Prev  

51. Surah Az-Zâriyât سورة الذاريات

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَالذَّارِيَاتِ ذَرْوًا
Waththariyati tharwa

Hausa
 
Ină rantsuwa da iskőki măsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.

Ayah  51:2  الأية
فَالْحَامِلَاتِ وِقْرًا
Falhamilati wiqra

Hausa
 
Sa'an nan da girăgizai măsu ɗaukar nauyi (na ruwa).

Ayah  51:3  الأية
فَالْجَارِيَاتِ يُسْرًا
Faljariyati yusra

Hausa
 
Sa'an nan da jirăge măsu gudăna (a kan ruwa) da sauƙi.

Ayah  51:4  الأية
فَالْمُقَسِّمَاتِ أَمْرًا
Falmuqassimati amra

Hausa
 
Sa'an nan da Mală'iku măsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).

Ayah  51:5  الأية
إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٌ
Innama tooAAadoona lasadiq

Hausa
 
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.

Ayah  51:6  الأية
وَإِنَّ الدِّينَ لَوَاقِعٌ
Wa-inna addeena lawaqiAA

Hausa
 
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne

Ayah  51:7  الأية
وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الْحُبُكِ
Wassama-i thati alhubuk

Hausa
 
Ină rantsuwa da samă ma'abũciyar hanyőyi ( na tafiyar taurări da sautin rediyo).

Ayah  51:8  الأية
إِنَّكُمْ لَفِي قَوْلٍ مُّخْتَلِفٍ
Innakum lafee qawlin mukhtalif

Hausa
 
Lalle kũ, haƙĩƙa, kună cikin magana mai săɓa wa juna (game da Alƙur'ani).

Ayah  51:9  الأية
يُؤْفَكُ عَنْهُ مَنْ أُفِكَ
Yu/faku AAanhu man ofik

Hausa
 
Ană karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).

Ayah  51:10  الأية
قُتِلَ الْخَرَّاصُونَ
Qutila alkharrasoon

Hausa
 
An la'ani măsu ƙiri-faɗi.

Ayah  51:11  الأية
الَّذِينَ هُمْ فِي غَمْرَةٍ سَاهُونَ
Allatheena hum fee ghamratin sahoon

Hausa
 
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jăhilci.

Ayah  51:12  الأية
يَسْأَلُونَ أَيَّانَ يَوْمُ الدِّينِ
Yas-aloona ayyana yawmu addeen

Hausa
 
Sună tambaya: "Yaushe ne rănar sakamako ză ta auku?"

Ayah  51:13  الأية
يَوْمَ هُمْ عَلَى النَّارِ يُفْتَنُونَ
Yawma hum AAala annariyuftanoon

Hausa
 
Ranar da suke a kan wuta ană fitinar su.

Ayah  51:14  الأية
ذُوقُوا فِتْنَتَكُمْ هَٰذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تَسْتَعْجِلُونَ
Thooqoo fitnatakum hatha allatheekuntum bihi tastaAAjiloon

Hausa
 
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kună nẽman zuwansa da gaggăwa."

Ayah  51:15  الأية
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ
Inna almuttaqeena fee jannatinwaAAuyoon

Hausa
 
Lalle măsu taƙawa, sună a cikin lambunan ităce da marẽmari.

Ayah  51:16  الأية
آخِذِينَ مَا آتَاهُمْ رَبُّهُمْ ۚ إِنَّهُمْ كَانُوا قَبْلَ ذَٰلِكَ مُحْسِنِينَ
Akhitheena ma atahumrabbuhum innahum kanoo qabla thalika muhsineen

Hausa
 
Sună măsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bă su. Lalle sũ, sun kasance măsu kyautatăwa a gabănin haka (a dũniya).

Ayah  51:17  الأية
كَانُوا قَلِيلًا مِّنَ اللَّيْلِ مَا يَهْجَعُونَ
Kanoo qaleelan mina allayli mayahjaAAoon

Hausa
 
Sun kasance a lőkaci kaɗan na dare suke yin barci.

Ayah  51:18  الأية
وَبِالْأَسْحَارِ هُمْ يَسْتَغْفِرُونَ
Wabil-ashari humyastaghfiroon

Hausa
 
Kuma a lőkutan asuba sună ta yin istigfări.

