Prev
75. Surah Al-Qiyâmah سورة القيامة
Next
1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
لَا أُقْسِمُ بِيَوْمِ الْقِيَامَةِ
La oqsimu biyawmi alqiyamat
Hausa
Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.
|
Ayah 75:2 الأية
وَلَا أُقْسِمُ بِالنَّفْسِ اللَّوَّامَةِ
Wala oqsimu binnafsi allawwamat
Hausa
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.
|
Ayah 75:3 الأية
أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُ
Ayahsabu al-insanu allannajmaAAa AAithamah
Hausa
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?
|
Ayah 75:4 الأية
بَلَىٰ قَادِرِينَ عَلَىٰ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُ
Bala qadireena AAala annusawwiya bananah
Hausa
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.
|
Ayah 75:5 الأية
بَلْ يُرِيدُ الْإِنسَانُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُ
Bal yureedu al-insanu liyafjura amamah
Hausa
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
|
Ayah 75:6 الأية
يَسْأَلُ أَيَّانَ يَوْمُ الْقِيَامَةِ
Yas-alu ayyana yawmu alqiyama
Hausa
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"
|
Ayah 75:7 الأية
فَإِذَا بَرِقَ الْبَصَرُ
Fa-itha bariqa albasar
Hausa
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
|
Ayah 75:8 الأية
وَخَسَفَ الْقَمَرُ
Wakhasafa alqamar
Hausa
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
|
Ayah 75:9 الأية
وَجُمِعَ الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ
WajumiAAa ashshamsu walqamar
Hausa
Aka tãra rãnã da watã
|
Ayah 75:10 الأية
يَقُولُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ الْمَفَرُّ
Yaqoolu al-insanu yawma-ithinayna almafar
Hausa
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"
|
Ayah 75:11 الأية
كَلَّا لَا وَزَرَ
Kalla la wazar
Hausa
A'aha! bãbu mafaka.
|
Ayah 75:12 الأية
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمُسْتَقَرُّ
Ila rabbika yawma-ithinalmustaqar
Hausa
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
|
Ayah 75:13 الأية
يُنَبَّأُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ
Yunabbao al-insanu yawma-ithinbima qaddama waakhkhar
Hausa
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
|
Ayah 75:14 الأية
بَلِ الْإِنسَانُ عَلَىٰ نَفْسِهِ بَصِيرَةٌ
Bali al-insanu AAala nafsihibaseera
Hausa
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.
|
Ayah 75:15 الأية
وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُ
Walaw alqa maAAatheerah
Hausa
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
|
Ayah 75:16 الأية
لَا تُحَرِّكْ بِهِ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِ
La tuharrik bihi lisanakalitaAAjala bih
Hausa
Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi
(Alƙur'ãni).
|
Ayah 75:17 الأية
إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُ وَقُرْآنَهُ
Inna AAalayna jamAAahu waqur-anah
Hausa
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
|
Ayah 75:18 الأية
فَإِذَا قَرَأْنَاهُ فَاتَّبِعْ قُرْآنَهُ
Fa-itha qara/nahu fattabiAAqur-anah
Hausa
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.
|
Ayah 75:19 الأية
ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُ
Thumma inna AAalayna bayanah
Hausa
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
|
Ayah 75:20 الأية
كَلَّا بَلْ تُحِبُّونَ الْعَاجِلَةَ
Kalla bal tuhibboona alAAajila
Hausa
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
|
Ayah 75:21 الأية
وَتَذَرُونَ الْآخِرَةَ
Watatharoona al-akhira
Hausa
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
|
Ayah 75:22 الأية
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاضِرَةٌ
Wujoohun yawma-ithin nadira
Hausa
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
|
Ayah 75:23 الأية
إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌ
Ila rabbiha nathira
Hausa
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.
|
Ayah 75:24 الأية
وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ بَاسِرَةٌ
Wawujoohun yawma-ithin basira
Hausa
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
|
Ayah 75:25 الأية
تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌ
Tathunnu an yufAAala bihafaqira
Hausa
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.
|
Ayah 75:26 الأية
كَلَّا إِذَا بَلَغَتِ التَّرَاقِيَ
Kalla itha balaghati attaraqiy
Hausa
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.
|
Ayah 75:27 الأية
وَقِيلَ مَنْ ۜ رَاقٍ
Waqeela man raq
Hausa
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"
|
Ayah 75:28 الأية
وَظَنَّ أَنَّهُ الْفِرَاقُ
Wathanna annahu alfiraq
Hausa
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.
|
Ayah 75:29 الأية
وَالْتَفَّتِ السَّاقُ بِالسَّاقِ
Waltaffati assaqu bilssaq
Hausa
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
|
Ayah 75:30 الأية
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمَسَاقُ
Ila rabbika yawma-ithin almasaq
Hausa
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.
|
Ayah 75:31 الأية
فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ
Fala saddaqa wala salla
Hausa
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!
|
Ayah 75:32 الأية
وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Walakin kaththaba watawalla
Hausa
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
|
Ayah 75:33 الأية
ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰ أَهْلِهِ يَتَمَطَّىٰ
Thumma thahaba ila ahlihiyatamatta
Hausa
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.
|
Ayah 75:34 الأية
أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ
Awla laka faawla
Hausa
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
|
Ayah 75:35 الأية
ثُمَّ أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ
Thumma awla laka faawla
Hausa
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
|
Ayah 75:36 الأية
أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَن يُتْرَكَ سُدًى
Ayahsabu al-insanu an yutrakasuda
Hausa
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi) ?
|
Ayah 75:37 الأية
أَلَمْ يَكُ نُطْفَةً مِّن مَّنِيٍّ يُمْنَىٰ
Alam yaku nutfatan min manayyin yumna
Hausa
Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa( a cikin mahaifa)
|
Ayah 75:38 الأية
ثُمَّ كَانَ عَلَقَةً فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ
Thumma kana AAalaqatan fakhalaqafasawwa
Hausa
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya
daidaita gaɓõɓinsa;
|
Ayah 75:39 الأية
فَجَعَلَ مِنْهُ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ
FajaAAala minhu azzawjayni aththakarawal-ontha
Hausa
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?
|
Ayah 75:40 الأية
أَلَيْسَ ذَٰلِكَ بِقَادِرٍ عَلَىٰ أَن يُحْيِيَ الْمَوْتَىٰ
Alaysa thalika biqadirin AAalaan yuhyiya almawta
Hausa
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|
|