1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَالصَّافَّاتِ صَفًّا
Wassaffati saffa
Hausa
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
|
Ayah 37:2 الأية
فَالزَّاجِرَاتِ زَجْرًا
Fazzajirati zajra
Hausa
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
|
Ayah 37:3 الأية
فَالتَّالِيَاتِ ذِكْرًا
Fattaliyati thikra
Hausa
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
|
Ayah 37:4 الأية
إِنَّ إِلَٰهَكُمْ لَوَاحِدٌ
Inna ilahakum lawahid
Hausa
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
|
Ayah 37:5 الأية
رَّبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ الْمَشَارِقِ
Rabbu assamawati wal-ardiwama baynahuma warabbu almashariq
Hausa
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar
rãnã.
|
Ayah 37:6 الأية
إِنَّا زَيَّنَّا السَّمَاءَ الدُّنْيَا بِزِينَةٍ الْكَوَاكِبِ
Inna zayyanna assamaaaddunya bizeenatin alkawakib
Hausa
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
|
Ayah 37:7 الأية
وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَانٍ مَّارِدٍ
Wahifthan min kulli shaytaninmarid
Hausa
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
|
Ayah 37:8 الأية
لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى الْمَلَإِ الْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ
La yassammaAAoona ila almala-ial-aAAla wayuqthafoona min kulli janib
Hausa
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar
su daga kõwane gẽfe.
|
Ayah 37:9 الأية
دُحُورًا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ
Duhooran walahum AAathabun wasib
Hausa
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
|
Ayah 37:10 الأية
إِلَّا مَنْ خَطِفَ الْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ ثَاقِبٌ
Illa man khatifa alkhatfatafaatbaAAahu shihabun thaqib
Hausa
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
|
Ayah 37:11 الأية
فَاسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَا ۚ إِنَّا خَلَقْنَاهُم
مِّن طِينٍ لَّازِبٍ
Fastaftihim ahum ashaddu khalqan amman khalaqna inna khalaqnahum min teeninlazib
Hausa
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka
halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
|
Ayah 37:12 الأية
بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ
Bal AAajibta wayaskharoon
Hausa
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
|
Ayah 37:13 الأية
وَإِذَا ذُكِّرُوا لَا يَذْكُرُونَ
Wa-itha thukkiroo la yathkuroon
Hausa
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
|
Ayah 37:14 الأية
وَإِذَا رَأَوْا آيَةً يَسْتَسْخِرُونَ
Wa-itha raaw ayatanyastaskhiroon
Hausa
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
|
Ayah 37:15 الأية
وَقَالُوا إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ
Waqaloo in hatha illasihrun mubeen
Hausa
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
|
Ayah 37:16 الأية
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
A-itha mitna wakunnaturaban waAAithaman a-innalamabAAoothoon
Hausa
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa,ashe, lalle mũ
tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
|
Ayah 37:17 الأية
أَوَآبَاؤُنَا الْأَوَّلُونَ
Awa abaona al-awwaloon
Hausa
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
|
Ayah 37:18 الأية
قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَاخِرُونَ
Qul naAAam waantum dakhiroon
Hausa
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
|
Ayah 37:19 الأية
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ
Fa-innama hiya zajratun wahidatunfa-itha hum yanthuroon
Hausa
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
|
Ayah 37:20 الأية
وَقَالُوا يَا وَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ الدِّينِ
Waqaloo ya waylana hathayawmu addeen
Hausa
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
|
Ayah 37:21 الأية
هَٰذَا يَوْمُ الْفَصْلِ الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ
Hatha yawmu alfasli allatheekuntum bihi tukaththiboon
Hausa
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
|
Ayah 37:22 الأية
احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأَزْوَاجَهُمْ وَمَا كَانُوا يَعْبُدُونَ
Ohshuroo allatheena thalamoowaazwajahum wama kanoo yaAAbudoon
Hausa
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã
bautãwa.
