1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
قَدْ أَفْلَحَ الْمُؤْمِنُونَ
Qad aflaha almu/minoon
Hausa
Lalle ne, Mũminai sun sãmi babban rabõ.
|
Ayah 23:2 الأية
الَّذِينَ هُمْ فِي صَلَاتِهِمْ خَاشِعُونَ
Allatheena hum fee salatihimkhashiAAoon
Hausa
Waɗanda suke a cikin sallarsu mãsu tawãli'u ne.
|
Ayah 23:3 الأية
وَالَّذِينَ هُمْ عَنِ اللَّغْوِ مُعْرِضُونَ
Wallatheena hum AAani allaghwimuAAridoon
Hausa
Kuma waɗanda suke, sũdaga barin yasassar magana, mãsu kau da kai ne.
|
Ayah 23:4 الأية
وَالَّذِينَ هُمْ لِلزَّكَاةِ فَاعِلُونَ
Wallatheena hum lizzakatifaAAiloon
Hausa
Kuma waɗanda suke ga zakka mãsu aikatãwa ne.
|
Ayah 23:5 الأية
وَالَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ
Wallatheena hum lifuroojihim hafithoon
Hausa
Kuma waɗanda suke ga farjõjinsu mãsu tsarẽwa ne.
|
Ayah 23:6 الأية
إِلَّا عَلَىٰ أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ
مَلُومِينَ
Illa AAala azwajihim awma malakat aymanuhum fa-innahum ghayru maloomeen
Hausa
Fãce a kan mãtan aurensu, kõ kuwa abin da hannayen dãmansu suka mallaka to lalle
sũ bã waɗanda ake zargi, ba, ne.
|
Ayah 23:7 الأية
فَمَنِ ابْتَغَىٰ وَرَاءَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْعَادُونَ
Famani ibtagha waraa thalikafaola-ika humu alAAadoon
Hausa
Sabõda haka wanda ya nẽmi abin da ke bãyan wancan, to, waɗancan sũ ne mãsu
ƙẽtarẽwar haddi.
|
Ayah 23:8 الأية
وَالَّذِينَ هُمْ لِأَمَانَاتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَاعُونَ
Wallatheena hum li-amanatihimwaAAahdihim raAAoon
Hausa
Kuma waɗanda suke, sũga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
|
Ayah 23:9 الأية
وَالَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَوَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ
Wallatheena hum AAala salawatihimyuhafithoon
Hausa
Kuma da waɗanda suke, sũ a kan sallõlinsu sunã tsarẽwa.
|
Ayah 23:10 الأية
أُولَٰئِكَ هُمُ الْوَارِثُونَ
Ola-ika humu alwarithoon
Hausa
Waɗannan, sũ ne magãda.
|
Ayah 23:11 الأية
الَّذِينَ يَرِثُونَ الْفِرْدَوْسَ هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ
Allatheena yarithoona alfirdawsa humfeeha khalidoon
Hausa
Waɗanda suke gãdõn (Aljannar) Firdausi, su a cikinta madawwama ne.
|
Ayah 23:12 الأية
وَلَقَدْ خَلَقْنَا الْإِنسَانَ مِن سُلَالَةٍ مِّن طِينٍ
Walaqad khalaqna al-insana minsulalatin min teen
Hausa
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga lãka.
|
Ayah 23:13 الأية
ثُمَّ جَعَلْنَاهُ نُطْفَةً فِي قَرَارٍ مَّكِينٍ
Thumma jaAAalnahu nutfatan feeqararin makeen
Hausa
Sa'an nan kuma Muka sanya shi, ɗigon maniyyi a cikin matabbata natsattsiya.
|
Ayah 23:14 الأية
ثُمَّ خَلَقْنَا النُّطْفَةَ عَلَقَةً فَخَلَقْنَا الْعَلَقَةَ مُضْغَةً
فَخَلَقْنَا الْمُضْغَةَ عِظَامًا فَكَسَوْنَا الْعِظَامَ لَحْمًا ثُمَّ
أَنشَأْنَاهُ خَلْقًا آخَرَ ۚ فَتَبَارَكَ اللهُ أَحْسَنُ الْخَالِقِينَ
Thumma khalaqna annutfataAAalaqatan fakhalaqna alAAalaqata mudghatanfakhalaqna
almudghata AAithamanfakasawna alAAithama lahmanthumma ansha/nahu khalqan akhara
fatabarakaAllahu ahsanu alkhaliqeen
Hausa
Sa'an nan kuma Muka halitta shi gudan jini, sa'an nan Muka halitta gudan jinin
tsõka, sa'an nan Muka halitta tsõkar ta zama ƙasũsuwa, sa'an nan Muka tufãtar da
ƙasũsuwan da wani nãma sa'an nan kuma Muka ƙãga shi wata halitta dabam. Sabõda
haka albarkun Allah sun bayyana, Shi ne Mafi kyaun mãsu halittawa.
|
Ayah 23:15 الأية
ثُمَّ إِنَّكُم بَعْدَ ذَٰلِكَ لَمَيِّتُونَ
Thumma innakum baAAda thalikalamayyitoon
Hausa
Sa'an nan kuma ku, bãyan wannan, lalle ne masu mutuwa ne.
|
Ayah 23:16 الأية
ثُمَّ إِنَّكُمْ يَوْمَ الْقِيَامَةِ تُبْعَثُونَ
Thumma innakum yawma alqiyamatitubAAathoon
Hausa
Sa'an nan kuma lalle ne kũ a Rãnar ¡iyãma, za a iãyar da ku,
|
Ayah 23:17 الأية
وَلَقَدْ خَلَقْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعَ طَرَائِقَ وَمَا كُنَّا عَنِ الْخَلْقِ
غَافِلِينَ
Walaqad khalaqna fawqakum sabAAa tara-iqawama kunna AAani alkhalqi ghafileen
Hausa
Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun halitta, a samanku, hanyõyi bakwai, kuma ba Mu kasance,
daga barin halittar, Mãsu shagala ba.
|
Ayah 23:18 الأية
وَأَنزَلْنَا مِنَ السَّمَاءِ مَاءً بِقَدَرٍ فَأَسْكَنَّاهُ فِي الْأَرْضِ ۖ
وَإِنَّا عَلَىٰ ذَهَابٍ بِهِ لَقَادِرُونَ
Waanzalna mina assama-imaan biqadarin faaskannahu fee al-ardiwa-inna AAala
thahabin bihi laqadiroon
Hausa
Muka saukar da ruwa daga sama bisa gwargwado, sa'an nan Muka zaunar da shi a
cikin ƙasa alhãli, lalle ne Mũ, a kan tafiyar da shi, Mãsu iyãwa ne.
|
Ayah 23:19 الأية
فَأَنشَأْنَا لَكُم بِهِ جَنَّاتٍ مِّن نَّخِيلٍ وَأَعْنَابٍ لَّكُمْ فِيهَا
فَوَاكِهُ كَثِيرَةٌ وَمِنْهَا تَأْكُلُونَ
Faansha/na lakum bihi jannatinmin nakheelin waaAAnabin lakum feeha
fawakihukatheeratun waminha ta/kuloon
Hausa
Sai Muka ƙãga muku, game da shi (ruwan), gõnaki daga daĩnai da inabõbi, kunã da,
a cikinsu, 'ya'yan itãcen marmari mãsu yawa, kuma daga gare su kuke ci.
