1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
قُلْ أُوحِيَ إِلَيَّ أَنَّهُ اسْتَمَعَ نَفَرٌ مِّنَ الْجِنِّ فَقَالُوا إِنَّا
سَمِعْنَا قُرْآنًا عَجَبًا
Qul oohiya ilayya annahu istamaAAanafarun mina aljinni faqaloo inna
samiAAnaqur-anan AAajaba
Hausa
Ka ce: "An yi wahayi zuwa gare ni cewa wasu jama'a na aljannu sun saurũri
(karatuna), sai suka ce: Lalle ne mũ mun ji wani abin karantãwa (Alƙui'ãni), mai
ban mãmãki."
|
Ayah 72:2 الأية
يَهْدِي إِلَى الرُّشْدِ فَآمَنَّا بِهِ ۖ وَلَن نُّشْرِكَ بِرَبِّنَا أَحَدًا
Yahdee ila arrushdi faamannabihi walan nushrika birabbina ahada
Hausa
"Yana nũni zuwa ga hanyar ƙwarai, sabõda haka mun yi ĩmãni da shi bã zã mu kõma
bautã wa Ubangijinmu tãre da kõwa ba."
|
Ayah 72:3 الأية
وَأَنَّهُ تَعَالَىٰ جَدُّ رَبِّنَا مَا اتَّخَذَ صَاحِبَةً وَلَا وَلَدًا
Waannahu taAAala jaddu rabbinama ittakhatha sahibatan wala walada
Hausa
"Kuma lalle ne shĩ girman Ubangijinmu, Ya ɗaukaka, bai riƙi mãta ba, kuma bai
riƙi ɗã ba."
|
Ayah 72:4 الأية
وَأَنَّهُ كَانَ يَقُولُ سَفِيهُنَا عَلَى اللهِ شَطَطًا
Waannahu kana yaqoolu safeehunaAAala Allahi shatata
Hausa
"Kuma lalle ne shi, wãwanmu ya kasance yana faɗar abin da ya ƙetare haddi ga
Allah."
|
Ayah 72:5 الأية
وَأَنَّا ظَنَنَّا أَن لَّن تَقُولَ الْإِنسُ وَالْجِنُّ عَلَى اللهِ كَذِبًا
Waanna thanannaan lan taqoola al-insu waljinnu AAala Allahikathiba
Hausa
"Kuma lalle ne mũ, mun yi zaton mutum da aljani bã zã su iya faɗar ƙarya ba ga
Allah."
|
Ayah 72:6 الأية
وَأَنَّهُ كَانَ رِجَالٌ مِّنَ الْإِنسِ يَعُوذُونَ بِرِجَالٍ مِّنَ الْجِنِّ
فَزَادُوهُمْ رَهَقًا
Waannahu kana rijalun minaal-insi yaAAoothoona birijalin mina aljinni
fazadoohumrahaqa
Hausa
"Kuma lalle ne shi wasu maza daga cikin mutãne, sun kasance sunã nẽman tsari da
wasu maza daga cikin aljannu, sabõda haka suka ƙara musu girman kai."
|
Ayah 72:7 الأية
وَأَنَّهُمْ ظَنُّوا كَمَا ظَنَنتُمْ أَن لَّن يَبْعَثَ اللهُ أَحَدًا
Waannahum thannoo kama thanantuman lan yabAAatha Allahu ahada
Hausa
"Kuma lalle ne sũ, sun yi zato, kamar yadda kuka yi zato, cewa Allah bã zai aiko
kowa ba."
|
Ayah 72:8 الأية
وَأَنَّا لَمَسْنَا السَّمَاءَ فَوَجَدْنَاهَا مُلِئَتْ حَرَسًا شَدِيدًا وَشُهُبًا
Waanna lamasna assamaafawajadnaha muli-at harasan shadeedanwashuhuba
Hausa
"Kuma lalle ne mũ mun nẽmi (hawan) sama, sai muka, sãme ta an cika ta da tsaro
mai tsanani da kuma yũlãye."
|
Ayah 72:9 الأية
وَأَنَّا كُنَّا نَقْعُدُ مِنْهَا مَقَاعِدَ لِلسَّمْعِ ۖ فَمَن يَسْتَمِعِ الْآنَ
يَجِدْ لَهُ شِهَابًا رَّصَدًا
Waanna kunna naqAAudu minhamaqaAAida lissamAAi faman yastamiAAi al-anayajid lahu
shihaban rasada
Hausa
"Kuma lalle ne mũ, mun kasance muna zama daga garẽta, a wurãren zama dõmin
saurare. To wanda ya yi saurãre a yanzu, zai sãmi yũla, mai dãko dõminsa."
