Prev
70. Surah Al-Ma'ârij سورة المعارج
Next
1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
سَأَلَ سَائِلٌ بِعَذَابٍ وَاقِعٍ
Saala sa-ilun biAAathabin waqiAA
Hausa
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
|
Ayah 70:2 الأية
لِّلْكَافِرِينَ لَيْسَ لَهُ دَافِعٌ
Lilkafireena laysa lahu dafiAA
Hausa
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
|
Ayah 70:3 الأية
مِّنَ اللهِ ذِي الْمَعَارِجِ
Mina Allahi thee almaAAarij
Hausa
Daga Allah Mai matãkala.
|
Ayah 70:4 الأية
تَعْرُجُ الْمَلَائِكَةُ وَالرُّوحُ إِلَيْهِ فِي يَوْمٍ كَانَ مِقْدَارُهُ
خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍ
TaAAruju almala-ikatu warroohuilayhi fee yawmin kana miqdaruhu khamseena
alfasana
Hausa
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda
gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
|
Ayah 70:5 الأية
فَاصْبِرْ صَبْرًا جَمِيلًا
Fasbir sabran jameela
Hausa
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
|
Ayah 70:6 الأية
إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُ بَعِيدًا
Innahum yarawnahu baAAeeda
Hausa
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
|
Ayah 70:7 الأية
وَنَرَاهُ قَرِيبًا
Wanarahu qareeba
Hausa
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
|
Ayah 70:8 الأية
يَوْمَ تَكُونُ السَّمَاءُ كَالْمُهْلِ
Yawma takoonu assamao kalmuhl
Hausa
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
|
Ayah 70:9 الأية
وَتَكُونُ الْجِبَالُ كَالْعِهْنِ
Watakoonu aljibalu kalAAihn
Hausa
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
|
Ayah 70:10 الأية
وَلَا يَسْأَلُ حَمِيمٌ حَمِيمًا
Wala yas-alu hameemun hameema
Hausa
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
|
Ayah 70:11 الأية
يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ الْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِي مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍ
بِبَنِيهِ
Yubassaroonahum yawaddu almujrimu lawyaftadee min AAathabi yawmi-ithin bibaneeh
Hausa
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar
rãnar nan, da ɗiyansa,
|
Ayah 70:12 الأية
وَصَاحِبَتِهِ وَأَخِيهِ
Wasahibatihi waakheeh
Hausa
Da matarsa da ɗan'uwansa.
|
Ayah 70:13 الأية
وَفَصِيلَتِهِ الَّتِي تُؤْوِيهِ
Wafaseelatihi allatee tu/weeh
Hausa
Da danginsa, mãsu tattarã shi.
|
Ayah 70:14 الأية
وَمَن فِي الْأَرْضِ جَمِيعًا ثُمَّ يُنجِيهِ
Waman fee al-ardi jameeAAan thummayunjeeh
Hausa
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
|
Ayah 70:15 الأية
كَلَّا ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ
Kalla innaha latha
Hausa
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
|
Ayah 70:16 الأية
نَزَّاعَةً لِّلشَّوَىٰ
NazzaAAatan lishshawa
Hausa
Mai twãle fãtar goshi.
