Kuma da yẽkuwa daga Allah da ManzonSa zuwa ga mutãne, a Rãnar Haji Babba cẽwa
lallene Allah Barrantacce ne daga mãsu shirki, kuma ManzonSa (haka). To, idan
kun tũba to shi ne mafi alhẽri a gare ku, kuma idan kun jũya, to, ku sani lalle
ne kũ, bã mãsu buwãyar Allah ba ne. Kuma ka bãyar da bishãra ga waɗanda suka
kãfirta, da azãba mai raɗaɗi.
Sai waɗanda kuka yi wani alkawari daga mãsu shirki, sa'an nan kuma ba su rage ku
da kõme ba, kuma ba su taimaki kõwa a kanku ba, to, ku cika alkawarin, zuwa gare
su, har ga iyakar yarjẽjẽyarsu. Lalle ne Allah Yanã son mãsu taƙawa.
Kuma idan watanni, mãsu alfarma suka shige, to, ku yãki mushirikai inda kuka
sãmẽ su, kuma ku kãmã su, kuma ku tsare su, kuma ku zaune musu dukkan madãkata.
To, idan sun tũba, kuma suka tsayar da salla, kuma suka bãyar da zakka to ku
sakar musu da hanyarsu. Lalle Allah ne Mai gãfara,Mai jin ƙai.
Idan wani daga mushirikai ya nemi maƙwabtakarka to, ka ba shi maƙwabtakar har ya
ji, maganar Allah, sa'an nan ka isar da shi ga wurin amincewarsa. Wancan fa
domin lalle ne su, mutãne ne waɗanda ba su sani ba.
Yãya wani alkawari a wurin Allah a wurin ManzonSa yake kasancẽwa ga mushirikai,
fãce ga waɗanda kuka yi wa alkawari wurin Masallaci Mai alfarma? To matuƙar sun
tsaya sõsai gare ku, sai ku tsayu sõsai gare su. Lalle ne Allah Yanã son mãsu
taƙawa.
Yãya, alhãli idan sun ci nasara a kanku, bã zã su tsare wata zumun ta ba a
cikinku, kuma haka wata amãna, sunã yardar da ku da bãkunansu kuma zukãtansu
sunã ƙi? Kuma mafi yawansu fãsiƙai ne.
Sa'an nan idan sun tũba kuma suka tsayar da salla, kuma suka bãyar da zakka, to,
'yan'uwanku ne a cikin addini, kuma Munã rarrabe ãyõyi daki-daki, ga mutãne
waɗanda suke sani.
Kuma idan suka warware rantsuwõyin amãna daga bãyan alkawarinsu, kuma suka yi
sũka a cikin addininku, to, ku yaki shũgabannin kãfirci. Lalle ne sũ, bãbu
rantsuwõyin amãna a gare su. Tsammãninsu sunã hanuwa.
Shin, bã ku yaƙin mutãne, waɗanda suka warware rantsuwõyinsu, kuma suka yi niyya
ga fitar da Manzo, kuma sũ ne suka fãra muku, tun a farkon lõkaci? Shin kunã
tsõron su ne? To, Allah ne marfi cancantar ku ji tsõronSa, idan kun kasance
mũminai!
Kõ kunã zaton a bar ku, tun Allah bai bayyana waɗanda suka yi jihãdi ba daga
gare ku, kuma sũ ba su riƙi wani shigeba, baicin Allah da ManzonSa da mũminai?
Kuma Allah ne Mai jarrabãwa ga abin da kuke aikatãwa.
Bã ya kasancewa ga mãsu shirki su rãya masallatan Allah, alhãli kuwa sunã mãsu
bãyar da shaida a kan rãyukansu da kafirci, waɗannan ayyukansu sun ɓãci, kuma a
cikin wutã sũ madawwama
Abin sani kawai, mai rãya masallãtan Allah, shĩ ne wanda ya yi ĩmãni da Allah da
Rãnar Lãhira, kuma ya tsayar da salla kuma ya bãyar da zakka, kuma bai ji tsõron
kõwa ba fãce Allah. To, akwai tsammãnin waɗannan su kasance daga shiryayyu.
