1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
يَا أَيُّهَا الْمُدَّثِّرُ
Ya ayyuha almuddaththir
Hausa
Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.
|
Ayah 74:2 الأية
قُمْ فَأَنذِرْ
Qum faanthir
Hausa
Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi
|
Ayah 74:3 الأية
وَرَبَّكَ فَكَبِّرْ
Warabbaka fakabbir
Hausa
Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,
|
Ayah 74:4 الأية
وَثِيَابَكَ فَطَهِّرْ
Wathiyabaka fatahhir
Hausa
Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,
|
Ayah 74:5 الأية
وَالرُّجْزَ فَاهْجُرْ
Warrujza fahjur
Hausa
Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.
|
Ayah 74:6 الأية
وَلَا تَمْنُن تَسْتَكْثِرُ
Wala tamnun tastakthir
Hausa
Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri
|
Ayah 74:7 الأية
وَلِرَبِّكَ فَاصْبِرْ
Walirabbika fasbir
Hausa
Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure
|
Ayah 74:8 الأية
فَإِذَا نُقِرَ فِي النَّاقُورِ
Fa-itha nuqira fee annaqoor
Hausa
To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.
|
Ayah 74:9 الأية
فَذَٰلِكَ يَوْمَئِذٍ يَوْمٌ عَسِيرٌ
Fathalika yawma-ithin yawmunAAaseer
Hausa
To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya
|
Ayah 74:10 الأية
عَلَى الْكَافِرِينَ غَيْرُ يَسِيرٍ
AAala alkafireena ghayruyaseer
Hausa
A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.
|
Ayah 74:11 الأية
ذَرْنِي وَمَنْ خَلَقْتُ وَحِيدًا
Tharnee waman khalaqtu waheeda
Hausa
Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,
|
Ayah 74:12 الأية
وَجَعَلْتُ لَهُ مَالًا مَّمْدُودًا
WajaAAaltu lahu malan mamdooda
Hausa
Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya
|
Ayah 74:13 الأية
وَبَنِينَ شُهُودًا
Wabaneena shuhooda
Hausa
Da ɗiyã halartattu,
|
Ayah 74:14 الأية
وَمَهَّدتُّ لَهُ تَمْهِيدًا
Wamahhadtu lahu tamheeda
Hausa
Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.
|
Ayah 74:15 الأية
ثُمَّ يَطْمَعُ أَنْ أَزِيدَ
Thumma yatmaAAu an azeed
Hausa
Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!
|
Ayah 74:16 الأية
كَلَّا ۖ إِنَّهُ كَانَ لِآيَاتِنَا عَنِيدًا
Kalla innahu kana li-ayatinaAAaneeda
Hausa
Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.
|
Ayah 74:17 الأية
سَأُرْهِقُهُ صَعُودًا
Saorhiquhu saAAooda
Hausa
Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.
|
Ayah 74:18 الأية
إِنَّهُ فَكَّرَ وَقَدَّرَ
Innahu fakkara waqaddar
Hausa
Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da
Alƙur'ãni)
|
Ayah 74:19 الأية
فَقُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ
Faqutila kayfa qaddar
Hausa
Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.
|
Ayah 74:20 الأية
ثُمَّ قُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ
Thumma qutila kayfa qaddar
Hausa
Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.
|
Ayah 74:21 الأية
ثُمَّ نَظَرَ
Thumma nathar
Hausa
Sa'an nan, ya yi tunãni
|
Ayah 74:22 الأية
ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ
Thumma AAabasa wabasar
Hausa
Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.
|
Ayah 74:23 الأية
ثُمَّ أَدْبَرَ وَاسْتَكْبَرَ
Thumma adbara wastakbar
Hausa
Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,
|
Ayah 74:24 الأية
فَقَالَ إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ يُؤْثَرُ
Faqala in hatha illa sihrunyu/thar
Hausa
Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."
|
Ayah 74:25 الأية
إِنْ هَٰذَا إِلَّا قَوْلُ الْبَشَرِ
In hatha illa qawlu albashar
Hausa
"Wannan maganar mutum dai ce."
|
Ayah 74:26 الأية
سَأُصْلِيهِ سَقَرَ
Saosleehi saqar
Hausa
Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.
|
Ayah 74:27 الأية
وَمَا أَدْرَاكَ مَا سَقَرُ
Wama adraka ma saqar
Hausa
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!
|
Ayah 74:28 الأية
لَا تُبْقِي وَلَا تَذَرُ
La tubqee wala tathar
Hausa
Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.
|
Ayah 74:29 الأية
لَوَّاحَةٌ لِّلْبَشَرِ
Lawwahatun lilbashar
Hausa
Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).
|
Ayah 74:30 الأية
عَلَيْهَا تِسْعَةَ عَشَرَ
AAalayha tisAAata AAashar
Hausa
A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.