|
Ayah 72:10 الأية
وَأَنَّا لَا نَدْرِي أَشَرٌّ أُرِيدَ بِمَن فِي الْأَرْضِ أَمْ أَرَادَ بِهِمْ
رَبُّهُمْ رَشَدًا
Waanna la nadree asharrunoreeda biman fee al-ardi am arada bihim rabbuhumrashada
Hausa
"Kuma lalle ne mũ ba mu sani ba, shin, sharri ne aka yi nufi ga waɗanda ke cikin
ƙasa, ko Ubangijinsu Yã yi nufin shiriya a gare su ne?"
|
Ayah 72:11 الأية
وَأَنَّا مِنَّا الصَّالِحُونَ وَمِنَّا دُونَ ذَٰلِكَ ۖ كُنَّا طَرَائِقَ قِدَدًا
Waanna minna assalihoonawaminna doona thalika kunna tara-iqaqidada
Hausa
"Kuma lalle ne mũ, akwai sãlaihai a cikinmu, kuma akwai a cikinmu waɗanda ba
haka bã mun kasance ƙungiyõyi dabam-dabam."
|
Ayah 72:12 الأية
وَأَنَّا ظَنَنَّا أَن لَّن نُّعْجِزَ اللهَ فِي الْأَرْضِ وَلَن نُّعْجِزَهُ
هَرَبًا
Wanna thanannaan lan nuAAjiza Allaha fee al-ardi walan nuAAjizahuharaba
Hausa
"Kuma lalle ne mũ mun tabbatã bã zã mu buwãyi Allah ba, a cikin ƙasa, kuma bã zã
mu buwãye Shi da gudu ba."
|
Ayah 72:13 الأية
وَأَنَّا لَمَّا سَمِعْنَا الْهُدَىٰ آمَنَّا بِهِ ۖ فَمَن يُؤْمِن بِرَبِّهِ فَلَا
يَخَافُ بَخْسًا وَلَا رَهَقًا
Waanna lamma samiAAnaalhuda amanna bihi faman yu/min birabbihifala yakhafu
bakhsan wala rahaqa
Hausa
"Kuma lalle ne mũ, a lõkacin da muka ji shiriya, mun yi ĩmãni da ita. To wanda
ya yi ĩimãni da Uhangijinsa, bã zai ji tsõron nakkasa ba, kuma bã zai ji tsõron
zãlunci ba."
|
Ayah 72:14 الأية
وَأَنَّا مِنَّا الْمُسْلِمُونَ وَمِنَّا الْقَاسِطُونَ ۖ فَمَنْ أَسْلَمَ
فَأُولَٰئِكَ تَحَرَّوْا رَشَدًا
Waanna minna almuslimoonawaminna alqasitoona faman aslama faola-ikataharraw
rashada
Hausa
"Kuma lalle ne mũ akwai a cikinmu, waɗanda suka mĩƙa wuya, kuma akwai a cikinmu
karkatattu. to, wanda ya mĩƙa wuya waɗancan kam sun nufi shiryuwa."
|
Ayah 72:15 الأية
وَأَمَّا الْقَاسِطُونَ فَكَانُوا لِجَهَنَّمَ حَطَبًا
Waama alqasitoona fakanoolijahannama hataba
Hausa
"Kuma amma karkatattu sai suka kasance makãmashi ga Jahannama."
|
Ayah 72:16 الأية
وَأَن لَّوِ اسْتَقَامُوا عَلَى الطَّرِيقَةِ لَأَسْقَيْنَاهُم مَّاءً غَدَقًا
Waallawi istaqamoo AAala attareeqatilaasqaynahum maan ghadaqa
Hausa
"Kuma dã sun tsayu sõsai a kan hanya, dã lalle Mun shãyar da su ruwa mai yawa."
|
Ayah 72:17 الأية
لِّنَفْتِنَهُمْ فِيهِ ۚ وَمَن يُعْرِضْ عَن ذِكْرِ رَبِّهِ يَسْلُكْهُ عَذَابًا
صَعَدًا
Linaftinahum feehi waman yuAArid AAanthikri rabbihi yasluk-hu AAathaban saAAada
Hausa
"Domin Mu jarraba su a ciki, kuma wanda ya kau da kai daga tuna Ubangijinsa,
Ubangijinsa zai shigar da shi azãba mai hauhawa."
|
Ayah 72:18 الأية
وَأَنَّ الْمَسَاجِدَ لِلَّهِ فَلَا تَدْعُوا مَعَ اللهِ أَحَدًا
Waanna almasajida lillahi falatadAAoo maAAa Allahi ahada
Hausa
"Kuma lalle ne wurãren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kõwa tãre da
Allah (da su, a cikinsu)."
|
Ayah 72:19 الأية
وَأَنَّهُ لَمَّا قَامَ عَبْدُ اللهِ يَدْعُوهُ كَادُوا يَكُونُونَ عَلَيْهِ
لِبَدًا
Waannahu lamma qama AAabdu AllahiyadAAoohu kadoo yakoonoona AAalayhi libada
Hausa
"Kuma, lalle ne shi, a lõkacin da bãwan Allah ke kiran Sa sun yi kusa su zama
kamar shirgi a kansa."