Shin, kun sanya shãyar da mahajjata da rãyar da Masallaci Mai alfarma kamar
wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya yi jihãɗi a cikin hanyar
Allah? Bã su daidaita a wurin Allah. Kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne
azzãlumai.
Waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi hijira, kuma suka yi jihãdi, a cikin hanyar
Allah, da dũkiyõyinsu, da rãyukansu, sũ ne mafi girma ga daraja, a wurin Allah,
kuma waɗannan sũ ne mãsu babban rabo.
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku riƙi ubanninku da 'yan'uwanku masõya, idan
sun nũna son kãfirci a kan ĩmãni. Kuma wanda ya jiɓince su daga gare ku, to,
waɗannan sũ ne azzãlumai.
Ka ce: "Idan ubanninku da ɗiyanku da 'yan'uwanku da mãtanku da danginku da
dũkiyõyi, waɗanda kuka yi tsiwirwirinsu, da fatauci wanda kuke tsõron
tasgaronsa, da gidaje waɗanda kuke yarda da su, sun kasance mafiya sõyuwa a gare
ku daga Allah da ManzonSa, da yin jihãdi ga hanyarSa, to, ku yi jira har Allah
Ya zo da umurninSa! Kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne fãsiƙai."
Lalle ne, haƙĩƙa, Allah Yã taimake ku a cikin wurãre mãsu yawa, da Rãnar
Hunainu, a lõkacin da yawanku ya bã ku sha'awa, sai bai amfãnar da ku da kõme
ba, kuma ƙasa ta yi ƙunci a kanku da yalwarta, sa'an nan kuma kuka jũya kunã
mãsu bãyar da bãya.
Sa'an nan kuma Allah Ya saukar da natsuwarSa a kan ManzonSa kuma a kan mũminai,
kuma Ya saukar da rundunõni waɗanda ba ku gan su ba, kuma Ya azabtar da waɗanda
suka kãfirta: Wancan ne sakamakon kãfirai.
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, mushirikai najasa ne, sabõda haka
kada su kusanci Masallaci Mai alfarma a bãyan shẽkararsu wannan. Kuma idan kun
ji tsõron talauci to, da sannu Allah zai wadãta ku daga falalarSa, idan Ya so.
Lalle Allah ne Masani, mai hikima.
Ku yãƙi waɗanda bã su yin ĩmãni da Allah kuma bã su ĩmãni da Rãnar Lãhira kumabã
su haramta abin da Allah da ManzonSa suka haramta, kuma bã su yin addini,
addinin gaskiya, daga waɗanda aka bai wa Littãfi, har sai sun bãyar da jizya
daga, hannu, kuma sunã ƙasƙantattu.
Kuma Yahũdãwa suka ce: "Uzairu ɗan Allah ne."Kuma Nasãra suka ce: "Masĩhu ɗan
Allah ne." Wancan zancensu ne da bãkunansu. Sunã kamã da maganar waɗanda suka
kãfirta daga gabãni. Allah Yã la'ance su! Yãya aka karkatar da su?
Sun riƙi mãlamansu (Yahũdu) da ruhubãnãwansu (Nasãra) Ubannangiji, baicin Allah,
kuma sun riƙi Masĩhu ɗan Maryama ( haka). Kuma ba a umurce su ba fãce da su
bautã wa Ubangiji Guda. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. TsarkinSa ya tabbata daga
barin abin da suke yin shirki da shi.
Yã waɗanda suka yi ĩmãni! Lalle ne mãsu yawa daga Ahbãr da Ruhbãnãwa haƙĩƙa sunã
cin dũkiyar mutãne da ƙarya, kuma sunã kangẽwa daga hanyar Allah. Kuma waɗanda
suke taskacẽwar zĩnãriya da azurfa, kuma bã su ciyar da ita a cikin hanyar
Allah, to, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
A Rãnar da ake ƙõna shi a kanta a cikin wutar Jahannama, sai a yi lalas da ita
ga gõshinansu da sãshinansu da bãyayyakinsu, (a ce musu): "Wannan ne abin da
kuka taskace dõmin rãyukanku. To, ku ɗanɗani abin da kuka kasance kunã sanyãwa a
taska."