|
Ayah 37:23 الأية
مِن دُونِ اللهِ فَاهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَاطِ الْجَحِيمِ
Min dooni Allahi fahdoohum ilasirati aljaheem
Hausa
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
|
Ayah 37:24 الأية
وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْئُولُونَ
Waqifoohum innahum masooloon
Hausa
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
|
Ayah 37:25 الأية
مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ
Ma lakum la tanasaroon
Hausa
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
|
Ayah 37:26 الأية
بَلْ هُمُ الْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ
Bal humu alyawma mustaslimoon
Hausa
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
|
Ayah 37:27 الأية
وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ
Waaqbala baAAduhum AAala baAAdinyatasaaloon
Hausa
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
|
Ayah 37:28 الأية
قَالُوا إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ الْيَمِينِ
Qaloo innakum kuntum ta/toonanaAAani alyameen
Hausa
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka
amince)."
|
Ayah 37:29 الأية
قَالُوا بَل لَّمْ تَكُونُوا مُؤْمِنِينَ
Qaloo bal lam takoonoo mu/mineen
Hausa
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
|
Ayah 37:30 الأية
وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَانٍ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَاغِينَ
Wama kana lanaAAalaykum min sultanin bal kuntum qawman tagheen
Hausa
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne
mãsu kẽtare iyãka."
|
Ayah 37:31 الأية
فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَا ۖ إِنَّا لَذَائِقُونَ
Fahaqqa AAalayna qawlu rabbinainna latha-iqoon
Hausa
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa
ne."
|
Ayah 37:32 الأية
فَأَغْوَيْنَاكُمْ إِنَّا كُنَّا غَاوِينَ
Faaghwaynakum inna kunnaghaween
Hausa
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
|
Ayah 37:33 الأية
فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِي الْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ
Fa-innahum yawma-ithin fee alAAathabimushtarikoon
Hausa
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
|
Ayah 37:34 الأية
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِالْمُجْرِمِينَ
Inna kathalika nafAAalu bilmujrimeen
Hausa
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
|
Ayah 37:35 الأية
إِنَّهُمْ كَانُوا إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَا إِلَٰهَ إِلَّا اللهُ يَسْتَكْبِرُونَ
Innahum kanoo itha qeela lahumla ilaha illa Allahu yastakbiroon
Hausa
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su
dõra girman kai.
|
Ayah 37:36 الأية
وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُو آلِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍ
Wayaqooloona a-inna latarikoo alihatinalishaAAirin majnoon
Hausa
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani
mawãƙi mahaukaci?
|
Ayah 37:37 الأية
بَلْ جَاءَ بِالْحَقِّ وَصَدَّقَ الْمُرْسَلِينَ
Bal jaa bilhaqqi wasaddaqaalmursaleen
Hausa
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
|
Ayah 37:38 الأية
إِنَّكُمْ لَذَائِقُو الْعَذَابِ الْأَلِيمِ
Innakum latha-iqoo alAAathabial-aleem
Hausa
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
|
Ayah 37:39 الأية
وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
Wama tujzawna illa makuntum taAAmaloon
Hausa
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
|
Ayah 37:40 الأية
إِلَّا عِبَادَ اللهِ الْمُخْلَصِينَ
Illa AAibada Allahialmukhlaseen
Hausa
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
|
Ayah 37:41 الأية
أُولَٰئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌ
Ola-ika lahum rizqun maAAloom
Hausa
Waɗannan sunã da abinci sananne.
|
Ayah 37:42 الأية
فَوَاكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ
Fawakihu wahum mukramoon
Hausa
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
|
Ayah 37:43 الأية
فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِ
Fee jannati annaAAeem
Hausa
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
|
Ayah 37:44 الأية
عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَابِلِينَ
AAala sururin mutaqabileen
Hausa
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
|
Ayah 37:45 الأية
يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ
Yutafu AAalayhim bika/sin min maAAeen
Hausa
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
|
Ayah 37:46 الأية
بَيْضَاءَ لَذَّةٍ لِّلشَّارِبِينَ
Baydaa laththatin lishsharibeen
Hausa
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
|
Ayah 37:47 الأية
لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ
La feeha ghawlun walahum AAanha yunzafoon
Hausa
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
|
Ayah 37:48 الأية
وَعِندَهُمْ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ عِينٌ
WaAAindahum qasiratu attarfiAAeen
Hausa
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
|
Ayah 37:49 الأية
كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌ
Kaannahunna baydun maknoon
Hausa
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
|
Ayah 37:50 الأية
فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ
Faaqbala baAAduhum AAala baAAdinyatasaaloon
Hausa
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
|
Ayah 37:51 الأية
قَالَ قَائِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٌ
Qala qa-ilun minhum innee kanalee qareen
Hausa
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a
dũniya)."
