Prev  

83. Surah Al-Mutaffifîn سورة المطفّفين

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَيْلٌ لِّلْمُطَفِّفِينَ
Waylun lilmutaffifeen

Hausa
 
Bone ya tabbata ga mãsu naƙƙasãwa.

Ayah  83:2  الأية
الَّذِينَ إِذَا اكْتَالُوا عَلَى النَّاسِ يَسْتَوْفُونَ
Allatheena itha iktalooAAala annasi yastawfoon

Hausa
 
Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.

Ayah  83:3  الأية
وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ
Wa-itha kaloohum aw wazanoohumyukhsiroon

Hausa
 
Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa

Ayah  83:4  الأية
أَلَا يَظُنُّ أُولَٰئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ
Ala yathunnu ola-ikaannahum mabAAoothoon

Hausa
 
Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?

Ayah  83:5  الأية
لِيَوْمٍ عَظِيمٍ
Liyawmin AAatheem

Hausa
 
Domin yini mai girma.

Ayah  83:6  الأية
يَوْمَ يَقُومُ النَّاسُ لِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Yawma yaqoomu annasu lirabbialAAalameen

Hausa
 
Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta?

Ayah  83:7  الأية
كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الْفُجَّارِ لَفِي سِجِّينٍ
Kalla inna kitaba alfujjarilafee sijjeen

Hausa
 
Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn.

Ayah  83:8  الأية
وَمَا أَدْرَاكَ مَا سِجِّينٌ
Wama adraka ma sijjeen

Hausa
 
Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn?

Ayah  83:9  الأية
كِتَابٌ مَّرْقُومٌ
Kitabun marqoom

Hausa
 
Wani 1ittãfi ne rubũtacce.

Ayah  83:10  الأية
وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
Waylun yawma-ithin lilmukaththibeen

Hausa
 
Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.

Ayah  83:11  الأية
الَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ الدِّينِ
Allatheena yukaththiboonabiyawmi addeen

Hausa
 
Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako.

Ayah  83:12  الأية
وَمَا يُكَذِّبُ بِهِ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ
Wama yukaththibu bihi illakullu muAAtadin atheem

Hausa
 
Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi.

Ayah  83:13  الأية
إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ آيَاتُنَا قَالَ أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ
Itha tutla AAalayhi ayatunaqala asateeru al-awwaleen

Hausa
 
Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne.

Ayah  83:14  الأية
كَلَّا ۖ بَلْ ۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا يَكْسِبُونَ
Kalla bal rana AAalaquloobihim ma kanoo yaksiboon

Hausa
 
A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu.

Ayah  83:15  الأية
كَلَّا إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّمَحْجُوبُونَ
Kalla innahum AAan rabbihim yawma-ithinlamahjooboon

Hausa
 
A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne.

Ayah  83:16  الأية
ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُو الْجَحِيمِ
Thumma innahum lasaloo aljaheem

Hausa
 
Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne.

Ayah  83:17  الأية
ثُمَّ يُقَالُ هَٰذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ
Thumma yuqalu hatha allatheekuntum bihi tukaththiboon

Hausa
 
Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi."

Ayah  83:18  الأية
كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الْأَبْرَارِ لَفِي عِلِّيِّينَ
Kalla inna kitaba al-abrarilafee AAilliyyeen

Hausa
 
A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna?

Ayah  83:19  الأية
وَمَا أَدْرَاكَ مَا عِلِّيُّونَ
Wama adraka maAAilliyyoon

Hausa
 
Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna?

Ayah  83:20  الأية
كِتَابٌ مَّرْقُومٌ
Kitabun marqoom

Hausa
 
Wani littãfi ne rubũtacce.

Ayah  83:21  الأية
يَشْهَدُهُ الْمُقَرَّبُونَ
Yashhaduhu almuqarraboon

Hausa
 
Muƙarrabai suke halarta shi.

Ayah  83:22  الأية
إِنَّ الْأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍ
Inna al-abrara lafee naAAeem

Hausa
 
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima.

Ayah  83:23  الأية
عَلَى الْأَرَائِكِ يَنظُرُونَ
AAala al-ara-iki yanthuroon

Hausa
 
A kan karagu, suna ta kallo.

Ayah  83:24  الأية
تَعْرِفُ فِي وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ النَّعِيمِ
TaAArifu fee wujoohihim nadrata annaAAeem

Hausa
 
Kana sani a cikin huskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima.

Ayah  83:25  الأية
يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍ مَّخْتُومٍ
Yusqawna min raheeqin makhtoom

Hausa
 
Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta.

Ayah  83:26  الأية
خِتَامُهُ مِسْكٌ ۚ وَفِي ذَٰلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ الْمُتَنَافِسُونَ
Khitamuhu miskun wafee thalikafalyatanafasi almutanafisoon

Hausa
 
¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma.

Ayah  83:27  الأية
وَمِزَاجُهُ مِن تَسْنِيمٍ
Wamizajuhu min tasneem

Hausa
 
Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake.

Ayah  83:28  الأية
عَيْنًا يَشْرَبُ بِهَا الْمُقَرَّبُونَ
AAaynan yashrabu biha almuqarraboon

Hausa
 
(Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi.

Ayah  83:29  الأية
إِنَّ الَّذِينَ أَجْرَمُوا كَانُوا مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا يَضْحَكُونَ
Inna allatheena ajramoo kanoomina allatheena amanoo yadhakoon

Hausa
 
Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya.

Ayah  83:30  الأية
وَإِذَا مَرُّوا بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ
Wa-itha marroo bihim yataghamazoon

Hausa
 
Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe.

Ayah  83:31  الأية
وَإِذَا انقَلَبُوا إِلَىٰ أَهْلِهِمُ انقَلَبُوا فَكِهِينَ
Wa-itha inqalaboo ila ahlihimuinqalaboo fakiheen

Hausa
 
Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci.

Ayah  83:32  الأية
وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوا إِنَّ هَٰؤُلَاءِ لَضَالُّونَ
Wa-itha raawhum qaloo inna haola-iladalloon

Hausa
 
Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne."

Ayah  83:33  الأية
وَمَا أُرْسِلُوا عَلَيْهِمْ حَافِظِينَ
Wama orsiloo AAalayhim hafitheen

Hausa
 
Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu.

Ayah  83:34  الأية
فَالْيَوْمَ الَّذِينَ آمَنُوا مِنَ الْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ
Falyawma allatheena amanoomina alkuffari yadhakoon

Hausa
 
To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni,sũ ke yi wa kãfirai dãriya.

Ayah  83:35  الأية
عَلَى الْأَرَائِكِ يَنظُرُونَ
AAala al-ara-iki yanthuroon

Hausa
 
A kan karagu, suna ta kallo.

Ayah  83:36  الأية
هَلْ ثُوِّبَ الْكُفَّارُ مَا كَانُوا يَفْعَلُونَ
Hal thuwwiba alkuffaru ma kanooyafAAaloon

Hausa
 
Shin an sãka ma kãfirai abin da suka kasance suna aikatawa? 




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us