Lallai ne ƙidãyayyun watanni a wurin Allah watã gõma shã biyu ne a cikin
Littãfin Allah, a Rãnar da Ya halicci sammai da ƙasa daga cikinsu akwai huɗu
mãsu alfarma. Wannan ne addini madaidaici. Sabõda haka kada ku zãlunci kanku a
cikinsu. Kuma ku yãƙi mushirikai gabã ɗaya, kamar yadda suke yãƙar ku gabã ɗaya.
Kuma ku sani cẽwa lallai ne Allah Yanã tãre da mãsu taƙawa.
Abin sani kawai, "Jinkirtãwa" ƙãri ne a cikin kãfirci, anã ɓatar da waɗanda suka
kãfirta game da shi. Sunã halattar da watã a wata shẽkara kuma su haramtar da
shi a wata shẽkara dõmin su dãce da adadin abin da Allah Ya haramta. Sabõda haka
sunã halattar da abin da Allah Ya haramtar. An ƙawãce musu mũnanan ayyukansu.
Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne kãfirai.
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Mẽne ne a gare ku, idan ance muku, "Ku fita da yãƙi
a cikin hanyar Allah," sai ku yi nauyi zuwa ga ƙasa. Shin, kun yarda da rãyuwar
dũniya ne daga ta Lãhira? To jin dãɗin rãyuwar dũniya bai zama ba a cikin
Lãhira, fãce kaɗan.
Idan ba ku fita da yãƙi ba, Allah zai azabta ku da azãba mai raɗaɗi, kuma Ya
musanya wasu mutãne, wasunku (a maimakonku). Kuma bã zã ku cũtar da Shida kõme
ba. Kuma Allah a kan dukan kõme Mai ĩkon yi ne.
Idan ba ku taimake shi ba, to, lalle ne Allah Yã taimake shi, a lõkacin da
waɗanda suka kãfirta suka fitar da shi, Yanã na biyun biyu, a lõkacin da suke
cikin kõgon dũtse, a lõkacin da yake cẽwa da sãhibinsa: "Kada ka yi baƙin ciki,
lalle ne Allah Yanã tãre da mu." Sai Allah Ya saukar da natsuwarSa a kansa, kuma
Ya taimake shi da waɗansu rundunõni, ba ku gan su ba, kuma Ya sanya kalmar
waɗanda suka kãfirta maƙasƙanciya, kuma kalmar Allah ita ce maɗaukakiya. Kuma
Allah ne Mabuwãyi, Mai hikima.
Ku fita da yãƙi kunã mãsu sauƙãƙan kãyã da mãsu nauyi, kuma ku yi jihãdi da
dũkiyõyinku da kuma rãyukanku a cikin hanyar Allah. Wancan ne mafi alhẽri a gare
ku, idan kun kasance kunã sani.
Dã yã kasance wata siffar dũniya ce: makusanciya, da tafiya matsakaiciya, dã sun
bĩ ka, kuma amma fagen yã yi musu nĩsa.Kuma zã su yi ta yin rantsuwa da Allah,
"Dã mun sãmi dãma, dã mun tafi tare da ku." Sunã halakar da kansu (da rantsuwar
ƙarya) ne, kuma Allah Yanã sanin lalle, haƙĩƙa, sumaƙaryata ne.'
Waɗanda suke yin ĩmãnida Allah da Rãnar Lãhira, bã zã su nẽmi izininka ga yin,
jihãdida dũkiyõyinsu da rãyukansu ba. Kuma Allah ne Masani ga mãsu taƙawa.
Abin sani kawai, waɗanda bã sa ĩmãni da Allah, da Rãnar Lãhira, kuma zukãtansu
suka yi shakka, sũ ne ke nẽman izininka, sa'an nan a cikin shakkarsu sunã ta yin
kai kãwo.
Kuma dã sun yi nufin fita, dã sun yi wani tattali sabõda shi, kuma amma Allah Ya
ƙi zãburarsu, sai Ya nauyayar da zamansu. Kuma aka ce ku zauna tãre da mãsu
zama.
