« Prev

70. Surah Al-Ma'ârij سورة المعارج

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
سَأَلَ سَائِلٌ بِعَذَابٍ وَاقِعٍ
Hausa
 
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.

Ayah   70:2   الأية
لِّلْكَافِرِينَ لَيْسَ لَهُ دَافِعٌ
Hausa
 
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.

Ayah   70:3   الأية
مِّنَ اللَّهِ ذِي الْمَعَارِجِ
Hausa
 
Daga Allah Mai matãkala.

Ayah   70:4   الأية
تَعْرُجُ الْمَلَائِكَةُ وَالرُّوحُ إِلَيْهِ فِي يَوْمٍ كَانَ مِقْدَارُهُ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍ
Hausa
 
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.

Ayah   70:5   الأية
فَاصْبِرْ صَبْرًا جَمِيلًا
Hausa
 
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.

Ayah   70:6   الأية
إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُ بَعِيدًا
Hausa
 
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.

Ayah   70:7   الأية
وَنَرَاهُ قَرِيبًا
Hausa
 
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.

Ayah   70:8   الأية
يَوْمَ تَكُونُ السَّمَاءُ كَالْمُهْلِ
Hausa
 
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.

Ayah   70:9   الأية
وَتَكُونُ الْجِبَالُ كَالْعِهْنِ
Hausa
 
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.

Ayah   70:10   الأية
وَلَا يَسْأَلُ حَمِيمٌ حَمِيمًا
Hausa
 
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.

Ayah   70:11   الأية
يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ الْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِي مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍ بِبَنِيهِ
Hausa
 
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

Ayah   70:12   الأية
وَصَاحِبَتِهِ وَأَخِيهِ
Hausa
 
Da matarsa da ɗan'uwansa.

Ayah   70:13   الأية
وَفَصِيلَتِهِ الَّتِي تُؤْوِيهِ
Hausa
 
Da danginsa, mãsu tattarã shi.

Ayah   70:14   الأية
وَمَن فِي الْأَرْضِ جَمِيعًا ثُمَّ يُنجِيهِ
Hausa
 
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

Ayah   70:15   الأية
كَلَّا ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ
Hausa
 
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

Ayah   70:16   الأية
نَزَّاعَةً لِّلشَّوَىٰ
Hausa
 
Mai twãle fãtar goshi.

Ayah   70:17   الأية
تَدْعُو مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ
Hausa
 
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

Ayah   70:18   الأية
وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰ
Hausa
 
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

Ayah   70:19   الأية
إِنَّ الْإِنسَانَ خُلِقَ هَلُوعًا
Hausa
 
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

Ayah   70:20   الأية
إِذَا مَسَّهُ الشَّرُّ جَزُوعًا
Hausa
 
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

Ayah   70:21   الأية
وَإِذَا مَسَّهُ الْخَيْرُ مَنُوعًا
Hausa
 
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

Ayah   70:22   الأية
إِلَّا الْمُصَلِّينَ
Hausa
 
Sai mãsu yin salla,

Ayah   70:23   الأية
الَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَائِمُونَ
Hausa
 
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

Ayah   70:24   الأية
وَالَّذِينَ فِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ مَّعْلُومٌ
Hausa
 
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

Ayah   70:25   الأية
لِّلسَّائِلِ وَالْمَحْرُومِ
Hausa
 
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

Ayah   70:26   الأية
وَالَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ الدِّينِ
Hausa
 
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

Ayah   70:27   الأية
وَالَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ
Hausa
 
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

Ayah   70:28   الأية
إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍ
Hausa
 
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

Ayah   70:29   الأية
وَالَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ
Hausa
 
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

Ayah   70:30   الأية
إِلَّا عَلَىٰ أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ
Hausa
 
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

Ayah   70:31   الأية
فَمَنِ ابْتَغَىٰ وَرَاءَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْعَادُونَ
Hausa
 
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

Ayah   70:32   الأية
وَالَّذِينَ هُمْ لِأَمَانَاتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَاعُونَ
Hausa
 
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

Ayah   70:33   الأية
وَالَّذِينَ هُم بِشَهَادَاتِهِمْ قَائِمُونَ
Hausa
 
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

Ayah   70:34   الأية
وَالَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ
Hausa
 
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

Ayah   70:35   الأية
أُولَٰئِكَ فِي جَنَّاتٍ مُّكْرَمُونَ
Hausa
 
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

Ayah   70:36   الأية
فَمَالِ الَّذِينَ كَفَرُوا قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ
Hausa
 
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).

Ayah   70:37   الأية
عَنِ الْيَمِينِ وَعَنِ الشِّمَالِ عِزِينَ
Hausa
 
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!

Ayah   70:38   الأية
أَيَطْمَعُ كُلُّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍ
Hausa
 
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?

Ayah   70:39   الأية
كَلَّا ۖ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ
Hausa
 
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.

Ayah   70:40   الأية
فَلَا أُقْسِمُ بِرَبِّ الْمَشَارِقِ وَالْمَغَارِبِ إِنَّا لَقَادِرُونَ
Hausa
 
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.

Ayah   70:41   الأية
عَلَىٰ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
Hausa
 
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.

Ayah   70:42   الأية
فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا وَيَلْعَبُوا حَتَّىٰ يُلَاقُوا يَوْمَهُمُ الَّذِي يُوعَدُونَ
Hausa
 
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita) .

Ayah   70:43   الأية
يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ الْأَجْدَاثِ سِرَاعًا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍ يُوفِضُونَ
Hausa
 
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.

Ayah   70:44   الأية
خَاشِعَةً أَبْصَارُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۚ ذَٰلِكَ الْيَوْمُ الَّذِي كَانُوا يُوعَدُونَ
Hausa
 
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us