|
Ayah 23:20 الأية
وَشَجَرَةً تَخْرُجُ مِن طُورِ سَيْنَاءَ تَنبُتُ بِالدُّهْنِ وَصِبْغٍ
لِّلْآكِلِينَ
Washajaratan takhruju min toori saynaatanbutu bidduhni wasibghin lilakileen
Hausa
Da wata itãciya, tanã fita daga dũtsin Sainã'a, tanã tsira da man shãfãwa, da
man miya dõmin masu cĩ.
|
Ayah 23:21 الأية
وَإِنَّ لَكُمْ فِي الْأَنْعَامِ لَعِبْرَةً ۖ نُّسْقِيكُم مِّمَّا فِي بُطُونِهَا
وَلَكُمْ فِيهَا مَنَافِعُ كَثِيرَةٌ وَمِنْهَا تَأْكُلُونَ
Wa-inna lakum fee al-anAAamilaAAibratan nusqeekum mimma fee butoonihawalakum
feeha manafiAAu katheeratun waminhata/kuloon
Hausa
Kuma lalle ne kunã da abin lũra a cikin dabbõbin ni'imõmi Munã shãyar da ku daga
abin da yake a cikinsu, kuma kunã da a cikinsu abũbuwan amfãni mãsu yawa, kuma
daga gare su kuke cĩ
|
Ayah 23:22 الأية
وَعَلَيْهَا وَعَلَى الْفُلْكِ تُحْمَلُونَ
WaAAalayha waAAala alfulki tuhmaloon
Hausa
Kuma a kansu da a kan jirgin ruwa ake ɗaukar ku.
|
Ayah 23:23 الأية
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا نُوحًا إِلَىٰ قَوْمِهِ فَقَالَ يَا قَوْمِ اعْبُدُوا اللهَ
مَا لَكُم مِّنْ إِلَٰهٍ غَيْرُهُ ۖ أَفَلَا تَتَّقُونَ
Walaqad arsalna noohan ilaqawmihi faqala ya qawmi oAAbudoo Allaha malakum min
ilahin ghayruhu afala tattaqoon
Hausa
Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika Nũhu zuwa ga mutãnensa, sai ya ce: "Yã mutãnẽna!
Ku bauta wa Allah. Bã ku da wani abin bautãwa waninsa. Shin, to, bã za ku yi
taƙawa ba?"
|
Ayah 23:24 الأية
فَقَالَ الْمَلَأُ الَّذِينَ كَفَرُوا مِن قَوْمِهِ مَا هَٰذَا إِلَّا بَشَرٌ
مِّثْلُكُمْ يُرِيدُ أَن يَتَفَضَّلَ عَلَيْكُمْ وَلَوْ شَاءَ اللهُ لَأَنزَلَ
مَلَائِكَةً مَّا سَمِعْنَا بِهَٰذَا فِي آبَائِنَا الْأَوَّلِينَ
Faqala almalao allatheenakafaroo min qawmihi ma hatha illa basharunmithlukum
yureedu an yatafaddala AAalaykum walaw shaaAllahu laanzala mala-ikatan ma
samiAAnabihatha fee aba-ina al-awwaleen
Hausa
Sai mashãwarta waɗanda suka kãfirta daga mutãnensa, suka ce: "Wannan ba kõwa ba
ne, fãce mutum misãlinku, yanã nufin ya ɗaukaka a kanku. Dã Allah Yã so, lalle
ne dã Yã saukar da Malã'iku, Ba muji (kõme)ba, game da wannan, a cikin ubanninmu
na farko."
|
Ayah 23:25 الأية
إِنْ هُوَ إِلَّا رَجُلٌ بِهِ جِنَّةٌ فَتَرَبَّصُوا بِهِ حَتَّىٰ حِينٍ
In huwa illa rajulun bihi jinnatunfatarabbasoo bihi hatta heen
Hausa
"Shi bai zamo kõwa ba fãce wani namiji ne, a gare shi akwai hauka, sai ku yi
jinkiri da shi har wani lõkaci."
|
Ayah 23:26 الأية
قَالَ رَبِّ انصُرْنِي بِمَا كَذَّبُونِ
Qala rabbi onsurnee bimakaththaboon
Hausa
Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka taimakeni sabõda sun ƙaryatani."
|
Ayah 23:27 الأية
فَأَوْحَيْنَا إِلَيْهِ أَنِ اصْنَعِ الْفُلْكَ بِأَعْيُنِنَا وَوَحْيِنَا فَإِذَا
جَاءَ أَمْرُنَا وَفَارَ التَّنُّورُ ۙ فَاسْلُكْ فِيهَا مِن كُلٍّ زَوْجَيْنِ
اثْنَيْنِ وَأَهْلَكَ إِلَّا مَن سَبَقَ عَلَيْهِ الْقَوْلُ مِنْهُمْ ۖ وَلَا
تُخَاطِبْنِي فِي الَّذِينَ ظَلَمُوا ۖ إِنَّهُم مُّغْرَقُونَ
Faawhayna ilayhi ani isnaAAialfulka bi-aAAyunina wawahyina fa-ithajaa amruna
wafara attannooru faslukfeeha min kullin zawjayni ithnayni waahlaka illaman
sabaqa AAalayhi alqawlu minhum wala tukhatibneefee allatheena thalamoo innahum
mughraqoon
Hausa
Sai Muka yi wahayi zuwa gare shi. "Ka sana'anta jirgin bisa ga idonMu, da
wahayinMu. To, idan umuminMu ya jẽ, kuma tandã ta ɓuɓɓuga da ruwa, to, ka shigar
a cikinta daga kõme, ma'aura biyu, da iyãlanka, sai wanda Magana ta gabãta a
kansa, daga gare su, kuma kada ka rõƙẽ Ni (sabõda wani) a cikin waɗanda suka yi
zãlunci, lalle ne sũ waɗanda ake nutsarwa ne.
|
Ayah 23:28 الأية
فَإِذَا اسْتَوَيْتَ أَنتَ وَمَن مَّعَكَ عَلَى الْفُلْكِ فَقُلِ الْحَمْدُ لِلَّهِ
الَّذِي نَجَّانَا مِنَ الْقَوْمِ الظَّالِمِينَ
Fa-itha istawayta anta waman maAAakaAAala alfulki faquli alhamdu lillahi
allatheenajjana mina alqawmi aththalimeen
Hausa
"Sa'an nan idan ka daidaitu kai da waɗanda ke tãre da kai a kan jirgin, sai ka
ce: "Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya tsĩrar damu daga mutãne azzãlumai."