|
Ayah 37:52 الأية
يَقُولُ أَإِنَّكَ لَمِنَ الْمُصَدِّقِينَ
Yaqoolu a-innaka lamina almusaddiqeen
Hausa
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
|
Ayah 37:53 الأية
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَدِينُونَ
A-itha mitna wakunnaturaban waAAithaman a-innalamadeenoon
Hausa
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ
tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
|
Ayah 37:54 الأية
قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ
Qala hal antum muttaliAAoon
Hausa
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
|
Ayah 37:55 الأية
فَاطَّلَعَ فَرَآهُ فِي سَوَاءِ الْجَحِيمِ
FattalaAAa faraahu feesawa-i aljaheem
Hausa
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
|
Ayah 37:56 الأية
قَالَ تَاللهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ
Qala tallahi in kidtalaturdeen
Hausa
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
|
Ayah 37:57 الأية
وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ الْمُحْضَرِينَ
Walawla niAAmatu rabbee lakuntu minaalmuhdareen
Hausa
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake
halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
|
Ayah 37:58 الأية
أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ
Afama nahnu bimayyiteen
Hausa
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
|
Ayah 37:59 الأية
إِلَّا مَوْتَتَنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ
Illa mawtatana al-oolawama nahnu bimuAAaththabeen
Hausa
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
|
Ayah 37:60 الأية
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ
Inna hatha lahuwa alfawzu alAAatheem
Hausa
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
|
Ayah 37:61 الأية
لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ الْعَامِلُونَ
Limithli hatha falyaAAmali alAAamiloon
Hausa
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
|
Ayah 37:62 الأية
أَذَٰلِكَ خَيْرٌ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ الزَّقُّومِ
Athalika khayrun nuzulan am shajaratuazzaqqoom
Hausa
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
|
Ayah 37:63 الأية
إِنَّا جَعَلْنَاهَا فِتْنَةً لِّلظَّالِمِينَ
Inna jaAAalnahafitnatan liththalimeen
Hausa
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
|
Ayah 37:64 الأية
إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِي أَصْلِ الْجَحِيمِ
Innaha shajaratun takhruju fee aslialjaheem
Hausa
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
|
Ayah 37:65 الأية
طَلْعُهَا كَأَنَّهُ رُءُوسُ الشَّيَاطِينِ
TalAAuha kaannahu ruoosu ashshayateen
Hausa
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
|
Ayah 37:66 الأية
فَإِنَّهُمْ لَآكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ
Fa-innahum laakiloona minhafamali-oona minha albutoon
Hausa
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga
gare ta.