Dã sun fita a cikinku bã zã su ƙãre ku da kõme ba fãce da ɓarna, kuma lalle dã
sun yi gaggãwar sanya annamĩmanci a tsakãninku, sunã nẽma muku fitina. Kuma a
cikinku akwai 'yan rahõto sabõda su. Kuma Allah ne Masani ga azzãlumai,
Kuma lalle ne, haƙĩƙa sun nẽmi fitina daga gabãni, kuma, suka jũya maka
al'amari, har gaskiya ta zo, kuma umurnin Allah Ya bayyana, alhãli sunã mãsu
ƙyãma,
Kuma daga cikinsu akwai mai cẽwa, "Ka yi mini izinin zama, kuma kada ka fitine
ni." To, a cikin fitinar suka fãɗa. Kuma lalle ne Jahannama, haƙĩƙa, mai
ƙẽwayẽwa ce ga kãfirai.
Idan wani alhẽri ya sãme ka, zai ɓãta musu rai, kuma idan wata masifa ta sãme ka
sai su ce: "Haƙĩƙa, mun riƙe al'amarinmu daga gabãni."Kuma sujũya, alhãli kuwa
sunã mãsu farin ciki.
Ka ce: "Shin, kunã dãko ne da mu? Fãce dai da ɗayan abũbuwan biyu mãsu kyau,
alhãli kuwa mũ, munã dãko da ku, AllahYa sãme ku da wata azãba daga gare Shi, kõ
kuwa da hannayenmu. To, ku yi dãko. Lalle ne mũ, tãre da ku mãsu dãkon ne."
Kuma bãbu abin da ya hana a karɓi ciyarwarsu daga gare su fãce dõmin sũ, sun
kãfirta da Allah da ManzonSa, kuma bã su zuwa ga salla fãce Luma sunã mãsu
kasãla, kuma bã su ciyarwa fãce sunã mãsu ƙyãma.
Sabõda haka, kada dũkiyõyinsu su bã ka sha'awa, kuma haka 'ya'yansu. Abin sani
kawai, Allah Yanã nufin Ya yi musu azãba, da su a cikin rãyuwar dũniya, kuma
rãyukansu su fita alhãli kuwa sunã kãfirai.
Kuma daga cikinsu akwai wanda yake zunɗen ka a kan sha'anin dũkiyõyin sadaka,
sai idan an bã su daga cikinta, su yarda, kuma idan ba a bã su ba daga cikinta
sai su zamo sunã mãsu fushi.
Kuma dã dai su lalle sun yarda da abin da Allah Ya bã su, da ManzonSa kuma suka
ce: "Ma'ishinmu Allah ne, zai kãwo mana daga falalarSa kuma ManzõnSa (zai bã
mu). Lalle ne mũ, zuwa ga Allah mãsu kwaɗayi ne."
Abin sani kawai, dũkiyõyin sadaka na faƙĩrai ne da miskinai da mãsu aiki a
kansu, da waɗanda ake lallãshin zukãtansu, kuma a cikin fansar wuyõyi, da
mabarta, da a cikin hanyar Allah da ɗan hanya (matafiyi). Farilla daga Allah.
Kuma Allah ne Masani, Mai hikima.
Kuma daga cikinsu akwai waɗanda suke cũtar Annabi, kuma sunã cẽwa "Shi kunne
ne." Ka ce: "Kunnen alhẽri gare ku,Yanã ĩmãni da Allah, kuma Yanã yarda da
mũminai, kuma rahama ne ga waɗanda suka yi ĩmãni daga gare ku."Kuma waɗanda suke
cũtar Manzon Allah sunã da azãba mai raɗaɗi.
Shin, ba su sani ba cẽwa "Lalle ne wanda ya sãɓa wa Allah da ManzonSa, haƙĩƙa
Yanã da wutar Jahannama, Yanã madawwami a cikinta? Waccan ita ce wulãkantãwa
babba!"