|
Ayah 23:29 الأية
وَقُل رَّبِّ أَنزِلْنِي مُنزَلًا مُّبَارَكًا وَأَنتَ خَيْرُ الْمُنزِلِينَ
Waqul rabbi anzilnee munzalan mubarakanwaanta khayru almunzileen
Hausa
"Kuma ka ce: 'Ya Ubangijĩna! Ka saukar da ni, saukarwa mai albarka. Kuma Kai ne
Mafi alhẽrin mãsu saukarwa.'"
|
Ayah 23:30 الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَاتٍ وَإِن كُنَّا لَمُبْتَلِينَ
Inna fee thalika laayatinwa-in kunna lamubtaleen
Hausa
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi, ko da yake Mun kasance, haƙẽƙa' Mãsu
jarrabãwa.
|
Ayah 23:31 الأية
ثُمَّ أَنشَأْنَا مِن بَعْدِهِمْ قَرْنًا آخَرِينَ
Thumma ansha/na min baAAdihim qarnan akhareen
Hausa
Sa'an nan kuma Muka ƙãga wani ƙarni na waɗansu dabam daga bãyansu.
|
Ayah 23:32 الأية
فَأَرْسَلْنَا فِيهِمْ رَسُولًا مِّنْهُمْ أَنِ اعْبُدُوا اللهَ مَا لَكُم مِّنْ
إِلَٰهٍ غَيْرُهُ ۖ أَفَلَا تَتَّقُونَ
Faarsalna feehim rasoolan minhum anioAAbudoo Allaha ma lakum min ilahin
ghayruhuafala tattaqoon
Hausa
Sai Muka aika a cikinsu Manzo daga gare su. "Ku bauta wa Allah. Bã ku da wani
abin bautãwa, sai Shi. Shin to, bã zã ku yi taƙawa ba?"
|
Ayah 23:33 الأية
وَقَالَ الْمَلَأُ مِن قَوْمِهِ الَّذِينَ كَفَرُوا وَكَذَّبُوا بِلِقَاءِ
الْآخِرَةِ وَأَتْرَفْنَاهُمْ فِي الْحَيَاةِ الدُّنْيَا مَا هَٰذَا إِلَّا بَشَرٌ
مِّثْلُكُمْ يَأْكُلُ مِمَّا تَأْكُلُونَ مِنْهُ وَيَشْرَبُ مِمَّا تَشْرَبُونَ
Waqala almalao min qawmihi allatheenakafaroo wakaththaboo biliqa-i
al-akhiratiwaatrafnahum fee alhayati addunyama hatha illa basharun mithlukum
ya/kulumimma ta/kuloona minhu wayashrabu mimma tashraboon
Hausa
Mashãwarta daga mutãnensa, waɗanda suka kãfirta kuma suka ƙaryata game da haɗuwa
da Lãhira, kuma Muka ni'imtar da su a cikin rãyuwar dũniya, suka ce: "Wannan bã
kõwa ba fãce wani mutum ne kamarku, yanã cĩ daga abin da kuke cĩ daga gare shi,
kuma yanã shã daga abin da kuke shã."
|
Ayah 23:34 الأية
وَلَئِنْ أَطَعْتُم بَشَرًا مِّثْلَكُمْ إِنَّكُمْ إِذًا لَّخَاسِرُونَ
Wala-in ataAAtum basharan mithlakuminnakum ithan lakhasiroon
Hausa
"Kuma lalle ne idan kun yi ɗã' a ga mutum misãlinku, lalle ne, a lõkacin nan,
haƙĩƙa, kũ mãsu hasãra ne."
|
Ayah 23:35 الأية
أَيَعِدُكُمْ أَنَّكُمْ إِذَا مِتُّمْ وَكُنتُمْ تُرَابًا وَعِظَامًا أَنَّكُم
مُّخْرَجُونَ
AyaAAidukum annakum itha mittumwakuntum turaban waAAithaman annakummukhrajoon
Hausa
"Shin, yanã yi muku wa'adin (cẽwa) lalle kũ, idan kun mutu kuma kuka kasance
turɓãya da ɓasũsuwa lalle ne kũ waɗanda ake fitarwa ne?"
|
Ayah 23:36 الأية
هَيْهَاتَ هَيْهَاتَ لِمَا تُوعَدُونَ
Hayhata hayhata limatooAAadoon
Hausa
"Faufau faufau ga abin da ake yi muku wa'adi da shi."
|
Ayah 23:37 الأية
إِنْ هِيَ إِلَّا حَيَاتُنَا الدُّنْيَا نَمُوتُ وَنَحْيَا وَمَا نَحْنُ
بِمَبْعُوثِينَ
In hiya illa hayatunaaddunya namootu wanahya wamanahnu bimabAAootheen
Hausa
"Rãyuwa ba ta zama ba fãce rãyuwarmu ta dũniya, munã mutuwa kuma munã rãyuwa,
kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
|
Ayah 23:38 الأية
إِنْ هُوَ إِلَّا رَجُلٌ افْتَرَىٰ عَلَى اللهِ كَذِبًا وَمَا نَحْنُ لَهُ
بِمُؤْمِنِينَ
In huwa illa rajulun iftaraAAala Allahi kathiban wama nahnulahu bimu/mineen
Hausa
"Bai zama kõwa ba fãce namiji, ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kuma ba mu zama,
sabõda shi, mãsu ĩmãni ba."
|
Ayah 23:39 الأية
قَالَ رَبِّ انصُرْنِي بِمَا كَذَّبُونِ
Qala rabbi onsurnee bimakaththaboon
Hausa
Ya ce: "Ya Ubangijĩna! Ka taimake ni sabõda sun ƙaryatã ni."
|
Ayah 23:40 الأية
قَالَ عَمَّا قَلِيلٍ لَّيُصْبِحُنَّ نَادِمِينَ
Qala AAamma qaleelin layusbihunnanadimeen
Hausa
Ya ce: "Daga abu kaɗan, lalle ne zã su wãyi gari sunã mãsu nadãma."
|
Ayah 23:41 الأية
فَأَخَذَتْهُمُ الصَّيْحَةُ بِالْحَقِّ فَجَعَلْنَاهُمْ غُثَاءً ۚ فَبُعْدًا
لِّلْقَوْمِ الظَّالِمِينَ
Faakhathat-humu assayhatubilhaqqi fajaAAalnahum ghuthaanfabuAAdan lilqawmi
aththalimeen
Hausa
Sai tsãwa ta kãma su da gaskiya, sai Muka sanya su tunkuɓa. Sabõda haka nĩsa ya
tabbataga mutãne azzãlumai!
|
Ayah 23:42 الأية
ثُمَّ أَنشَأْنَا مِن بَعْدِهِمْ قُرُونًا آخَرِينَ
Thumma ansha/na min baAAdihimquroonan akhareen
Hausa
Sa'an kuma Muka ƙãga halittar wasu ƙarnõni dabam daga bayãnsu.