Ayah  51:19  الأية
وَفِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ لِّلسَّائِلِ وَالْمَحْرُومِ
Wafee amwalihim haqqun lissa-iliwalmahroom

Hausa
 
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rőƙo da wanda aka hana wa rőƙo.

Ayah  51:20  الأية
وَفِي الْأَرْضِ آيَاتٌ لِّلْمُوقِنِينَ
Wafee al-ardi ayatunlilmooqineen

Hausa
 
Kuma a cikin ƙasă akwai ăyőyi ga măsu yaƙĩni.

Ayah  51:21  الأية
وَفِي أَنفُسِكُمْ ۚ أَفَلَا تُبْصِرُونَ
Wafee anfusikum afala tubsiroon

Hausa
 
Kuma a cikin răyukanku (akwai ăyőyi). To, bă ză ku dũbă ba?

Ayah  51:22  الأية
وَفِي السَّمَاءِ رِزْقُكُمْ وَمَا تُوعَدُونَ
Wafee assama-i rizqukum wamatooAAadoon

Hausa
 
Kuma a cikin sama arzikinku ( yake fitőwa) da abin da ake yi muku alkawari.

Ayah  51:23  الأية
فَوَرَبِّ السَّمَاءِ وَالْأَرْضِ إِنَّهُ لَحَقٌّ مِّثْلَ مَا أَنَّكُمْ تَنطِقُونَ
Fawarabbi assama-i wal-ardiinnahu lahaqqun mithla ma annakum tantiqoon

Hausa
 
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasă, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kună karantăwa na magana,

Ayah  51:24  الأية
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ ضَيْفِ إِبْرَاهِيمَ الْمُكْرَمِينَ
Hal ataka hadeethu dayfiibraheema almukrameen

Hausa
 
Shin, lăbărin Băƙin Ibrăhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?

Ayah  51:25  الأية
إِذْ دَخَلُوا عَلَيْهِ فَقَالُوا سَلَامًا ۖ قَالَ سَلَامٌ قَوْمٌ مُّنكَرُونَ
Ith dakhaloo AAalayhi faqaloosalaman qala salamun qawmun munkaroon

Hausa
 
A lőkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutăne băƙi!"

Ayah  51:26  الأية
فَرَاغَ إِلَىٰ أَهْلِهِ فَجَاءَ بِعِجْلٍ سَمِينٍ
Faragha ila ahlihi fajaabiAAijlin sameen

Hausa
 
Sai ya jũya zuwa ga iyălinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,

Ayah  51:27  الأية
فَقَرَّبَهُ إِلَيْهِمْ قَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ
Faqarrabahu ilayhim qala alata/kuloon

Hausa
 
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bă ză ku ci ba?"

Ayah  51:28  الأية
فَأَوْجَسَ مِنْهُمْ خِيفَةً ۖ قَالُوا لَا تَخَفْ ۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَامٍ عَلِيمٍ
Faawjasa minhum kheefatan qaloo latakhaf wabashsharoohu bighulamin AAaleem

Hausa
 
Sai ya ji tsőro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsőro." Kuma suka yi masa bushăra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.

Ayah  51:29  الأية
فَأَقْبَلَتِ امْرَأَتُهُ فِي صَرَّةٍ فَصَكَّتْ وَجْهَهَا وَقَالَتْ عَجُوزٌ عَقِيمٌ
Faaqbalati imraatuhu fee sarratin fasakkatwajhaha waqalat AAajoozun AAaqeem

Hausa
 
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallőwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsőhuwa bakarăriya (ză ta haihu)!"

Ayah  51:30  الأية
قَالُوا كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِ ۖ إِنَّهُ هُوَ الْحَكِيمُ الْعَلِيمُ
Qaloo kathaliki qalarabbuki innahu huwa alhakeemu alAAaleem

Hausa
 
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."

Ayah  51:31  الأية
قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا الْمُرْسَلُونَ
Qala fama khatbukumayyuha almursaloon

Hausa
 
(Ibrăĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yă kũ Manzanni!"

Ayah  51:32  الأية
قَالُوا إِنَّا أُرْسِلْنَا إِلَىٰ قَوْمٍ مُّجْرِمِينَ
Qaloo inna orsilna ilaqawmin mujrimeen

Hausa
 
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutăne, măsu laifi.

