« Prev
82. Surah Al-Infitâr سورة الإنفطار
Next »
First Ayah 1 الأية الأوليبِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
إِذَا السَّمَاءُ انفَطَرَتْ
Hausa
Idan sama ta tsãge.
|
Ayah 82:2 الأية
وَإِذَا الْكَوَاكِبُ انتَثَرَتْ
Hausa
Kuma idan taurãri suka wãtse.
|
Ayah 82:3 الأية
وَإِذَا الْبِحَارُ فُجِّرَتْ
Hausa
Kuma idan tẽkuna aka facce su.
|
Ayah 82:4 الأية
وَإِذَا الْقُبُورُ بُعْثِرَتْ
Hausa
Kuma idan kaburbura aka tõne su.
|
Ayah 82:5 الأية
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ
Hausa
Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.
|
Ayah 82:6 الأية
يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ الْكَرِيمِ
Hausa
Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.
|
Ayah 82:7 الأية
الَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّاكَ فَعَدَلَكَ
Hausa
Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.
|
Ayah 82:8 الأية
فِي أَيِّ صُورَةٍ مَّا شَاءَ رَكَّبَكَ
Hausa
A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.
|
Ayah 82:9 الأية
كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِالدِّينِ
Hausa
A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!
|
Ayah 82:10 الأية
وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَافِظِينَ
Hausa
Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.
|
Ayah 82:11 الأية
كِرَامًا كَاتِبِينَ
Hausa
Mãsu daraja, marubũta.
|
Ayah 82:12 الأية
يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ
Hausa
Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.
|
Ayah 82:13 الأية
إِنَّ الْأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍ
Hausa
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.
|
Ayah 82:14 الأية
وَإِنَّ الْفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٍ
Hausa
Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.
|
Ayah 82:15 الأية
يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ الدِّينِ
Hausa
Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.
|
Ayah 82:16 الأية
وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَائِبِينَ
Hausa
Bã zã su faku daga gare ta ba.
|
Ayah 82:17 الأية
وَمَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ
Hausa
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?
|
Ayah 82:18 الأية
ثُمَّ مَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ
Hausa
Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?
|
Ayah 82:19 الأية
يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌ لِّنَفْسٍ شَيْئًا ۖ وَالْأَمْرُ يَوْمَئِذٍ لِّلَّهِ
Hausa
Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar
nan, ga Allah (ɗai) yake.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|
|