|
Ayah 23:43 الأية
مَا تَسْبِقُ مِنْ أُمَّةٍ أَجَلَهَا وَمَا يَسْتَأْخِرُونَ
Ma tasbiqu min ommatin ajalahawama yasta/khiroon
Hausa
Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
|
Ayah 23:44 الأية
ثُمَّ أَرْسَلْنَا رُسُلَنَا تَتْرَىٰ ۖ كُلَّ مَا جَاءَ أُمَّةً رَّسُولُهَا
كَذَّبُوهُ ۚ فَأَتْبَعْنَا بَعْضَهُم بَعْضًا وَجَعَلْنَاهُمْ أَحَادِيثَ ۚ
فَبُعْدًا لِّقَوْمٍ لَّا يُؤْمِنُونَ
Thumma arsalna rusulana tatrakulla ma jaa ommatan rasooluha
kaththaboohufaatbaAAna baAAdahum baAAdan wajaAAalnahumahadeetha fabuAAdan
liqawmin la yu/minoon
Hausa
Sa'an nan kuma Muka aika da ManzanninMu jẽre a kõda yaushe Manzon wata al'umma
ya jẽ mata, sai su ƙaryata shi, sabõda haka Muka biyar da sãshensu ga sãshe,
kuma Muka sanya su lãbãrun hĩra. To, nĩsa ya tabbata ga mutãne (waɗanda) bã su
yin ĩmãni!
|
Ayah 23:45 الأية
ثُمَّ أَرْسَلْنَا مُوسَىٰ وَأَخَاهُ هَارُونَ بِآيَاتِنَا وَسُلْطَانٍ مُّبِينٍ
Thumma arsalna moosa waakhahuharoona bi-ayatina wasultaninmubeen
Hausa
Sa'an nan kuma Muka aika Mũsã da ɗan'uwansa Hãrũna, game da ãyõyinMu da, dalĩli
bayyananne.
|
Ayah 23:46 الأية
إِلَىٰ فِرْعَوْنَ وَمَلَئِهِ فَاسْتَكْبَرُوا وَكَانُوا قَوْمًا عَالِينَ
Ila firAAawna wamala-ihi fastakbaroowakanoo qawman AAaleen
Hausa
Zuwa ga Fir'auna da majalisarsa, sai suka kangara, alhãli sun kasance mutãne ne
marinjãya.
|
Ayah 23:47 الأية
فَقَالُوا أَنُؤْمِنُ لِبَشَرَيْنِ مِثْلِنَا وَقَوْمُهُمَا لَنَا عَابِدُونَ
Faqaloo anu/minu libasharayni mithlinawaqawmuhuma lana AAabidoon
Hausa
Sai suka ce: "Shin, zã Mu yi ĩmãni sabõda wasu mutãne biyu misãlinmu, alhãli
kuwa mutãnensu a gare mu, mãsu bauta ne."
|
Ayah 23:48 الأية
فَكَذَّبُوهُمَا فَكَانُوا مِنَ الْمُهْلَكِينَ
Fakaththaboohuma fakanoomina almuhlakeen
Hausa
Sai suka ƙaryata su sabõda haka suka kasance halakakku.
|
Ayah 23:49 الأية
وَلَقَدْ آتَيْنَا مُوسَى الْكِتَابَ لَعَلَّهُمْ يَهْتَدُونَ
Walaqad atayna moosaalkitaba laAAallahum yahtadoon
Hausa
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã littãfi tsammaninsu zã su shiryu.
|
Ayah 23:50 الأية
وَجَعَلْنَا ابْنَ مَرْيَمَ وَأُمَّهُ آيَةً وَآوَيْنَاهُمَا إِلَىٰ رَبْوَةٍ ذَاتِ
قَرَارٍ وَمَعِينٍ
WajaAAalna ibna maryama waommahu ayatanwaawaynahuma ila rabwatin thatiqararin
wamaAAeen
Hausa
Kuma Mun sanya ¦an Maryama, shi da uwarsa wata ãyã Kuma Muka tattara su zuwa ga
wani tsauni ma'abũcin natsuwa da marẽmari.
|
Ayah 23:51 الأية
يَا أَيُّهَا الرُّسُلُ كُلُوا مِنَ الطَّيِّبَاتِ وَاعْمَلُوا صَالِحًا ۖ إِنِّي
بِمَا تَعْمَلُونَ عَلِيمٌ
Ya ayyuha arrusulukuloo mina attayyibati waAAmaloo salihaninnee bima taAAmaloona
AAaleem
Hausa
Yã ku Manzanni! Ku ci daga abũbuwa mãsu dãɗi kuma ku aikata aikin ƙwarai. Lalle
Nĩga abin da kuke aikatãwa, Masani ne.
|
Ayah 23:52 الأية
وَإِنَّ هَٰذِهِ أُمَّتُكُمْ أُمَّةً وَاحِدَةً وَأَنَا رَبُّكُمْ فَاتَّقُونِ
Wa-inna hathihi ommatukum ommatan wahidatanwaana rabbukum fattaqoon
Hausa
Kuma lalle ne, wannan al'ummarku ce, al'umma guda, kuma Nĩ, Ubangijinku ne, sai
ku bĩ Ni da taƙawa.
|
Ayah 23:53 الأية
فَتَقَطَّعُوا أَمْرَهُم بَيْنَهُمْ زُبُرًا ۖ كُلُّ حِزْبٍ بِمَا لَدَيْهِمْ
فَرِحُونَ
FataqattaAAoo amrahum baynahumzuburan kullu hizbin bima ladayhim farihoon
Hausa
Sai (al'ummar) suka yanyanke al'amarinsu a tsakãninsu guntu-guntu, kõwace
ƙungiya sunã mãsu farin ciki da abin da yake a gare su.
|
Ayah 23:54 الأية
فَذَرْهُمْ فِي غَمْرَتِهِمْ حَتَّىٰ حِينٍ
Fatharhum fee ghamratihim hattaheen
Hausa
To, ka bar su a cikin ɓatarsu har a wani lõkaci.
|
Ayah 23:55 الأية
أَيَحْسَبُونَ أَنَّمَا نُمِدُّهُم بِهِ مِن مَّالٍ وَبَنِينَ
Ayahsaboona annama numidduhumbihi min malin wabaneen
Hausa
Shin, sunã zaton cẽwa abin da Muke taimakon su da shi daga dũkiya da ɗiya,
|
Ayah 23:56 الأية
نُسَارِعُ لَهُمْ فِي الْخَيْرَاتِ ۚ بَل لَّا يَشْعُرُونَ
NusariAAu lahum fee alkhayratibal la yashAAuroon
Hausa
Munã yi musu gaggãwa ne a cikin alhẽrõri?