|
Ayah 37:67 الأية
ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍ
Thumma inna lahum AAalayha lashawbanmin hameem
Hausa
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
|
Ayah 37:68 الأية
ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى الْجَحِيمِ
Thumma inna marjiAAahum la-ila aljaheem
Hausa
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
|
Ayah 37:69 الأية
إِنَّهُمْ أَلْفَوْا آبَاءَهُمْ ضَالِّينَ
Innahum alfaw abaahum dalleen
Hausa
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
|
Ayah 37:70 الأية
فَهُمْ عَلَىٰ آثَارِهِمْ يُهْرَعُونَ
Fahum AAala atharihimyuhraAAoon
Hausa
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
|
Ayah 37:71 الأية
وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ الْأَوَّلِينَ
Walaqad dalla qablahum aktharual-awwaleen
Hausa
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
|
Ayah 37:72 الأية
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ
Walaqad arsalna feehim munthireen
Hausa
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
|
Ayah 37:73 الأية
فَانظُرْ كَيْفَ كَانَ عَاقِبَةُ الْمُنذَرِينَ
Fanthur kayfa kanaAAaqibatu almunthareen
Hausa
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
|
Ayah 37:74 الأية
إِلَّا عِبَادَ اللهِ الْمُخْلَصِينَ
Illa AAibada Allahialmukhlaseen
Hausa
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
|
Ayah 37:75 الأية
وَلَقَدْ نَادَانَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ الْمُجِيبُونَ
Walaqad nadana noohunfalaniAAma almujeeboon
Hausa
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
|
Ayah 37:76 الأية
وَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ
Wanajjaynahu waahlahu mina alkarbialAAatheem
Hausa
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
|
Ayah 37:77 الأية
وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُ هُمُ الْبَاقِينَ
WajaAAalna thurriyyatahu humualbaqeen
Hausa
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
|
Ayah 37:78 الأية
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Watarakna AAalayhi fee al-akhireen
Hausa
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
|
Ayah 37:79 الأية
سَلَامٌ عَلَىٰ نُوحٍ فِي الْعَالَمِينَ
Salamun AAala noohinfee alAAalameen
Hausa
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
|
Ayah 37:80 الأية
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Inna kathalika najzee almuhsineen
Hausa
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
|
Ayah 37:81 الأية
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Innahu min AAibadinaalmu/mineen
Hausa
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
|
Ayah 37:82 الأية
ثُمَّ أَغْرَقْنَا الْآخَرِينَ
Thumma aghraqna al-akhareen
Hausa
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
|
Ayah 37:83 الأية
وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِ لَإِبْرَاهِيمَ
Wa-inna min sheeAAatihi la-ibraheem
Hausa
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
|
Ayah 37:84 الأية
إِذْ جَاءَ رَبَّهُ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ
Ith jaa rabbahu biqalbinsaleem
Hausa
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
|
Ayah 37:85 الأية
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَاذَا تَعْبُدُونَ
Ith qala li-abeehi waqawmihi mathataAAbudoon
Hausa
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
|
Ayah 37:86 الأية
أَئِفْكًا آلِهَةً دُونَ اللهِ تُرِيدُونَ
A-ifkan alihatan doona Allahitureedoon
Hausa
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
|
Ayah 37:87 الأية
فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Fama thannukum birabbialAAalameen
Hausa
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
|
Ayah 37:88 الأية
فَنَظَرَ نَظْرَةً فِي النُّجُومِ
Fanathara nathratanfee annujoom
Hausa
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
|
Ayah 37:89 الأية
فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٌ
Faqala innee saqeem
Hausa
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
|
Ayah 37:90 الأية
فَتَوَلَّوْا عَنْهُ مُدْبِرِينَ
Fatawallaw AAanhu mudbireen
Hausa
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
|
Ayah 37:91 الأية
فَرَاغَ إِلَىٰ آلِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ
Faragha ila alihatihimfaqala ala ta/kuloon
Hausa
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
|
Ayah 37:92 الأية
مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ
Ma lakum la tantiqoon
Hausa
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
|
Ayah 37:93 الأية
فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًا بِالْيَمِينِ
Faragha AAalayhim darban bilyameen
Hausa
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
|
Ayah 37:94 الأية
فَأَقْبَلُوا إِلَيْهِ يَزِفُّونَ
Faaqbaloo ilayhi yaziffoon
Hausa
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
|
Ayah 37:95 الأية
قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ
Qala ataAAbudoona ma tanhitoon
Hausa
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
|
Ayah 37:96 الأية
وَاللهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ
Wallahu khalaqakum wamataAAmaloon
Hausa
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
|
Ayah 37:97 الأية
قَالُوا ابْنُوا لَهُ بُنْيَانًا فَأَلْقُوهُ فِي الْجَحِيمِ
Qaloo ibnoo lahu bunyananfaalqoohu fee aljaheem
Hausa
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
|
Ayah 37:98 الأية
فَأَرَادُوا بِهِ كَيْدًا فَجَعَلْنَاهُمُ الْأَسْفَلِينَ
Faaradoo bihi kaydan fajaAAalnahumual-asfaleen
Hausa
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi
ƙasƙanci.
