Prev  

89. Surah Al-Fajr سورة الفجر

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَالْفَجْرِ
Walfajr

Hausa
 
Inã rantsuwa da alfijiri.

Ayah  89:2  الأية
وَلَيَالٍ عَشْرٍ
Walayalin AAashr

Hausa
 
Da darũruwa gõma.

Ayah  89:3  الأية
وَالشَّفْعِ وَالْوَتْرِ
WashshafAAi walwatr

Hausa
 
Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

Ayah  89:4  الأية
وَاللَّيْلِ إِذَا يَسْرِ
Wallayli itha yasr

Hausa
 
Da dare idan yana shũɗewa.

Ayah  89:5  الأية
هَلْ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٌ لِّذِي حِجْرٍ
Hal fee thalika qasamun lithee hijr

Hausa
 
Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

Ayah  89:6  الأية
أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ
Alam tara kayfa faAAala rabbuka biAAad

Hausa
 
Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

Ayah  89:7  الأية
إِرَمَ ذَاتِ الْعِمَادِ
Irama thati alAAimad

Hausa
 
Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.

Ayah  89:8  الأية
الَّتِي لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِي الْبِلَادِ
Allatee lam yukhlaq mithluha fee albilad

Hausa
 
Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

Ayah  89:9  الأية
وَثَمُودَ الَّذِينَ جَابُوا الصَّخْرَ بِالْوَادِ
Wathamooda allatheena jaboo assakhrabilwad

Hausa
 
Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?

Ayah  89:10  الأية
وَفِرْعَوْنَ ذِي الْأَوْتَادِ
WafirAAawna thee al-awtad

Hausa
 
Da Fir'auna mai turãku.

Ayah  89:11  الأية
الَّذِينَ طَغَوْا فِي الْبِلَادِ
Allatheena taghaw fee albilad

Hausa
 
Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

Ayah  89:12  الأية
فَأَكْثَرُوا فِيهَا الْفَسَادَ
Faaktharoo feeha alfasad

Hausa
 
Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

Ayah  89:13  الأية
فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ
Fasabba AAalayhim rabbuka sawtaAAathab

Hausa
 
Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

Ayah  89:14  الأية
إِنَّ رَبَّكَ لَبِالْمِرْصَادِ
Inna rabbaka labilmirsad

Hausa
 
Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

Ayah  89:15  الأية
فَأَمَّا الْإِنسَانُ إِذَا مَا ابْتَلَاهُ رَبُّهُ فَأَكْرَمَهُ وَنَعَّمَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَكْرَمَنِ
Faamma al-insanu itha maibtalahu rabbuhu faakramahu wanaAAAAamahu fayaqoolu rabbeeakraman

Hausa
 
To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

Ayah  89:16  الأية
وَأَمَّا إِذَا مَا ابْتَلَاهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَهَانَنِ
Waamma itha ma ibtalahufaqadara AAalayhi rizqahu fayaqoolu rabbee ahanan

Hausa
 
Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

Ayah  89:17  الأية
كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ الْيَتِيمَ
Kalla bal la tukrimoonaalyateem

Hausa
 
A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

Ayah  89:18  الأية
وَلَا تَحَاضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ
Wala tahaddoona AAala taAAamialmiskeen

Hausa
 
Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

Ayah  89:19  الأية
وَتَأْكُلُونَ التُّرَاثَ أَكْلًا لَّمًّا
Wata/kuloona atturatha aklanlamma

Hausa
 
Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

Ayah  89:20  الأية
وَتُحِبُّونَ الْمَالَ حُبًّا جَمًّا
Watuhibboona almala hubbanjamma

Hausa
 
Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

Ayah  89:21  الأية
كَلَّا إِذَا دُكَّتِ الْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا
Kalla itha dukkati al-ardudakkan dakka

Hausa
 
A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

Ayah  89:22  الأية
وَجَاءَ رَبُّكَ وَالْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا
Wajaa rabbuka walmalaku saffansaffa

Hausa
 
Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.

Ayah  89:23  الأية
وَجِيءَ يَوْمَئِذٍ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ وَأَنَّىٰ لَهُ الذِّكْرَىٰ
Wajee-a yawma-ithin bijahannamayawma-ithin yatathakkaru al-insanu waannalahu aththikra

Hausa
 
Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

Ayah  89:24  الأية
يَقُولُ يَا لَيْتَنِي قَدَّمْتُ لِحَيَاتِي
Yaqoolu ya laytanee qaddamtu lihayatee

Hausa
 
Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"

Ayah  89:25  الأية
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُ أَحَدٌ
Fayawma-ithin la yuAAaththibuAAathabahu ahad

Hausa
 
To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.

Ayah  89:26  الأية
وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُ أَحَدٌ
Wala yoothiqu wathaqahu ahad

Hausa
 
Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.

Ayah  89:27  الأية
يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ
Ya ayyatuha annafsualmutma-inna

Hausa
 
Yã kai rai mai natsuwa!

Ayah  89:28  الأية
ارْجِعِي إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةً
IrjiAAee ila rabbiki radiyatanmardiyya

Hausa
 
Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).

Ayah  89:29  الأية
فَادْخُلِي فِي عِبَادِي
Fadkhulee fee AAibadee

Hausa
 
Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).

Ayah  89:30  الأية
وَادْخُلِي جَنَّتِي
Wadkhulee jannatee

Hausa
 
Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira). 




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us