|
Ayah 23:57 الأية
إِنَّ الَّذِينَ هُم مِّنْ خَشْيَةِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ
Inna allatheena hum min khashyatirabbihim mushfiqoon
Hausa
Lalle ne waɗanda suke mãsu sauna sabo da tsõron Ubangijinsu,
|
Ayah 23:58 الأية
وَالَّذِينَ هُم بِآيَاتِ رَبِّهِمْ يُؤْمِنُونَ
Wallatheena hum bi-ayatirabbihim yu/minoon
Hausa
Da waɗanda suke, game da ãyõyin Ubangijinsu sunã ĩmãni,
|
Ayah 23:59 الأية
وَالَّذِينَ هُم بِرَبِّهِمْ لَا يُشْرِكُونَ
Wallatheena hum birabbihim layushrikoon
Hausa
Da waɗanda suke game da Ubangijinsu bã su yin shirki,
|
Ayah 23:60 الأية
وَالَّذِينَ يُؤْتُونَ مَا آتَوا وَّقُلُوبُهُمْ وَجِلَةٌ أَنَّهُمْ إِلَىٰ
رَبِّهِمْ رَاجِعُونَ
Wallatheena yu/toona maataw waquloobuhum wajilatun annahum ila rabbihim
rajiAAoon
Hausa
Da waɗanda ke bãyar da abin da suka bãyar, alhãli kuwa zukãtansu sunã tsõrace
dõmin sunã kõmãwa zuwa ga Ubangijinsu,
|
Ayah 23:61 الأية
أُولَٰئِكَ يُسَارِعُونَ فِي الْخَيْرَاتِ وَهُمْ لَهَا سَابِقُونَ
Ola-ika yusariAAoona feealkhayrati wahum laha sabiqoon
Hausa
Waɗancan sunã gaggãwar tsẽre a cikin ayyukan alhẽri, alhãli kuwa sunã mãsu
tsẽrẽwa zuwa gare su (ayyukan alhẽri).
|
Ayah 23:62 الأية
وَلَا نُكَلِّفُ نَفْسًا إِلَّا وُسْعَهَا ۖ وَلَدَيْنَا كِتَابٌ يَنطِقُ
بِالْحَقِّ ۚ وَهُمْ لَا يُظْلَمُونَ
Wala nukallifu nafsan illawusAAaha waladayna kitabun yantiqu bilhaqqiwahum la
yuthlamoon
Hausa
Kuma bã Mu kallafa wa rai fãce abin iyawarsa, kuma a wurinMu akwai wani Littãfi
wanda yake magana da gakiya, kuma sũ bã a zãluntar su.
|
Ayah 23:63 الأية
بَلْ قُلُوبُهُمْ فِي غَمْرَةٍ مِّنْ هَٰذَا وَلَهُمْ أَعْمَالٌ مِّن دُونِ ذَٰلِكَ
هُمْ لَهَا عَامِلُونَ
Bal quloobuhum fee ghamratin min hathawalahum aAAmalun min dooni thalika hum
lahaAAamiloon
Hausa
Ã'a, zukãtansu sunã cikin jãhilci daga wannan (magana), kuma sunã da waɗansu
ayyuka, baicin wancan, sũ a gare su,mãsu aikatãwa ne.
|
Ayah 23:64 الأية
حَتَّىٰ إِذَا أَخَذْنَا مُتْرَفِيهِم بِالْعَذَابِ إِذَا هُمْ يَجْأَرُونَ
Hatta itha akhathnamutrafeehim bilAAathabi itha hum yaj-aroon
Hausa
Har idan Mun kãma mani'imtansu da azãba, sai gã su sunã hargõwa.
|
Ayah 23:65 الأية
لَا تَجْأَرُوا الْيَوْمَ ۖ إِنَّكُم مِّنَّا لَا تُنصَرُونَ
La taj-aroo alyawma innakum minnala tunsaroon
Hausa
Kada ku yi hargowa a yau, lalle ne kũ, daga gare Mu bã a taimakon ku.
|
Ayah 23:66 الأية
قَدْ كَانَتْ آيَاتِي تُتْلَىٰ عَلَيْكُمْ فَكُنتُمْ عَلَىٰ أَعْقَابِكُمْ
تَنكِصُونَ
Qad kanat ayatee tutlaAAalaykum fakuntum AAala aAAqabikum tankisoon
Hausa
Lalle ne, ãyõyĩNa sun kasance anã karãtun su a kanku, sai kuka kasance, a kan
dugãduganku, kunã kõmãwa bãya.
|
Ayah 23:67 الأية
مُسْتَكْبِرِينَ بِهِ سَامِرًا تَهْجُرُونَ
Mustakbireena bihi samiran tahjuroon
Hausa
Kunã mãsu girman kai gare shi (Annabi), da hĩrã kunã alfãsha.
|
Ayah 23:68 الأية
أَفَلَمْ يَدَّبَّرُوا الْقَوْلَ أَمْ جَاءَهُم مَّا لَمْ يَأْتِ آبَاءَهُمُ
الْأَوَّلِينَ
Afalam yaddabbaroo alqawla am jaahumma lam ya/ti abaahumu al-awwaleen
Hausa
Shin fa, ba su yi ta'ammalin maganar (Alƙur'ãni) ba, kõ abin da bai jẽ wa
ubanninsu na farko ba ne ya jẽ musu?
|
Ayah 23:69 الأية
أَمْ لَمْ يَعْرِفُوا رَسُولَهُمْ فَهُمْ لَهُ مُنكِرُونَ
Am lam yaAArifoo rasoolahum fahum lahumunkiroon
Hausa
Kõ ba su san Manzonsu ba ne dõmin haka suke mãsu musu a gare shi?
|
Ayah 23:70 الأية
أَمْ يَقُولُونَ بِهِ جِنَّةٌ ۚ بَلْ جَاءَهُم بِالْحَقِّ وَأَكْثَرُهُمْ لِلْحَقِّ
كَارِهُونَ
Am yaqooloona bihi jinnatun bal jaahumbilhaqqi waaktharuhum lilhaqqi karihoon
Hausa
Kõ sunã cẽwa, "Akwai hauka gare shi?" Ã'a, yã zo musu da gaskiya, alhãli kuwa
mafi yawansu, ga gaskiya, mãsu ƙi ne.
|
Ayah 23:71 الأية
وَلَوِ اتَّبَعَ الْحَقُّ أَهْوَاءَهُمْ لَفَسَدَتِ السَّمَاوَاتُ وَالْأَرْضُ
وَمَن فِيهِنَّ ۚ بَلْ أَتَيْنَاهُم بِذِكْرِهِمْ فَهُمْ عَن ذِكْرِهِم
مُّعْرِضُونَ
Walawi ittabaAAa alhaqqu ahwaahumlafasadati assamawatu wal-arduwaman feehinna
bal ataynahum bithikrihim fahum AAanthikrihim muAAridoon
Hausa
Kuma dã gaskiya (Alƙur'ãni) yã bi son zuciyoyinsu, haƙĩƙa dã sammai da ƙasa da
wanda yake a cikinsu sun ɓãci. Ã'a, Mun tafo musu da ambaton (darajar) su, sa'an
nan sũ daga barin ambaton su mãsu bijirẽwa ne, bijirẽwa.
|
Ayah 23:72 الأية
أَمْ تَسْأَلُهُمْ خَرْجًا فَخَرَاجُ رَبِّكَ خَيْرٌ ۖ وَهُوَ خَيْرُ الرَّازِقِينَ
Am tas-aluhum kharjan fakharajurabbika khayrun wahuwa khayru arraziqeen
Hausa
Kõ kanã tambayar su wani harãji ne (a kan iyar da Manzanci a gare su)? To,
harãjin Ubangijinka ne mafi alhẽri kuma Shĩ ne Mafi alhẽrin mãsu ciyarwa.
