Prev  

82. Surah Al-Infitâr سورة الإنفطار

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
إِذَا السَّمَاءُ انفَطَرَتْ
Itha assamao infatarat

Hausa
 
Idan sama ta tsãge.

Ayah  82:2  الأية
وَإِذَا الْكَوَاكِبُ انتَثَرَتْ
Wa-itha alkawakibu intatharat

Hausa
 
Kuma idan taurãri suka wãtse.

Ayah  82:3  الأية
وَإِذَا الْبِحَارُ فُجِّرَتْ
Wa-itha albiharu fujjirat

Hausa
 
Kuma idan tẽkuna aka facce su.

Ayah  82:4  الأية
وَإِذَا الْقُبُورُ بُعْثِرَتْ
Wa-itha alqubooru buAAthirat

Hausa
 
Kuma idan kaburbura aka tõne su.

Ayah  82:5  الأية
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ
AAalimat nafsun ma qaddamatwaakhkharat

Hausa
 
Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.

Ayah  82:6  الأية
يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ الْكَرِيمِ
Ya ayyuha al-insanu magharraka birabbika alkareem

Hausa
 
Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.

Ayah  82:7  الأية
الَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّاكَ فَعَدَلَكَ
Allathee khalaqaka fasawwakafaAAadalak

Hausa
 
Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.

Ayah  82:8  الأية
فِي أَيِّ صُورَةٍ مَّا شَاءَ رَكَّبَكَ
Fee ayyi sooratin ma shaarakkabak

Hausa
 
A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.

Ayah  82:9  الأية
كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِالدِّينِ
Kalla bal tukaththiboona biddeen

Hausa
 
A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!

Ayah  82:10  الأية
وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَافِظِينَ
Wa-inna AAalaykum lahafitheen

Hausa
 
Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.

Ayah  82:11  الأية
كِرَامًا كَاتِبِينَ
Kiraman katibeen

Hausa
 
Mãsu daraja, marubũta.

Ayah  82:12  الأية
يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ
YaAAlamoona ma tafAAaloon

Hausa
 
Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.

Ayah  82:13  الأية
إِنَّ الْأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍ
Inna al-abrara lafee naAAeem

Hausa
 
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.

Ayah  82:14  الأية
وَإِنَّ الْفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٍ
Wa-inna alfujjara lafee jaheem

Hausa
 
Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.

Ayah  82:15  الأية
يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ الدِّينِ
Yaslawnaha yawma addeen

Hausa
 
Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.

Ayah  82:16  الأية
وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَائِبِينَ
Wama hum AAanha bigha-ibeen

Hausa
 
Bã zã su faku daga gare ta ba.

Ayah  82:17  الأية
وَمَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ
Wama adraka ma yawmu addeeni

Hausa
 
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?

Ayah  82:18  الأية
ثُمَّ مَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ
Thumma ma adraka mayawmu addeen

Hausa
 
Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?

Ayah  82:19  الأية
يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌ لِّنَفْسٍ شَيْئًا ۖ وَالْأَمْرُ يَوْمَئِذٍ لِّلَّهِ
Yawma la tamliku nafsun linafsinshay-an wal-amru yawma-ithin lillah

Hausa
 
Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us