Munãfukai sunã tsõron a saukar da wata sũra a kansu,wadda take bã su lãbãri ga
abin da yake cikin zukãtansu. Ka ce: "Ku yi izgili. Lalle ne, Allah ne Mai fitai
da abin da kuke tsõro."
Kuma lalle ne, idan ka tambaye , su haƙĩƙa, sunã cẽwa, "Abin sani kawai, mun
kasance munã hĩra kuma munã wãsã. Ka ce: "Shin da Allah, da kuma ãyõyinSa da
ManzonSa kuka kasance kunã izgili?"
"Kada ku kãwo wani uzuri, haƙĩƙa, kun kãfirta a bãyanĩmãninku. Idan Mun yãfe
laifi ga wata ƙungiya daga gare ku, zã Mu azabta wata ƙungiya sabõda, lalle, sun
kasance mãsu laifi."
Munãfukai maza da munãfukai mãtã, sãshensu daga sãshe, sunã umurni da abin ƙi
kuma sunã hani daga alhẽri.Kuma sunã damƙẽwar hannayensu.Sun mance Allah, sai Ya
mantã da su. Lalle ne munãfukai sũ ne fãsiƙai.
Allah yã yi wa'adi ga munãfukai maza da munãfukai mãtã da kãfirai da wutar
Jahannama, sunã madawwama a cikinta. Ita ce ma'ishiyarsu. Kuma Allah Yã la'ance
su, kuma sunã da azãba zaunanniya.
Kamar waɗanda suke a gabãninku, sun kasance mafi tsananin ƙarfi daga gare ku,
kuma mafi yawan dũkiyõyi da ɗiya. Sai suka ji daɗi da rabonsu, sai kuka ji daɗi
da rabonku kamar yadda waɗanda suke a gabãninku suka ji dãɗi, da rabonsu, kuma
kuka kũtsa kamar kũtsãwarsu. Waɗancan ayyukansu sun ɓãci a dũniya da Lãhira,
kuma waɗannan sũ ne mãsu hasãra.
Shin lãbarin waɗanda suke a gabãninsu bai je musu ba, mutãnen Nũhu da Ãdãwa da
Samũdãwa da mutãnen Ibrãhĩm da Ma'abũta Madyana da waɗanda aka birkice?
Manzanninsu sun jẽ musu da ãyõyayi bayanannu. To, Allah bai kasance Yanã
zãluntar su ba, amma sun kasance rãyukansu suke zãlunta.
Kuma mummunai maza da mummunai mãtã sãshensu majiɓincin sãshe ne, sunã umurni da
alhẽri kuma sunã hani daga abin da bã a so, kuma sunã tsayar da salla, kuma sunã
bãyar da zakka, kuma sunãɗã'a ga Allah da ManzonSa. Waɗannan Allah zai yi musu
rahama. Lalle Allah ne Mabuwãyi, Mai hikima.
Kuma Allah Yã yi wa'adi ga mummunai maza da mummunai mãtã da gidãjen Aljanna
ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwamã a cikinsu, da wurãren zama
mãsu dãɗi a cikin gidãjen Aljannar. Kuma yarda daga Allah ce mafi girma. Wancan
shi ne babban rabo, mai girma.
Sunã rantsuwa da Allah, ba su faɗa ba, alhãli kuwa lalle ne, haƙĩƙa, sun faɗi
kalmar kãfirci, kuma; sun kãfirta a bãyan musuluntarsu, kuma sun yi himma ga
abin da ba su sãmu ba. Kuma ba su zargi kõme ba fãce dõmin Allah da ManzonSa Ya
wadãtar da su daga falalarSa. To, idan sun tũba zai kasance mafi alhẽri gare
su,kuma idan sun jũya bãya, Allah zaiazabtã su da azãba mai raɗaɗi a cikin
dũniya da Lãhira, kuma bã su da wani masõyi kõ wani mataimaki a cikin kasa.
Kuma daga cikinsu akwai wadɗanda suka yi wa Allah alkawari, "Lalle ne idan ya
kãwo mana daga falalarSa, haƙĩƙa, munãbãyar da sadaka, kuma lalle ne munã
kasancẽwa, daga sãlihai."