|
Ayah 23:73 الأية
وَإِنَّكَ لَتَدْعُوهُمْ إِلَىٰ صِرَاطٍ مُّسْتَقِيمٍ
Wa-innaka latadAAoohum ila siratinmustaqeem
Hausa
Kuma lalle ne kai haƙĩƙa kanã kiran su zuwa ga hanya madaidaiciya.
|
Ayah 23:74 الأية
وَإِنَّ الَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِالْآخِرَةِ عَنِ الصِّرَاطِ لَنَاكِبُونَ
Wa-inna allatheena layu/minoona bil-akhirati AAani assiratilanakiboon
Hausa
Kuma lalle waɗanda ba su yi ĩmãni da Lãhira ba mãsu karkacẽwa daga hanya ne.
|
Ayah 23:75 الأية
وَلَوْ رَحِمْنَاهُمْ وَكَشَفْنَا مَا بِهِم مِّن ضُرٍّ لَّلَجُّوا فِي
طُغْيَانِهِمْ يَعْمَهُونَ
Walaw rahimnahum wakashafnama bihim min durrin lalajjoo fee
tughyanihimyaAAmahoon
Hausa
Kuma dã Mun ji tausayinsu, kuma Muka kuranye musu abin da yake tãre da su na
cũta, lalle ne dã sun yi zurfi a cikin ɓatarsu, sunã ɗimuwa.
|
Ayah 23:76 الأية
وَلَقَدْ أَخَذْنَاهُم بِالْعَذَابِ فَمَا اسْتَكَانُوا لِرَبِّهِمْ وَمَا
يَتَضَرَّعُونَ
Walaqad akhathnahum bilAAathabifama istakanoo lirabbihim wama yatadarraAAoon
Hausa
Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã kãma su da azãba sai dai ba su saukar da kai ba, ga
Ubangijinsu, kama bã su yin tawãli'u.
|
Ayah 23:77 الأية
حَتَّىٰ إِذَا فَتَحْنَا عَلَيْهِم بَابًا ذَا عَذَابٍ شَدِيدٍ إِذَا هُمْ فِيهِ
مُبْلِسُونَ
Hatta itha fatahnaAAalayhim baban tha AAathabin shadeedin ithahum feehi
mublisoon
Hausa
Har idan Mun bũɗe, akansu, wata ƙõfa mai azãba mai tsanani sai gã su a cikinta
sunã mãsu mugi.
|
Ayah 23:78 الأية
وَهُوَ الَّذِي أَنشَأَ لَكُمُ السَّمْعَ وَالْأَبْصَارَ وَالْأَفْئِدَةَ ۚ
قَلِيلًا مَّا تَشْكُرُونَ
Wahuwa allathee anshaa lakumu assamAAawal-absara wal-af-idata qaleelan
matashkuroon
Hausa
Kuma Shi ne Wanda Ya ƙãga halittar ji da gani da zukãta dominku. Kaɗan ƙwarai
kuke gõdẽwa.
|
Ayah 23:79 الأية
وَهُوَ الَّذِي ذَرَأَكُمْ فِي الْأَرْضِ وَإِلَيْهِ تُحْشَرُونَ
Wahuwa allathee tharaakum feeal-ardi wa-ilayhi tuhsharoon
Hausa
Kuma Shĩ ne Ya halitta ku a cikin ƙasa, kuma zuwa gare Shi ake tãyar da ku.
|
Ayah 23:80 الأية
وَهُوَ الَّذِي يُحْيِي وَيُمِيتُ وَلَهُ اخْتِلَافُ اللَّيْلِ وَالنَّهَارِ ۚ
أَفَلَا تَعْقِلُونَ
Wahuwa allathee yuhyeewayumeetu walahu ikhtilafu allayli wannahariafala
taAAqiloon
Hausa
Kuma Shĩ ne Wanda Yake rãyarwa, kuma Yanã matarwa, kuma a gare Shi ne sãɓawar
dare da yini take. Shin, to, bã zã ku hankalta ba?
|
Ayah 23:81 الأية
بَلْ قَالُوا مِثْلَ مَا قَالَ الْأَوَّلُونَ
Bal qaloo mithla ma qalaal-awwaloon
Hausa
Ã'a, sun faɗi misãlin abin da na farko suka faɗa.
|
Ayah 23:82 الأية
قَالُوا أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
Qaloo a-itha mitnawakunna turaban waAAithamana-inna lamabAAoothoon
Hausa
Suka ce: "Shin idan mun mutu kuma muka kasance turɓaya da ƙasũsuwa shin lal1e ne
mu haƙĩƙa waɗanda ake tãyarwa ne?
|
Ayah 23:83 الأية
لَقَدْ وُعِدْنَا نَحْنُ وَآبَاؤُنَا هَٰذَا مِن قَبْلُ إِنْ هَٰذَا إِلَّا
أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ
Laqad wuAAidna nahnu waabaonahatha min qablu in hatha illa asateerual-awwaleen
Hausa
"Lalle ne, haƙĩƙa, an yi mana wa'adi, mũ da ubanninmu ga wannan a gabãni, wannan
abu bai zama kõme ba, fãce tãtsũniyõyin na farko."
|
Ayah 23:84 الأية
قُل لِّمَنِ الْأَرْضُ وَمَن فِيهَا إِن كُنتُمْ تَعْلَمُونَ
Qul limani al-ardu waman feehain kuntum taAAlamoon
Hausa
Ka ce: "Wane ne da mulkin ƙasa da wanda ke a cikinta, idan kun kasance kunã
sani?"
|
Ayah 23:85 الأية
سَيَقُولُونَ لِلَّهِ ۚ قُلْ أَفَلَا تَذَكَّرُونَ
Sayaqooloona lillahi qul afalatathakkaroon
Hausa
Zã su ce: "Ta Allah ne." Ka ce, "Shin, to, bã zã ku yi tunãni ba?"
|
Ayah 23:86 الأية
قُلْ مَن رَّبُّ السَّمَاوَاتِ السَّبْعِ وَرَبُّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ
Qul man rabbu assamawatiassabAAi warabbu alAAarshi alAAatheem
Hausa
Ka ce: "Wãne ne Ubangijin sammai bakwai kuma Ubangijin Al'arshi mai girma?"
|
Ayah 23:87 الأية
سَيَقُولُونَ لِلَّهِ ۚ قُلْ أَفَلَا تَتَّقُونَ
Sayaqooloona lillahi qul afalatattaqoon
Hausa
Zã su ce: "Na Allah ne." Ka ce, "Shin, to, bã zã ku bĩ Shi da taƙawa ba?"
|
Ayah 23:88 الأية
قُلْ مَن بِيَدِهِ مَلَكُوتُ كُلِّ شَيْءٍ وَهُوَ يُجِيرُ وَلَا يُجَارُ عَلَيْهِ
إِن كُنتُمْ تَعْلَمُونَ
Qul man biyadihi malakootu kulli shay-inwahuwa yujeeru wala yujaru AAalayhi in
kuntumtaAAlamoon
Hausa
Ka ce: "Wãne ne ga hannunsa mallakar kõwane abu take alhãli kuwa shi yanã
tsarẽwar wani, kuma ba a tsare kõwa daga gare shi, idan kun kasance kunã sani?"