|
Ayah 70:17 الأية
تَدْعُو مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ
TadAAoo man adbara watawalla
Hausa
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
|
Ayah 70:18 الأية
وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰ
WajamaAAa faawAAa
Hausa
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
|
Ayah 70:19 الأية
إِنَّ الْإِنسَانَ خُلِقَ هَلُوعًا
Inna al-insana khuliqa halooAAa
Hausa
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
|
Ayah 70:20 الأية
إِذَا مَسَّهُ الشَّرُّ جَزُوعًا
Itha massahu ashsharrujazooAAa
Hausa
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
|
Ayah 70:21 الأية
وَإِذَا مَسَّهُ الْخَيْرُ مَنُوعًا
Wa-itha massahu alkhayru manooAAa
Hausa
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
|
Ayah 70:22 الأية
إِلَّا الْمُصَلِّينَ
Illa almusalleen
Hausa
Sai mãsu yin salla,
|
Ayah 70:23 الأية
الَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَائِمُونَ
Allatheena hum AAala salatihimda-imoon
Hausa
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
|
Ayah 70:24 الأية
وَالَّذِينَ فِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ مَّعْلُومٌ
Wallatheena fee amwalihimhaqqun maAAloom
Hausa
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
|
Ayah 70:25 الأية
لِّلسَّائِلِ وَالْمَحْرُومِ
Lissa-ili walmahroom
Hausa
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
|
Ayah 70:26 الأية
وَالَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ الدِّينِ
Wallatheena yusaddiqoonabiyawmi addeen
Hausa
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
|
Ayah 70:27 الأية
وَالَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ
Wallatheena hum min AAathabirabbihim mushfiqoon
Hausa
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
|
Ayah 70:28 الأية
إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍ
Inna AAathaba rabbihim ghayru ma/moon
Hausa
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
|
Ayah 70:29 الأية
وَالَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ
Wallatheena hum lifuroojihim hafithoon
Hausa
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
|
Ayah 70:30 الأية
إِلَّا عَلَىٰ أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ
مَلُومِينَ
Illa AAala azwajihim awma malakat aymanuhum fa-innahum ghayru maloomeen
Hausa
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle
ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
|
Ayah 70:31 الأية
فَمَنِ ابْتَغَىٰ وَرَاءَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْعَادُونَ
Famani ibtagha waraa thalikafaola-ika humu alAAadoon
Hausa
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu
ƙetare iyãka.
|
Ayah 70:32 الأية
وَالَّذِينَ هُمْ لِأَمَانَاتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَاعُونَ
Wallatheena hum li-amanatihimwaAAahdihim raAAoon
Hausa
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
|
Ayah 70:33 الأية
وَالَّذِينَ هُم بِشَهَادَاتِهِمْ قَائِمُونَ
Wallatheena hum bishahadatihimqa-imoon
Hausa
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
|
Ayah 70:34 الأية
وَالَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ
Wallatheena hum AAala salatihimyuhafithoon
Hausa
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
|
Ayah 70:35 الأية
أُولَٰئِكَ فِي جَنَّاتٍ مُّكْرَمُونَ
Ola-ika fee jannatin mukramoon
Hausa
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
|
Ayah 70:36 الأية
فَمَالِ الَّذِينَ كَفَرُوا قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ
Famali allatheena kafarooqibalaka muhtiAAeen
Hausa
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
|
Ayah 70:37 الأية
عَنِ الْيَمِينِ وَعَنِ الشِّمَالِ عِزِينَ
AAani alyameeni waAAani ashshimaliAAizeen
Hausa
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
|
Ayah 70:38 الأية
أَيَطْمَعُ كُلُّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍ
AyatmaAAu kullu imri-in minhum anyudkhala jannata naAAeem
Hausa
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne
(ba da wani aiki ba)?
|
Ayah 70:39 الأية
كَلَّا ۖ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ
Kalla inna khalaqnahummimma yaAAlamoon
Hausa
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
|
Ayah 70:40 الأية
فَلَا أُقْسِمُ بِرَبِّ الْمَشَارِقِ وَالْمَغَارِبِ إِنَّا لَقَادِرُونَ
Fala oqsimu birabbi almashariqiwalmagharibi inna laqadiroon
Hausa
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren
fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
|
Ayah 70:41 الأية
عَلَىٰ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
AAala an nubaddila khayran minhum wamanahnu bimasbooqeen
Hausa
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda
ake rinjãya ba.
|
Ayah 70:42 الأية
فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا وَيَلْعَبُوا حَتَّىٰ يُلَاقُوا يَوْمَهُمُ الَّذِي
يُوعَدُونَ
Fatharhum yakhoodoowayalAAaboo hatta yulaqoo yawmahumu allatheeyooAAadoon
Hausa
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda
ake yi musu alkawari (da ita) .
|
Ayah 70:43 الأية
يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ الْأَجْدَاثِ سِرَاعًا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍ
يُوفِضُونَ
Yawma yakhrujoona mina al-ajdathi siraAAankaannahum ila nusubin yoofidoon
Hausa
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata
kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
|
Ayah 70:44 الأية
خَاشِعَةً أَبْصَارُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۚ ذَٰلِكَ الْيَوْمُ الَّذِي كَانُوا
يُوعَدُونَ
KhashiAAatan absaruhumtarhaquhum thillatun thalika alyawmu allatheekanoo
yooAAadoon
Hausa
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka
kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|
|