|
Ayah 74:31 الأية
وَمَا جَعَلْنَا أَصْحَابَ النَّارِ إِلَّا مَلَائِكَةً ۙ وَمَا جَعَلْنَا
عِدَّتَهُمْ إِلَّا فِتْنَةً لِّلَّذِينَ كَفَرُوا لِيَسْتَيْقِنَ الَّذِينَ
أُوتُوا الْكِتَابَ وَيَزْدَادَ الَّذِينَ آمَنُوا إِيمَانًا ۙ وَلَا يَرْتَابَ
الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ وَالْمُؤْمِنُونَ ۙ وَلِيَقُولَ الَّذِينَ فِي
قُلُوبِهِم مَّرَضٌ وَالْكَافِرُونَ مَاذَا أَرَادَ اللهُ بِهَٰذَا مَثَلًا ۚ
كَذَٰلِكَ يُضِلُّ اللهُ مَن يَشَاءُ وَيَهْدِي مَن يَشَاءُ ۚ وَمَا يَعْلَمُ
جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَ ۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكْرَىٰ لِلْبَشَرِ
Wama jaAAalna as-habaannari illa mala-ikatan wamajaAAalna AAiddatahum illa
fitnatan lillatheenakafaroo liyastayqina allatheena ootoo alkitabawayazdada
allatheena amanoo eemananwala yartaba allatheena ootoo alkitabawalmu/minoona
waliyaqoola allatheena feequloobihim maradun walkafiroona mathaarada Allahu
bihatha mathalan kathalikayudillu Allahu man yashao wayahdee man yashaowama
yaAAlamu junooda rabbika illa huwa wamahiya illa thikra lilbashar
Hausa
Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu
sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta
domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su
ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba,
kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ
Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda
Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan
Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce
ga mutum.
|
Ayah 74:32 الأية
كَلَّا وَالْقَمَرِ
Kalla walqamar
Hausa
A'aha! Ina rantsuwa da watã.
|
Ayah 74:33 الأية
وَاللَّيْلِ إِذْ أَدْبَرَ
Wallayli ith adbar
Hausa
Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.
|
Ayah 74:34 الأية
وَالصُّبْحِ إِذَا أَسْفَرَ
Wassubhi ithaasfar
Hausa
Da sãfiya idan ta wãye.
|
Ayah 74:35 الأية
إِنَّهَا لَإِحْدَى الْكُبَرِ
Innaha la-ihda alkubar
Hausa
Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.
|
Ayah 74:36 الأية
نَذِيرًا لِّلْبَشَرِ
Natheeran lilbashar
Hausa
Mai gargaɗĩ ce ga mutum.
|
Ayah 74:37 الأية
لِمَن شَاءَ مِنكُمْ أَن يَتَقَدَّمَ أَوْ يَتَأَخَّرَ
Liman shaa minkum an yataqaddama awyataakhkhar
Hausa
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.
|
Ayah 74:38 الأية
كُلُّ نَفْسٍ بِمَا كَسَبَتْ رَهِينَةٌ
Kullu nafsin bima kasabat raheena
Hausa
Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.
|
Ayah 74:39 الأية
إِلَّا أَصْحَابَ الْيَمِينِ
Illa as-haba alyameen
Hausa
Fãce mutãnen dãma.
|
Ayah 74:40 الأية
فِي جَنَّاتٍ يَتَسَاءَلُونَ
Fee jannatin yatasaaloon
Hausa
A cikin Aljanna suna tambayar jũna.
|
Ayah 74:41 الأية
عَنِ الْمُجْرِمِينَ
AAani almujrimeen
Hausa
Game da mãsu laifi.
|
Ayah 74:42 الأية
مَا سَلَكَكُمْ فِي سَقَرَ
Ma salakakum fee saqar
Hausa
(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"
|
Ayah 74:43 الأية
قَالُوا لَمْ نَكُ مِنَ الْمُصَلِّينَ
Qaloo lam naku mina almusalleen
Hausa
Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."
|
Ayah 74:44 الأية
وَلَمْ نَكُ نُطْعِمُ الْمِسْكِينَ
Walam naku nutAAimu almiskeen
Hausa
"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."
|
Ayah 74:45 الأية
وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ الْخَائِضِينَ
Wakunna nakhoodu maAAa alkha-ideen
Hausa
"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."
|
Ayah 74:46 الأية
وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوْمِ الدِّينِ
Wakunna nukaththibu biyawmi addeen
Hausa
"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."
|
Ayah 74:47 الأية
حَتَّىٰ أَتَانَا الْيَقِينُ
Hatta atanaalyaqeen
Hausa
"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."
|
Ayah 74:48 الأية
فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَاعَةُ الشَّافِعِينَ
Fama tanfaAAuhum shafaAAatu ashshafiAAeen
Hausa
Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.
|
Ayah 74:49 الأية
فَمَا لَهُمْ عَنِ التَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ
Fama lahum AAani attathkiratimuAArideen
Hausa
Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.
|
Ayah 74:50 الأية
كَأَنَّهُمْ حُمُرٌ مُّسْتَنفِرَةٌ
Kaannahum humurun mustanfira
Hausa
Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.
|
Ayah 74:51 الأية
فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍ
Farrat min qaswara
Hausa
Sun gudu daga zãki.
|
Ayah 74:52 الأية
بَلْ يُرِيدُ كُلُّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًا مُّنَشَّرَةً
Bal yureedu kullu imri-in minhum an yu/tasuhufan munashshara
Hausa
A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa)ana
wãtsãwa
|
Ayah 74:53 الأية
كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ الْآخِرَةَ
Kalla bal la yakhafoonaal-akhira
Hausa
A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.
|
Ayah 74:54 الأية
كَلَّا إِنَّهُ تَذْكِرَةٌ
Kalla innahu tathkira
Hausa
A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.
|
Ayah 74:55 الأية
فَمَن شَاءَ ذَكَرَهُ
Faman shaa thakarah
Hausa
Dõmin wanda ya so, ya tuna.
|
Ayah 74:56 الأية
وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّا أَن يَشَاءَ اللهُ ۚ هُوَ أَهْلُ التَّقْوَىٰ وَأَهْلُ
الْمَغْفِرَةِ
Wama yathkuroona illaan yashaa Allahu huwa ahlu attaqwawaahlu almaghfirat
Hausa
Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da
taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|