Ayah  51:33  الأية
لِنُرْسِلَ عَلَيْهِمْ حِجَارَةً مِّن طِينٍ
Linursila AAalayhim hijaratanmin teen

Hausa
 
"Dőmin mu saka musu waɗansu duwătsu na wani yumɓu ( bom).

Ayah  51:34  الأية
مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلْمُسْرِفِينَ
Musawwamatan AAinda rabbika lilmusrifeen

Hausa
 
"Waɗanda aka yi wa alăma daga wajen Ubangijinka, dőmin măsu ɓarna."

Ayah  51:35  الأية
فَأَخْرَجْنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Faakhrajna man kana feehamina almu/mineen

Hausa
 
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.

Ayah  51:36  الأية
فَمَا وَجَدْنَا فِيهَا غَيْرَ بَيْتٍ مِّنَ الْمُسْلِمِينَ
Fama wajadna feehaghayra baytin mina almuslimeen

Hausa
 
Sai dai ba mu sămu ba, a cikinta, făce gida guda na Musulmi.

Ayah  51:37  الأية
وَتَرَكْنَا فِيهَا آيَةً لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ الْعَذَابَ الْأَلِيمَ
Watarakna feeha ayatanlillatheena yakhafoona alAAathaba al-aleem

Hausa
 
Kuma Muka bar wata ăyă, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsőron azăba, mai raɗaɗi.

Ayah  51:38  الأية
وَفِي مُوسَىٰ إِذْ أَرْسَلْنَاهُ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍ
Wafee moosa ith arsanahuila firAAawna bisultanin mubeen

Hausa
 
Kuma ga Mũsă, a lőkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.

Ayah  51:39  الأية
فَتَوَلَّىٰ بِرُكْنِهِ وَقَالَ سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ
Fatawalla biruknihi waqala sahirunaw majnoon

Hausa
 
Sai ya jũya băya tăre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kő kuwa mahaukaci !"

Ayah  51:40  الأية
فَأَخَذْنَاهُ وَجُنُودَهُ فَنَبَذْنَاهُمْ فِي الْيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٌ
Faakhathnahu wajunoodahufanabathnahum fee alyammi wahuwa muleem

Hausa
 
Sabőda haka, Muka kama shi tăre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhăli kuwa yană wanda ake zargi.

Ayah  51:41  الأية
وَفِي عَادٍ إِذْ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمُ الرِّيحَ الْعَقِيمَ
Wafee AAadin ith arsalnaAAalayhimu arreeha alAAaqeem

Hausa
 
Kuma ga Ădăwa, a lőkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.

Ayah  51:42  الأية
مَا تَذَرُ مِن شَيْءٍ أَتَتْ عَلَيْهِ إِلَّا جَعَلَتْهُ كَالرَّمِيمِ
Ma tatharu min shay-in atatAAalayhi illa jaAAalat-hu karrameem

Hausa
 
Bă ta barin kőme da ta jẽ a kansa, făce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.

Ayah  51:43  الأية
وَفِي ثَمُودَ إِذْ قِيلَ لَهُمْ تَمَتَّعُوا حَتَّىٰ حِينٍ
Wafee thamooda ith qeela lahumtamattaAAoo hatta heen

Hausa
 
Kuma ga Samũdăwa, a lőkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dăɗi har wani ɗan lőkaci,"

Ayah  51:44  الأية
فَعَتَوْا عَنْ أَمْرِ رَبِّهِمْ فَأَخَذَتْهُمُ الصَّاعِقَةُ وَهُمْ يَنظُرُونَ
FaAAataw AAan amri rabbihim faakhathat-humuassaAAiqatu wahum yanthuroon

Hausa
 
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabőda haka tsăwa ta kăma su, alhăli kuwa sună kallo.

Ayah  51:45  الأية
فَمَا اسْتَطَاعُوا مِن قِيَامٍ وَمَا كَانُوا مُنتَصِرِينَ
Fama istataAAoo min qiyaminwama kanoo muntasireen

Hausa
 
Ba su kő sămu dămar tsayăwa ba, kuma ba su kasance măsu nẽman ăgaji ba.

Ayah  51:46  الأية
وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا قَوْمًا فَاسِقِينَ
Waqawma noohin min qablu innahum kanooqawman fasiqeen

Hausa
 
Da mutănen Nũhu a gabănin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutăne ne făsiƙai.