|
Ayah 23:89 الأية
سَيَقُولُونَ لِلَّهِ ۚ قُلْ فَأَنَّىٰ تُسْحَرُونَ
Sayaqooloona lillahi qul faannatusharoon
Hausa
Zã su ce: "Ga Allah yake." Ka ce: "To, yãya ake sihirce ku?"
|
Ayah 23:90 الأية
بَلْ أَتَيْنَاهُم بِالْحَقِّ وَإِنَّهُمْ لَكَاذِبُونَ
Bal ataynahum bilhaqqiwa-innahum lakathiboon
Hausa
Ã'a, Mun zo musu da gaskiya, kuma lalle ne sũ, haƙĩƙa, maƙaryata ne.
|
Ayah 23:91 الأية
مَا اتَّخَذَ اللهُ مِن وَلَدٍ وَمَا كَانَ مَعَهُ مِنْ إِلَٰهٍ ۚ إِذًا
لَّذَهَبَ كُلُّ إِلَٰهٍ بِمَا خَلَقَ وَلَعَلَا بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ ۚ
سُبْحَانَ اللهِ عَمَّا يَصِفُونَ
Ma ittakhatha Allahumin waladin wama kana maAAahu min ilahin ithanlathahaba
kullu ilahin bima khalaqa walaAAalabaAAduhum AAala baAAdin subhana AllahiAAamma
yasifoon
Hausa
Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma bãbu wani abin bautãwa tãre da Shi.
Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne dã kõwane abin bautawar
ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, dã waɗansu sun rinjãya a kan
waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantãwa.
|
Ayah 23:92 الأية
عَالِمِ الْغَيْبِ وَالشَّهَادَةِ فَتَعَالَىٰ عَمَّا يُشْرِكُونَ
AAalimi alghaybi washshahadatifataAAala AAamma yushrikoon
Hausa
Masanin ɓõye da bayyane. sa'an nan Ya ɗaukaka daga barin abin da suke yi na
shirka.
|
Ayah 23:93 الأية
قُل رَّبِّ إِمَّا تُرِيَنِّي مَا يُوعَدُونَ
Qul rabbi imma turiyannee mayooAAadoon
Hausa
Ka ce: "Yã Ubangijina! Ko dai Ka nũna mini abin da ake yi musu wa'adi da shi."
|
Ayah 23:94 الأية
رَبِّ فَلَا تَجْعَلْنِي فِي الْقَوْمِ الظَّالِمِينَ
Rabbi fala tajAAalnee fee alqawmi aththalimeen
Hausa
"Yã Ubangijina, to, kada Ka sanya ni a cikin mutãne azzãlumai."
|
Ayah 23:95 الأية
وَإِنَّا عَلَىٰ أَن نُّرِيَكَ مَا نَعِدُهُمْ لَقَادِرُونَ
Wa-inna AAala an nuriyaka manaAAiduhum laqadiroon
Hausa
Kuma lalle ne Mũ haƙĩƙa Mãsu iyawa ne a kan Mu nũna maka abin da Muke yi musu
wa'adi da shi.
|
Ayah 23:96 الأية
ادْفَعْ بِالَّتِي هِيَ أَحْسَنُ السَّيِّئَةَ ۚ نَحْنُ أَعْلَمُ بِمَا يَصِفُونَ
IdfaAA billatee hiya ahsanu assayyi-atanahnu aAAlamu bima yasifoon
Hausa
Ka tunkuɗe cũta da wadda take ita ce mafi kyau. Mũ neMafi sani game da abin da
suke siffantãwa.
|
Ayah 23:97 الأية
وَقُل رَّبِّ أَعُوذُ بِكَ مِنْ هَمَزَاتِ الشَّيَاطِينِ
Waqul rabbi aAAoothu bika min hamazatiashshayateen
Hausa
Ka ce: "Yã Ubangijĩna, inã nẽman tsari da Kai daga fizge-fizgen Shaiɗãnu."
|
Ayah 23:98 الأية
وَأَعُوذُ بِكَ رَبِّ أَن يَحْضُرُونِ
WaaAAoothu bika rabbi an yahduroon
Hausa
"Kuma inã nẽman tsari da Kai, ya Ubangijĩna! Dõmin kada su halarto ni, "
|
Ayah 23:99 الأية
حَتَّىٰ إِذَا جَاءَ أَحَدَهُمُ الْمَوْتُ قَالَ رَبِّ ارْجِعُونِ
Hatta itha jaa ahadahumualmawtu qala rabbi irjiAAoon
Hausa
Har idan mutuwa ta jẽ wa ɗayansu, sai ya ce: "Yã Ubangijina, Ku mayar da ni
(dũniya)."
|
Ayah 23:100 الأية
لَعَلِّي أَعْمَلُ صَالِحًا فِيمَا تَرَكْتُ ۚ كَلَّا ۚ إِنَّهَا كَلِمَةٌ هُوَ
قَائِلُهَا ۖ وَمِن وَرَائِهِم بَرْزَخٌ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ
LaAAallee aAAmalu salihanfeema taraktu kalla innaha kalimatun huwa qa-iluhawamin
wara-ihim barzakhun ila yawmi yubAAathoon
Hausa
"Tsammãnina in aikata aiki na ƙwarai cikin abin da na bari." Kayya! Lalle ne ita
kalma ce, shĩ ne mafaɗinta, alhãli kuwa a bãya gare su akwai wani shãmaki har
rãnar da zã a tãyar da su.
|
Ayah 23:101 الأية
فَإِذَا نُفِخَ فِي الصُّورِ فَلَا أَنسَابَ بَيْنَهُمْ يَوْمَئِذٍ وَلَا
يَتَسَاءَلُونَ
Fa-itha nufikha fee assoorifala ansaba baynahum yawma-ithin walayatasaaloon
Hausa
Sa'an nan idan an yi bũsa a cikin ƙaho, to, bãbu dangantakõki a tsakãninsu a
rãnar nan kuma bã zã su tambayi jũnansu ba.
|
Ayah 23:102 الأية
فَمَن ثَقُلَتْ مَوَازِينُهُ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْمُفْلِحُونَ
Faman thaqulat mawazeenuhu faola-ikahumu almuflihoon
Hausa
To, wadanda sikẽlinsu ya yi nauyi, to, waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
|
Ayah 23:103 الأية
وَمَنْ خَفَّتْ مَوَازِينُهُ فَأُولَٰئِكَ الَّذِينَ خَسِرُوا أَنفُسَهُمْ فِي
جَهَنَّمَ خَالِدُونَ
Waman khaffat mawazeenuhu faola-ikaallatheena khasiroo anfusahum fee jahannama
khalidoon
Hausa
Kuma waɗanda sikẽlinsu ya yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasãrar
rãyukansu sunã madawwama a cikin Jahannama.
