Prev  

75. Surah Al-Qiyâmah سورة القيامة

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
لَا أُقْسِمُ بِيَوْمِ الْقِيَامَةِ
La oqsimu biyawmi alqiyamat

Hausa
 
Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.

Ayah  75:2  الأية
وَلَا أُقْسِمُ بِالنَّفْسِ اللَّوَّامَةِ
Wala oqsimu binnafsi allawwamat

Hausa
 
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.

Ayah  75:3  الأية
أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُ
Ayahsabu al-insanu allannajmaAAa AAithamah

Hausa
 
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?

Ayah  75:4  الأية
بَلَىٰ قَادِرِينَ عَلَىٰ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُ
Bala qadireena AAala annusawwiya bananah

Hausa
 
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.

Ayah  75:5  الأية
بَلْ يُرِيدُ الْإِنسَانُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُ
Bal yureedu al-insanu liyafjura amamah

Hausa
 
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.

Ayah  75:6  الأية
يَسْأَلُ أَيَّانَ يَوْمُ الْقِيَامَةِ
Yas-alu ayyana yawmu alqiyama

Hausa
 
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"

Ayah  75:7  الأية
فَإِذَا بَرِقَ الْبَصَرُ
Fa-itha bariqa albasar

Hausa
 
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).

Ayah  75:8  الأية
وَخَسَفَ الْقَمَرُ
Wakhasafa alqamar

Hausa
 
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

Ayah  75:9  الأية
وَجُمِعَ الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ
WajumiAAa ashshamsu walqamar

Hausa
 
Aka tãra rãnã da watã

Ayah  75:10  الأية
يَقُولُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ الْمَفَرُّ
Yaqoolu al-insanu yawma-ithinayna almafar

Hausa
 
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"

Ayah  75:11  الأية
كَلَّا لَا وَزَرَ
Kalla la wazar

Hausa
 
A'aha! bãbu mafaka.

Ayah  75:12  الأية
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمُسْتَقَرُّ
Ila rabbika yawma-ithinalmustaqar

Hausa
 
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.

Ayah  75:13  الأية
يُنَبَّأُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ
Yunabbao al-insanu yawma-ithinbima qaddama waakhkhar

Hausa
 
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.

Ayah  75:14  الأية
بَلِ الْإِنسَانُ عَلَىٰ نَفْسِهِ بَصِيرَةٌ
Bali al-insanu AAala nafsihibaseera

Hausa
 
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.

Ayah  75:15  الأية
وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُ
Walaw alqa maAAatheerah

Hausa
 
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).

Ayah  75:16  الأية
لَا تُحَرِّكْ بِهِ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِ
La tuharrik bihi lisanakalitaAAjala bih

Hausa
 
Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).

Ayah  75:17  الأية
إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُ وَقُرْآنَهُ
Inna AAalayna jamAAahu waqur-anah

Hausa
 
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.

Ayah  75:18  الأية
فَإِذَا قَرَأْنَاهُ فَاتَّبِعْ قُرْآنَهُ
Fa-itha qara/nahu fattabiAAqur-anah

Hausa
 
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.

Ayah  75:19  الأية
ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُ
Thumma inna AAalayna bayanah

Hausa
 
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.

Ayah  75:20  الأية
كَلَّا بَلْ تُحِبُّونَ الْعَاجِلَةَ
Kalla bal tuhibboona alAAajila

Hausa
 
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.

Ayah  75:21  الأية
وَتَذَرُونَ الْآخِرَةَ
Watatharoona al-akhira

Hausa
 
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).

Ayah  75:22  الأية
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاضِرَةٌ
Wujoohun yawma-ithin nadira

Hausa
 
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.

Ayah  75:23  الأية
إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌ
Ila rabbiha nathira

Hausa
 
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.

Ayah  75:24  الأية
وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ بَاسِرَةٌ
Wawujoohun yawma-ithin basira

Hausa
 
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.

Ayah  75:25  الأية
تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌ
Tathunnu an yufAAala bihafaqira

Hausa
 
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.

Ayah  75:26  الأية
كَلَّا إِذَا بَلَغَتِ التَّرَاقِيَ
Kalla itha balaghati attaraqiy

Hausa
 
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.

Ayah  75:27  الأية
وَقِيلَ مَنْ ۜ رَاقٍ
Waqeela man raq

Hausa
 
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"

Ayah  75:28  الأية
وَظَنَّ أَنَّهُ الْفِرَاقُ
Wathanna annahu alfiraq

Hausa
 
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.

Ayah  75:29  الأية
وَالْتَفَّتِ السَّاقُ بِالسَّاقِ
Waltaffati assaqu bilssaq

Hausa
 
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.

Ayah  75:30  الأية
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمَسَاقُ
Ila rabbika yawma-ithin almasaq

Hausa
 
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.

Ayah  75:31  الأية
فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ
Fala saddaqa wala salla

Hausa
 
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!

Ayah  75:32  الأية
وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Walakin kaththaba watawalla

Hausa
 
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!

Ayah  75:33  الأية
ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰ أَهْلِهِ يَتَمَطَّىٰ
Thumma thahaba ila ahlihiyatamatta

Hausa
 
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.

Ayah  75:34  الأية
أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ
Awla laka faawla

Hausa
 
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.

Ayah  75:35  الأية
ثُمَّ أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ
Thumma awla laka faawla

Hausa
 
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.

Ayah  75:36  الأية
أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَن يُتْرَكَ سُدًى
Ayahsabu al-insanu an yutrakasuda

Hausa
 
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi) ?

Ayah  75:37  الأية
أَلَمْ يَكُ نُطْفَةً مِّن مَّنِيٍّ يُمْنَىٰ
Alam yaku nutfatan min manayyin yumna

Hausa
 
Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa( a cikin mahaifa)

Ayah  75:38  الأية
ثُمَّ كَانَ عَلَقَةً فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ
Thumma kana AAalaqatan fakhalaqafasawwa

Hausa
 
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;

Ayah  75:39  الأية
فَجَعَلَ مِنْهُ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ
FajaAAala minhu azzawjayni aththakarawal-ontha

Hausa
 
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?

Ayah  75:40  الأية
أَلَيْسَ ذَٰلِكَ بِقَادِرٍ عَلَىٰ أَن يُحْيِيَ الْمَوْتَىٰ
Alaysa thalika biqadirin AAalaan yuhyiya almawta

Hausa
 
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu? 




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us