Sai Ya biyar musu da munãfunci a cikin zukatansu har zuwa ga Rãnar da suke
haɗuwa da Shi sabõda sãɓã wa Allah a abin da suka yi Masa alkawari, kuma sabõda
abin da suka kasance sunã yi na ƙarya.
Waɗanda suke aibanta mãsu yin alhẽri daga mummunaia cikin dũkiyõyin sadaka, da
waɗanda ba su sãmu fãce iyãkar ƙõƙarinsu, sai sanã yi musu izgili. Allah Yanã
yin izgili gare su. Kuma sunã da azãba mai raɗaɗi.
Kõ kã nẽma musu gãfara ko ba ka nẽma musu ba, idan ka nẽma musu gãfara sau
saba'in, to, Allah bã zai gãfarta musu ba. Sabõda sũ, sun kãfirta da Allah da
ManzonSa. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne fãsiƙai.
Waɗanda aka bari sun yi farin ciki da zamansu a bãyan Manzon Allah, kuma suka ƙi
su yi jihãdi da dũkiyõyinsu da rãyukansu a cikin hanyar Allah, kuma suka ce:
"Kada ku fita zuwa yãƙi a cikin zãfi."Ka ce: "Wutar Jahannama ce mafi tsanlnin
zãfi." Dã sun kasance sunã fahimta!
To, idan Allah Ya mayar da kai zuwa ga wata ƙungiyã daga gare su sa'an nan suka
nẽme ka izni dõmin su fita, to, ka ce: "Bã zã ku fita tãre da nĩ ba har
abada,kuma bã zã ku yi yãƙi tãre da nĩ ba a kan wani maƙiyi. Lalle ne kũ, kun
yarda da zama a farkon lõkaci, sai ku zauna tãre da mãtã mãsu zaman gida."
Kuma kada ka yi salla a kan kõwa daga cikinsu wanda ya mutu, har abada, kuma
kada ka tsaya a kan kabarinsa. Lalle ne sũ, sun kãfirta da Allah da ManzonSa,
kuma sun mutu alhãli kuwa sunã fãsiƙai.
Kuma kada dũkiyõyinsu da ɗiyansu su bã ka sha'awa. Abin sani kawai, Allah Yanã
nufin Ya yi musu azãba da su a cikin dũniya, kuma rãyukansu su fita alhãli kuwa
sunã kãfirai.
Kuma idan aka saukar da wata sũra cẽwa; Ku yi ĩmãni da Allah kuma ku yi jihãdi
tãre da ManzionSa. Sai mawadãta daga gare su su nẽmi izninka, kuma su ce: Ka bar
mu mu kasance tãre da mazauna.
Amma Manzon Allah da waɗanda suka yi ĩmãni tãre da shi, sun yi jihãdi da
dũkiyõyinsu da rãyukansu. Kuma waɗannan sunã da ayyukan alhẽri, kuma waɗannan sũ
ne mãsu cin nasara.
Kuma mãsu uzuri daga ƙauyãwa zuka zo dõmin a yi musu izini, kuma waɗanda suka yi
wa Allah da ManzonSa ƙarya, suka yi zamansu. wata azãba mai raɗaɗi zã ta sãmi
waɗanda suka kãfirta daga gare su.
Bãbu laifi a kan maraunana kuma haka majinyata, kuma bãbu laifi a kan waɗanda bã
su sãmun abin da suke ciyarwa idan sun yi nasĩha ga Allah da ManzonSa. Kuma bãbu
wani laifi a kan mãsu kyautatãwa. Kuma Allah ne Mai gãfara, Mai tausayi.
Kuma bãbu (laifi) a kan waɗanda idan sun je maka dõmin ka ɗauke su ka ce: "Bã ni
da abin da nake ɗaukar ku a kansa," suka jũya alhãli kuwa idãnunsu sunã zubar da
hawãye dõmin baƙin ciki cẽwa ba su sãmi abin da suke ciyarwa ba.