Ayah  51:47  الأية
وَالسَّمَاءَ بَنَيْنَاهَا بِأَيْدٍ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ
Wassamaa banaynahabi-aydin wa-inna lamoosiAAoon

Hausa
 
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhăli kuwa lalle Mũ ne Măsu yalwatăwa.

Ayah  51:48  الأية
وَالْأَرْضَ فَرَشْنَاهَا فَنِعْمَ الْمَاهِدُونَ
Wal-arda farashnahafaniAAma almahidoon

Hausa
 
Kuma ƙasă Mun shimfiɗa ta, To, madalla da măsu shimfiɗăwa, Mũ,

Ayah  51:49  الأية
وَمِن كُلِّ شَيْءٍ خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَ
Wamin kulli shay-in khalaqna zawjaynilaAAallakum tathakkaroon

Hausa
 
Kuma daga kőme Mun halitta nau'i biyu, watakila ză ku yi tunăni.

Ayah  51:50  الأية
فَفِرُّوا إِلَى اللهِ ۖ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌ
Fafirroo ila Allahi inneelakum minhu natheerun mubeen

Hausa
 
Sabőda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

Ayah  51:51  الأية
وَلَا تَجْعَلُوا مَعَ اللهِ إِلَٰهًا آخَرَ ۖ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌ
Wala tajAAaloo maAAa Allahi ilahanakhara innee lakum minhu natheerun mubeen

Hausa
 
Kuma kada ku sanya, tăre da Allah wani abin bautăwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

Ayah  51:52  الأية
كَذَٰلِكَ مَا أَتَى الَّذِينَ مِن قَبْلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُوا سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ
Kathalika ma ata allatheenamin qablihim min rasoolin illa qaloo sahirunaw majnoon

Hausa
 
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabăninsu ba făce sun ce: "Mai sihiri ne kő mahaukaci."

Ayah  51:53  الأية
أَتَوَاصَوْا بِهِ ۚ بَلْ هُمْ قَوْمٌ طَاغُونَ
Atawasaw bihi bal hum qawmun taghoon

Hausa
 
shin, sună yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ă'a, sũ dai mutăne ne măsu girman kai.

Ayah  51:54  الأية
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ فَمَا أَنتَ بِمَلُومٍ
Fatawalla AAanhum fama anta bimaloom

Hausa
 
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.

Ayah  51:55  الأية
وَذَكِّرْ فَإِنَّ الذِّكْرَىٰ تَنفَعُ الْمُؤْمِنِينَ
Wathakkir fa-inna aththikratanfaAAu almu/mineen

Hausa
 
Kuma ka tunătar, dőmin tunătarwa tană amfănin mũminai.

Ayah  51:56  الأية
وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ
Wama khalaqtu aljinna wal-insailla liyaAAbudoon

Hausa
 
Kuma Ban halitta aljannu da mutăne ba sai dőmin su bauta Mini.

Ayah  51:57  الأية
مَا أُرِيدُ مِنْهُم مِّن رِّزْقٍ وَمَا أُرِيدُ أَن يُطْعِمُونِ
Ma oreedu minhum min rizqin wamaoreedu an yutAAimoon

Hausa
 
Bă Ni nufln (sămun) wani arziki daga gare su, Bă Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.

Ayah  51:58  الأية
إِنَّ اللهَ هُوَ الرَّزَّاقُ ذُو الْقُوَّةِ الْمَتِينُ
Inna Allaha huwa arrazzaquthoo alquwwati almateen

Hausa
 
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtăwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.

Ayah  51:59  الأية
فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا ذَنُوبًا مِّثْلَ ذَنُوبِ أَصْحَابِهِمْ فَلَا يَسْتَعْجِلُونِ
Fa-inna lillatheena thalamoothanooban mithla thanoobi as-habihimfala yastaAAjiloon

Hausa
 
To, lalle waɗanda suka yi zălunci sună da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abőkansu, sabőda haka kada su yi Mini gaggăwa.

Ayah  51:60  الأية
فَوَيْلٌ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا مِن يَوْمِهِمُ الَّذِي يُوعَدُونَ
Fawaylun lillatheena kafaroo minyawmihimu allathee yooAAadoon

Hausa
 
Sabőda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kăfirta, daga rănar su wadda aka yi musu alkawari.




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us