|
Ayah 72:20 الأية
قُلْ إِنَّمَا أَدْعُو رَبِّي وَلَا أُشْرِكُ بِهِ أَحَدًا
Qul innama adAAoo rabbee walaoshriku bihi ahada
Hausa
Ka ce: "lna kiran Ubangijina ne kawai, kuma bã zan tãra kowa da Shi ba."
|
Ayah 72:21 الأية
قُلْ إِنِّي لَا أَمْلِكُ لَكُمْ ضَرًّا وَلَا رَشَدًا
Qul innee la amliku lakum darranwala rashada
Hausa
Ka ce: "Lalle ne, nĩ bã ni mallakar wata cũta gare ku, kuma bã ni mallakar wani
alhẽri."
|
Ayah 72:22 الأية
قُلْ إِنِّي لَن يُجِيرَنِي مِنَ اللهِ أَحَدٌ وَلَنْ أَجِدَ مِن دُونِهِ
مُلْتَحَدًا
Qul innee lan yujeeranee mina Allahiahadun walan ajida min doonihi multahada
Hausa
Ka ce: "Lalle ne, nĩ kõwa bã ya iya cẽtona daga Allah, kuma bã zan iya sãmun
mafaka ba daga gare Shi."
|
Ayah 72:23 الأية
إِلَّا بَلَاغًا مِّنَ اللهِ وَرِسَالَاتِهِ ۚ وَمَن يَعْصِ اللهَ وَرَسُولَهُ
فَإِنَّ لَهُ نَارَ جَهَنَّمَ خَالِدِينَ فِيهَا أَبَدًا
Illa balaghan mina Allahiwarisalatihi waman yaAAsi Allahawarasoolahu fa-inna
lahu nara jahannama khalideenafeeha abada
Hausa
"Fãce iyarwa, daga Allah, da manzancinsa. To, wanda ya sãɓa wa Allah da
ManzonSa, to, lalle yana da wutar Jahannama suna mãsu dawwama a cikinta, har
abada."
|
Ayah 72:24 الأية
حَتَّىٰ إِذَا رَأَوْا مَا يُوعَدُونَ فَسَيَعْلَمُونَ مَنْ أَضْعَفُ نَاصِرًا
وَأَقَلُّ عَدَدًا
Hatta itha raaw mayooAAadoona fasayaAAlamoona man adAAafu nasiranwaaqallu
AAadada
Hausa
Har idan sun ga abin da ake yi musu gargaɗi da shi, to, zã su san wanda ya zama
mafi raunin mataimaki da mafi ƙarancin adadi.
|
Ayah 72:25 الأية
قُلْ إِنْ أَدْرِي أَقَرِيبٌ مَّا تُوعَدُونَ أَمْ يَجْعَلُ لَهُ رَبِّي أَمَدًا
Qul in adree aqareebun ma tooAAadoonaam yajAAalu lahu rabbee amada
Hausa
Ka ce: "Ban sani ba a kusa ne abin da ake yi muku gargaɗi da shi, ko Ubangijina
Ya sanya maSa dõgon ajali!"
|
Ayah 72:26 الأية
عَالِمُ الْغَيْبِ فَلَا يُظْهِرُ عَلَىٰ غَيْبِهِ أَحَدًا
AAalimu alghaybi fala yuthhiruAAala ghaybihi ahada
Hausa
"Shi ɗai ne Masanin fake sabõda haka, bã Ya bayyana gaibinSa ga kowa."
|
Ayah 72:27 الأية
إِلَّا مَنِ ارْتَضَىٰ مِن رَّسُولٍ فَإِنَّهُ يَسْلُكُ مِن بَيْنِ يَدَيْهِ وَمِنْ
خَلْفِهِ رَصَدًا
Illa mani irtada min rasoolinfa-innahu yasluku min bayni yadayhi wamin khalfihi
rasada
Hausa
"Fãce ga wanda Yã yarda da shi, wato wani manzo sa'an nan lalle ne, zai sanya
gãdi a gaba gare shi da bãya gare shi."
|
Ayah 72:28 الأية
لِّيَعْلَمَ أَن قَدْ أَبْلَغُوا رِسَالَاتِ رَبِّهِمْ وَأَحَاطَ بِمَا لَدَيْهِمْ
وَأَحْصَىٰ كُلَّ شَيْءٍ عَدَدًا
LiyaAAlama an qad ablaghoo risalatirabbihim waahata bima ladayhim waahsa
kullashay-in AAadada
Hausa
"Dõmin Ya san lalle, sun iyar da sãƙonnin Ubangijinsu, kuma (Shi Ubangijin) Yã
kẽwaye su da sani, kuma Yã lissafe dukan kõme da ƙididdiga."
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|