« Prev

82. Surah Al-Infitâr سورة الإنفطار

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
إِذَا السَّمَاءُ انفَطَرَتْ
Hausa
 
Idan sama ta tsãge.

Ayah   82:2   الأية
وَإِذَا الْكَوَاكِبُ انتَثَرَتْ
Hausa
 
Kuma idan taurãri suka wãtse.

Ayah   82:3   الأية
وَإِذَا الْبِحَارُ فُجِّرَتْ
Hausa
 
Kuma idan tẽkuna aka facce su.

Ayah   82:4   الأية
وَإِذَا الْقُبُورُ بُعْثِرَتْ
Hausa
 
Kuma idan kaburbura aka tõne su.

Ayah   82:5   الأية
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ
Hausa
 
Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.

Ayah   82:6   الأية
يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ الْكَرِيمِ
Hausa
 
Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.

Ayah   82:7   الأية
الَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّاكَ فَعَدَلَكَ
Hausa
 
Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.

Ayah   82:8   الأية
فِي أَيِّ صُورَةٍ مَّا شَاءَ رَكَّبَكَ
Hausa
 
A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.

Ayah   82:9   الأية
كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِالدِّينِ
Hausa
 
A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!

Ayah   82:10   الأية
وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَافِظِينَ
Hausa
 
Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.

Ayah   82:11   الأية
كِرَامًا كَاتِبِينَ
Hausa
 
Mãsu daraja, marubũta.

Ayah   82:12   الأية
يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ
Hausa
 
Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.

Ayah   82:13   الأية
إِنَّ الْأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍ
Hausa
 
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.

Ayah   82:14   الأية
وَإِنَّ الْفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٍ
Hausa
 
Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.

Ayah   82:15   الأية
يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ الدِّينِ
Hausa
 
Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.

Ayah   82:16   الأية
وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَائِبِينَ
Hausa
 
Bã zã su faku daga gare ta ba.

Ayah   82:17   الأية
وَمَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ
Hausa
 
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?

Ayah   82:18   الأية
ثُمَّ مَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ
Hausa
 
Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?

Ayah   82:19   الأية
يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌ لِّنَفْسٍ شَيْئًا ۖ وَالْأَمْرُ يَوْمَئِذٍ لِّلَّهِ
Hausa
 
Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake. 
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us