|
Ayah 37:99 الأية
وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهْدِينِ
Waqala innee thahibun ilarabbee sayahdeen
Hausa
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar
da ni."
|
Ayah 37:100 الأية
رَبِّ هَبْ لِي مِنَ الصَّالِحِينَ
Rabbi hablee mina assaliheen
Hausa
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
|
Ayah 37:101 الأية
فَبَشَّرْنَاهُ بِغُلَامٍ حَلِيمٍ
Fabashsharnahu bighulamin haleem
Hausa
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
|
Ayah 37:102 الأية
فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ السَّعْيَ قَالَ يَا بُنَيَّ إِنِّي أَرَىٰ فِي الْمَنَامِ
أَنِّي أَذْبَحُكَ فَانظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَا أَبَتِ افْعَلْ مَا تُؤْمَرُ
ۖ سَتَجِدُنِي إِن شَاءَ اللهُ مِنَ الصَّابِرِينَ
Falamma balagha maAAahu assaAAyaqala ya bunayya innee ara fee almanamiannee
athbahuka fanthur mathatara qala ya abati ifAAal ma tu/marusatajidunee in shaa
Allahu mina assabireen
Hausa
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã
gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce:
"Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so,
daga mãsu haƙuri."
|
Ayah 37:103 الأية
فَلَمَّا أَسْلَمَا وَتَلَّهُ لِلْجَبِينِ
Falamma aslama watallahuliljabeen
Hausa
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
|
Ayah 37:104 الأية
وَنَادَيْنَاهُ أَن يَا إِبْرَاهِيمُ
Wanadaynahu an ya ibraheem
Hausa
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
|
Ayah 37:105 الأية
قَدْ صَدَّقْتَ الرُّؤْيَا ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Qad saddaqta arru/yainna kathalika najzee almuhsineen
Hausa
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
|
Ayah 37:106 الأية
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْبَلَاءُ الْمُبِينُ
Inna hatha lahuwa albalaoalmubeen
Hausa
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
|
Ayah 37:107 الأية
وَفَدَيْنَاهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍ
Wafadaynahu bithibhinAAatheem
Hausa
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
|
Ayah 37:108 الأية
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Watarakna AAalayhi fee al-akhireen
Hausa
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
|
Ayah 37:109 الأية
سَلَامٌ عَلَىٰ إِبْرَاهِيمَ
Salamun AAala ibraheem
Hausa
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
|
Ayah 37:110 الأية
كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Kathalika najzee almuhsineen
Hausa
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
|
Ayah 37:111 الأية
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Innahu min AAibadinaalmu/mineen
Hausa
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
|
Ayah 37:112 الأية
وَبَشَّرْنَاهُ بِإِسْحَاقَ نَبِيًّا مِّنَ الصَّالِحِينَ
Wabashsharnahu bi-ishaqanabiyyan mina assaliheen
Hausa
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
|
Ayah 37:113 الأية
وَبَارَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰ إِسْحَاقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ
وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِ مُبِينٌ
Wabarakna AAalayhi waAAalaishaqa wamin thurriyyatihima muhsinunwathalimun
linafsihi mubeen
Hausa
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu
akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga
zãluncin).
|
Ayah 37:114 الأية
وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ
Walaqad mananna AAala moosawaharoon
Hausa
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
|
Ayah 37:115 الأية
وَنَجَّيْنَاهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ
Wanajjaynahuma waqawmahumamina alkarbi alAAatheem
Hausa
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
|
Ayah 37:116 الأية
وَنَصَرْنَاهُمْ فَكَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ
Wanasarnahum fakanoohumu alghalibeen
Hausa
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
|
Ayah 37:117 الأية
وَآتَيْنَاهُمَا الْكِتَابَ الْمُسْتَبِينَ
Waataynahuma alkitabaalmustabeen
Hausa
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
|
|