalimoonabaAAduhum baAAdan illa ghuroora

Hausa
 
Ka ce: "Shin, kun ga abũbuwan shirkinku, waɗanda kuke kira, wasun Allah? Ku nũna mini, mẽne ne suka halitta daga ƙasă? Kő sună da tărayya ne a cikin sammai? Kő kuma Mun bă su wani littăfi ne sabőda haka sună a kan wata hujja ce daga gare shi? Ă'a, azzălumai bă su yin wani wa'adi, săshensu zuwa ga săshe, făce rũɗi."

Ayah  35:41  الأية
إِنَّ اللهَ يُمْسِكُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ أَن تَزُولَا ۚ وَلَئِن زَالَتَا إِنْ أَمْسَكَهُمَا مِنْ أَحَدٍ مِّن بَعْدِهِ ۚ إِنَّهُ كَانَ حَلِيمًا غَفُورًا
Inna Allaha yumsiku assamawatiwal-arda an tazoola wala-in zalatain amsakahuma min ahadin min baAAdihi innahu kanahaleeman ghafoora

Hausa
 
Lalle Allah Yană riƙe sammai da ƙasă dőmin kada su gushe. Kuma haƙĩƙa, idan sun gushe, băbu wani baicinSa da zai riƙe su. Lalle Shi Yă kasance Mai haƙuri, Mai găfara.

Ayah  35:42  الأية
وَأَقْسَمُوا بِاللهِ جَهْدَ أَيْمَانِهِمْ لَئِن جَاءَهُمْ نَذِيرٌ لَّيَكُونُنَّ أَهْدَىٰ مِنْ إِحْدَى الْأُمَمِ ۖ فَلَمَّا جَاءَهُمْ نَذِيرٌ مَّا زَادَهُمْ إِلَّا نُفُورًا
Waaqsamoo billahi jahda aymanihimla-in jaahum natheerun layakoonunna ahda minihda al-omami falamma jaahum natheerunma zadahum illa nufoora

Hausa
 
Kuma suka yi rantsuwa da Allah, mafi nauyin rantsuwarsu, "Lalle, idan wani mai gargaɗi ya zo musu tabbas ză su kasance mafi shiryuwa, daga ɗayan al'ummőmi." To, a lőkacin da mai gargaɗi ya jẽ musu, bai ƙară su da kőme ba făce gudu.

Ayah  35:43  الأية
اسْتِكْبَارًا فِي الْأَرْضِ وَمَكْرَ السَّيِّئِ ۚ وَلَا يَحِيقُ الْمَكْرُ السَّيِّئُ إِلَّا بِأَهْلِهِ ۚ فَهَلْ يَنظُرُونَ إِلَّا سُنَّتَ الْأَوَّلِينَ ۚ فَلَن تَجِدَ لِسُنَّتِ اللهِ تَبْدِيلًا ۖ وَلَن تَجِدَ لِسُنَّتِ اللهِ تَحْوِيلًا
Istikbaran fee al-ardi wamakraassayyi-i wala yaheequ almakru assayyi-oilla bi-ahlihi fahal yanthuroona illasunnata al-awwaleena falan tajida lisunnati Allahitabdeelan walan tajida lisunnati Allahi tahweela

Hausa
 
Dőmin nũna girman kai a cikin ƙasă da măkircin cũta. Kuma măkirci na cũta bă ya fădăwa făce a kan mutănensa. To shin sună jiran (wani abu ne) făce dai hanyar (kăfiran) farko. To, bă ză ka sămi musanya ba ga hanyar Allah. Kuma bă ză ka sămi jũyarwa ba ga hanyar Allah.

Ayah  35:44  الأية
أَوَلَمْ يَسِيرُوا فِي الْأَرْضِ فَيَنظُرُوا كَيْفَ كَانَ عَاقِبَةُ الَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ وَكَانُوا أَشَدَّ مِنْهُمْ قُوَّةً ۚ وَمَا كَانَ اللهُ لِيُعْجِزَهُ مِن شَيْءٍ فِي السَّمَاوَاتِ وَلَا فِي الْأَرْضِ ۚ إِنَّهُ كَانَ عَلِيمًا قَدِيرًا
Awa lam yaseeroo fee al-ardi fayanthurookayfa kana AAaqibatu allatheena min qablihimwakanoo ashadda minhum quwwatan wama kanaAllahu liyuAAjizahu min shay-in fee assamawatiwala fee al-ardi innahu kana AAaleemanqadeera

Hausa
 
Ashe, kuma ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasă, dőmin su dũba yadda ăƙibar waɗannan da suke a gabăninsu ta kasance? Alhăli kuwa sun kasance mafĩfĩta ƙarfi daga gare su? Kuma Allah bai kasance wani abu nă iya rinjăyarSa ba, a cikin sammai, kuma haka a cikin kaƙă. Lalle Shi ne Ya kasance Masani, Mai ĩkon yi.

Ayah  35:45  الأية
وَلَوْ يُؤَاخِذُ اللهُ النَّاسَ بِمَا كَسَبُوا مَا تَرَكَ عَلَىٰ ظَهْرِهَا مِن دَابَّةٍ وَلَٰكِن يُؤَخِّرُهُمْ إِلَىٰ أَجَلٍ مُّسَمًّى ۖ فَإِذَا جَاءَ أَجَلُهُمْ فَإِنَّ اللهَ كَانَ بِعِبَادِهِ بَصِيرًا
Walaw yu-akhithu Allahuannasa bima kasaboo ma taraka AAalathahriha min dabbatin walakinyu-akhkhiruhum ila ajalin musamman fa-itha jaaajaluhum fa-inna Allaha kana biAAibadihi baseera

Hausa
 
Kuma dă Allah Yană kăma mutăne sabőda abin da suka aikata, dă bai bar wata dabba ba a kanta (kasă). Amma Yană jinkirta musu zuwa ga ajalin da aka ambată. Sa'an nan idan ajalinsu ya zo, to, lalle Allah yă kasance Mai gani ga băyinSa.




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us