Abin sani kawai, laifi Yanã a kan waɗanda suke nẽman izininka alhãli kuwa sũ
mawadãta ne.Sun yarda su kasance tãre da mãtã mamaya (gidãje), kuma Allah Yã
danne a kan zukãtansu, dõmin haka sũ, bã su gãnẽwa.
Sunã kãwo uzurinsu zuwa gare ku idan kun kõma zuwa gare su Ka ce: "Kada ku kãwo
wani uzuri, bã zã mu amince muku ba. Haƙĩƙa, Allah Yã bã mu lãbãri daga
lãbãrunku, Allah zai ga aikinku kuma ManzonSa (zai gani). Sa'an nan kuma a mayar
da ku zuwa ga Masanin gaibi da bayyane, sai Ya bã ku lãbarin abin da kuka
kasance kunã aikatãwa."
Zã su yi rantsuwa da Allah a gare ku idan kun jũya zuwa gare su, dõmin ku kau da
kai daga gare su. To, ku kau da kai daga gare su don kõ sũ ƙarantã ne, kuma
Jahannama ce matattararsu bisa ga sãkamakon abin da suka kasance sunã
tsirfatãwa.
¡auyãwã ne mafi tsananin kãfirci da munãfinci, kuma sũne mafi kamanta ga, rashin
sanin haddõjin abin da Allah Ya saukar a kan ManzonSa. Kuma Allah ne Masani, Mai
hikima.
Kuma daga ƙauyãwã akwai waɗanda suke riƙon abin da suke ciyarwa a kan tãra ce,
kuma sunã saurãron aukuwar masĩfa a gare ku, aukuwar mummunar masĩfa ta tabbata
a kansu. Kuma Allah ne Mai ji, Masani.
Kuma daga ƙauyãwã akawi waɗanda suke yin ĩmanida Allah da Rãnar Lãhira, kuma
sunã riƙon abin da suke ciyarwa (tamkar) waɗansu ibãdõdin nẽman kusanta ne a
wurin Allah da addu'õ'in ManzonSa. To, lalle ne ita (ciyarwar nan) ibãdar nẽman
kusanta ce a gare su. Allah zai shigar da su a cikin RahamarSa. Lalle Allah ne
Mai gãfara, Mai jin ƙai.
Kuma mãsu tsẽrẽwa na farko daga Muhãjirina da Ansar da waɗanda suka bi su da
kyautatãwa, Allah Ya yarda daga gare su su kuma sun yarda daga gare Shi, kuma Ya
yi mãsu tattalin gidãjen Aljanna; ¡õramu sunã gudãna a ƙarƙashinsu, suna
madawwamã a cikinsu har abada. Wancan ne babban rabo mai girma.
Kuma daga waɗanda suke a gẽfenku daga ƙauyãwa akwai munãfukai, haka kuma daga
mutãnen Madnĩa. Sun gõge a kan munãfunci, bã ka sanin su, Mũ ne Muke sanin su.
zã Mu yi musu azãba sau biyu, sa'an nan a mayar da su zuwa ga azãba mai girma.
Kuma da waɗansu, sun yi furuci da laifinsu, sun haɗa aiki na ƙwarai da wani
mummuna. Akwai tsammãnin Allah Ya karɓi tũba a kansu. Lallai Allah ne Mai
gãfara, Mai jin ƙai.
Ka karɓi sadaka daga dũkiyõyinsu kana tsarkake su, kuma kana tabbatar da
kirkinsu da ita. Kuma ka yi musu addu'a. Lallai addu'õ'inKa natsuwã ne a gare
su. Kuma Allah ne Mai ji, Masani.
Shin, ba su sani ba cẽwa lallai Allah, ne Yake karɓar tũbã daga bãyinSa, kuma
Yanã karɓar sadakõkinsu, kuma lalle Allah ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai?
Kuma ka ce: "Ku yi aiki, sa'an nan Allah zai ga aikinku, da ManzonSa da Muminai
kuma zã a mayar da ku zuwa ga masanin fake da bayyane, sa'an nan Ya bã ku lãbãri
ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
Kuma waɗanda suka riƙi wani masallãci dõmin cũta da kãfirci da nẽman rarrabẽwa a
tsakãnin muminai da fakẽwã ga taimakon wanda ya yãƙi Allah da ManzonSa daga
gabãni, kuma haƙĩƙa sunã yin rantsuwa cẽwa, "Ba mu yi nufin kõmai ba fãce
alhẽri", alhãli kuwa Allah Yanã yin shaida cẽwa,su, haƙĩƙa, maƙaryata ne.