|
Ayah 23:104 الأية
تَلْفَحُ وُجُوهَهُمُ النَّارُ وَهُمْ فِيهَا كَالِحُونَ
Talfahu wujoohahumu annaruwahum feeha kalihoon
Hausa
Fuskokinsu sunã balbalar wuta, kuma su a cikinta mãsu yãgaggun leɓɓa daga haƙõra
ne.
|
Ayah 23:105 الأية
أَلَمْ تَكُنْ آيَاتِي تُتْلَىٰ عَلَيْكُمْ فَكُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ
Alam takun ayatee tutlaAAalaykum fakuntum biha tukaththiboon
Hausa
"Shin, ayõyĩNa ba su kasance anã karanta su a kanku ba sai kuka kasance game da
su kunã ƙaryatãwa?"
|
Ayah 23:106 الأية
قَالُوا رَبَّنَا غَلَبَتْ عَلَيْنَا شِقْوَتُنَا وَكُنَّا قَوْمًا ضَالِّينَ
Qaloo rabbana ghalabatAAalayna shiqwatuna wakunna qawman dalleen
Hausa
Suka ce: "Yã Ubangijinmu, shaƙãwamiu ce ta rinjãya a kanmu, kuma mun kasance
mutãne ɓatattu."
|
Ayah 23:107 الأية
رَبَّنَا أَخْرِجْنَا مِنْهَا فَإِنْ عُدْنَا فَإِنَّا ظَالِمُونَ
Rabbana akhrijna minhafa-in AAudna fa-inna thalimoon
Hausa
"Yã Ubangjinmu! Ka fitar da mu daga gare ta, sa'an nan idan mun kõma, to, lalle
ne, mũ ne mãsu zãlunci."
|
Ayah 23:108 الأية
قَالَ اخْسَئُوا فِيهَا وَلَا تُكَلِّمُونِ
Qala ikhsaoo feeha walatukallimoon
Hausa
Ya ce: "Ku tafi (da wulãkanci) a cikinta. Kada ku yi Mini magana."
|
Ayah 23:109 الأية
إِنَّهُ كَانَ فَرِيقٌ مِّنْ عِبَادِي يَقُولُونَ رَبَّنَا آمَنَّا فَاغْفِرْ لَنَا
وَارْحَمْنَا وَأَنتَ خَيْرُ الرَّاحِمِينَ
Innahu kana fareequn min AAibadeeyaqooloona rabbana amanna faghfirlana warhamna
waanta khayru arrahimeen
Hausa
Lalle ne waɗansu ƙungiyoyi daga bãyiNa sun kasance sunã cẽwa, "Yã Ubangijinmu!
Mun yi ĩmãni, sai Ka gãfarta mana, kuma Ka yi mana rahama, kuma Kai ne Mafi
alhẽrin mãsu tausayi."
|
Ayah 23:110 الأية
فَاتَّخَذْتُمُوهُمْ سِخْرِيًّا حَتَّىٰ أَنسَوْكُمْ ذِكْرِي وَكُنتُم مِّنْهُمْ
تَضْحَكُونَ
Fattakhathtumoohumsikhriyyan hatta ansawkum thikree wakuntumminhum tadhakoon
Hausa
Sai kuka riƙe su lẽburõri har suka mantar da ku ambatõNa kuma kun kasance, daga
gare su kuke yin dãriya.
|
Ayah 23:111 الأية
إِنِّي جَزَيْتُهُمُ الْيَوْمَ بِمَا صَبَرُوا أَنَّهُمْ هُمُ الْفَائِزُونَ
Innee jazaytuhumu alyawma bima sabarooannahum humu alfa-izoon
Hausa
Lalle ne Nĩ Inã sãka musu a yau, sabõda abin da suka yi wa haƙuri. Dõmin lalle
ne sũ sũ ne mãsu sãmun babban rabo.
|
Ayah 23:112 الأية
قَالَ كَمْ لَبِثْتُمْ فِي الْأَرْضِ عَدَدَ سِنِينَ
Qala kam labithtum fee al-ardiAAadada sineen
Hausa
Ya ce: "Nawa kuka zauna a cikin ƙasa na ƙidãyar shẽkaru?"
|
Ayah 23:113 الأية
قَالُوا لَبِثْنَا يَوْمًا أَوْ بَعْضَ يَوْمٍ فَاسْأَلِ الْعَادِّينَ
Qaloo labithna yawman aw baAAdayawmin fas-ali alAAaddeen
Hausa
Suka ce: "Mun zauna a yini ɗaya ko rabin yini, sai ka tambayi mãsu ƙidãyãwa."
|
Ayah 23:114 الأية
قَالَ إِن لَّبِثْتُمْ إِلَّا قَلِيلًا ۖ لَّوْ أَنَّكُمْ كُنتُمْ تَعْلَمُونَ
Qala in labithtum illaqaleelan law annakum kuntum taAAlamoon
Hausa
Ya ce: "Ba ku zauna ba fãce kaɗan, dã dai kun kasance kunã sani."
|
Ayah 23:115 الأية
أَفَحَسِبْتُمْ أَنَّمَا خَلَقْنَاكُمْ عَبَثًا وَأَنَّكُمْ إِلَيْنَا لَا
تُرْجَعُونَ
Afahasibtum annama khalaqnakumAAabathan waannakum ilayna la turjaAAoon
Hausa
"Shin, to, kun yi zaton cẽwa Mun halitta ku ne da wãsa kuma lalle ku, zuwa gare
Mu, bã zã ku kõmo ba?"
|
Ayah 23:116 الأية
فَتَعَالَى اللهُ الْمَلِكُ الْحَقُّ ۖ لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ رَبُّ الْعَرْشِ
الْكَرِيمِ
FataAAala Allahualmaliku alhaqqu la ilaha illa huwarabbu alAAarshi alkareem
Hausa
Allah Mamallaki gaskiya, Yã ɗaukaka. Bãbu abin bautãwa, fãce Shi. Shĩ ne
Ubangijin Al'arshi, mai daraja.
|
Ayah 23:117 الأية
وَمَن يَدْعُ مَعَ اللهِ إِلَٰهًا آخَرَ لَا بُرْهَانَ لَهُ بِهِ فَإِنَّمَا
حِسَابُهُ عِندَ رَبِّهِ ۚ إِنَّهُ لَا يُفْلِحُ الْكَافِرُونَ
Waman yadAAu maAAa Allahi ilahanakhara la burhana lahu bihi fa-innamahisabuhu
AAinda rabbihi innahu la yuflihualkafiroon
Hausa
Kuma wanda ya kira, tãre da Allah, waɗansu abũbuwan bautãwa na dabam, bã yanã da
wani dalĩli game da shĩ (kiran) ba, to hisãbinsa yanã wurin Ubangijinsa kawai.
Lalle ne, kãfirai bã su cin nasara.
|
Ayah 23:118 الأية
وَقُل رَّبِّ اغْفِرْ وَارْحَمْ وَأَنتَ خَيْرُ الرَّاحِمِينَ
Waqul rabbi ighfir warhamwaanta khayru arrahimeen
Hausa
Kuma ka ce: "Yã Ubangijina! Ka yi gãfara, Ka yi rahama, kuma Kai ne Mafi alhẽrin
mãsu rahama."
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|