Kada ka tsaya a cikinsa har abada. Lalle ne, Masallaci wanda aka yi harsãshinsa
a kan taƙawa tun farkon yini, shĩ ne mafi cancantar ka tsaya a cikinsa. A
cikinsa akwai waɗansu maza sunã son su tsarkaka. Kuma Allah Yanã son mãsu nẽman
tsarkakuwa.
Shin, wanda ya sanya harsãshin gininsa a kan taƙawa daga Allah da yarda, shi ne
mafi alhẽri kõ kuwa wanda ya sanya harsãshin gininsa a kan gãɓar rãmi mai
tusgãwa? Sai ya rũsa da shi a cikin wutar Jahannama. Kuma Allah bã Ya shiryar da
mutãne azzãlumai.
Lalle ne, Allah Ya saya daga mummunai, rãyukansu da dũkiyõyinsu, da cẽwa sunã da
Aljanna, sunã yin yãƙi a cikin hanyar Allah, sabõda haka sunã kashẽwa anã kashẽ
su. (Allah Yã yi)wa'adi a kanSa, tabbace a cikin Attaura da Linjĩla da
Alƙur'ãni. Kuma wãne ne mafi cikãwa da alkawarinsa daga Allah? Sabõda haka ku yi
bushãra da cinikinku wanda kuka ƙulla da Shi. Kuma wancan shi ne babban rabo,
mai girma.
Mãsu tũba, mãsu bautãwa, mãsu gõdẽwa, mãsu tafiya, mãsu ruku'i, mãsu sujada mãsu
umurni da alhẽri da mãsu hani daga abin da aka ƙi da mãsu tsarẽwaã ga iyãkõkin
Allah. Kuma ka bãyar da bushãra ga muminai.
Bã ya kasancẽwa ga Annabi da waɗanda suka yi ĩmãni, su yi istigifãri ga
mushirikai, kuma kõ dã sun kasance ma'abũta zumunta ne daga bãyan sun bayyana a
gare su, cẽwa lalle ne, sũ, 'yan Jahĩm ne.
Kuma istigifãrin Ibrãhĩm ga ubansa bai kasance ba fãce sabõda wani wa'adi ne da
ya ƙulla alƙawarinsa da shi, sa'an nan a lõkacin da ya bayyana a gare shi
(Ibrãhĩm) cẽwa lalle ne shĩ (ubansa) maƙiyi ne ga Allah, sai ya barranta daga
gare shi. Lalle ne Ibrahim, haƙĩƙa, mai yawan addu'a ne, mai haƙuri.
Kuma Allah bai kasance mai ɓatar da mutãne a bãyan Yã shiryar da su ba, sai Ya
bayyanã musu abin da zã su yi taƙawa da shi. Lalle ne Alllh, ga kõme, Masani ne.
Lalle ne, haƙĩƙa, Allah Ya karɓi tũbar Anbabi da Muhãjirĩna da Ansãr waɗanda
suka bĩ shi, a cikin sã'ar tsanani, daga bãya zukãtan wani ɓangare daga gare su
sun yi kusa su karkata, sa'an nan ( Allah) Ya karɓi tũbarsu. Lalle, Shĩ ne Mai
tausayi, Mai jin ƙai gare su.
Kuma (Allah) Yã karɓi tũba a kan ukun nan waɗanda aka jinkirtar har ƙasa da
yalwarta ta yi ƙunci a kansu, kuma rãyukansu suka yi ƙunci a kansu, kuma suka yi
zaton bãbu wata mafakã daga Allah fãce (kõmãwa) zuwa gare Shi. Sa'an nan Allah
Ya karɓi tũbarsu, dõmin su tabbata a kan tũba. Lalle Allah ne Mai karɓar tũba,
Mai jin ƙai.