« Prev

69. Surah Al-Hâqqah سورة الحاقة

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الْحَاقَّةُ
Hausa
 
Kiran gaskiya!

Ayah   69:2   الأية
مَا الْحَاقَّةُ
Hausa
 
Mẽne ne kiran gaskiya?

Ayah   69:3   الأية
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحَاقَّةُ
Hausa
 
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?

Ayah   69:4   الأية
كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌ بِالْقَارِعَةِ
Hausa
 
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!

Ayah   69:5   الأية
فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا بِالطَّاغِيَةِ
Hausa
 
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.

Ayah   69:6   الأية
وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ
Hausa
 
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.

Ayah   69:7   الأية
سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَانِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى الْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ
Hausa
 
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.

Ayah   69:8   الأية
فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّن بَاقِيَةٍ
Hausa
 
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?

Ayah   69:9   الأية
وَجَاءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُ وَالْمُؤْتَفِكَاتُ بِالْخَاطِئَةِ
Hausa
 
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.

Ayah   69:10   الأية
فَعَصَوْا رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةً
Hausa
 
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).

Ayah   69:11   الأية
إِنَّا لَمَّا طَغَى الْمَاءُ حَمَلْنَاكُمْ فِي الْجَارِيَةِ
Hausa
 
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.

Ayah   69:12   الأية
لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَا أُذُنٌ وَاعِيَةٌ
Hausa
 
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

Ayah   69:13   الأية
فَإِذَا نُفِخَ فِي الصُّورِ نَفْخَةٌ وَاحِدَةٌ
Hausa
 
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.

Ayah   69:14   الأية
وَحُمِلَتِ الْأَرْضُ وَالْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَاحِدَةً
Hausa
 
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.

Ayah   69:15   الأية
فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ الْوَاقِعَةُ
Hausa
 
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.

Ayah   69:16   الأية
وَانشَقَّتِ السَّمَاءُ فَهِيَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌ
Hausa
 
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.

Ayah   69:17   الأية
وَالْمَلَكُ عَلَىٰ أَرْجَائِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَانِيَةٌ
Hausa
 
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.

Ayah   69:18   الأية
يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌ
Hausa
 
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.

Ayah   69:19   الأية
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ فَيَقُولُ هَاؤُمُ اقْرَءُوا كِتَابِيَهْ
Hausa
 
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."

Ayah   69:20   الأية
إِنِّي ظَنَنتُ أَنِّي مُلَاقٍ حِسَابِيَهْ
Hausa
 
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."

Ayah   69:21   الأية
فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ
Hausa
 
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.

Ayah   69:22   الأية
فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٍ
Hausa
 
A cikin Aljanna maɗaukakiya.

Ayah   69:23   الأية
قُطُوفُهَا دَانِيَةٌ
Hausa
 
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),

Ayah   69:24   الأية
كُلُوا وَاشْرَبُوا هَنِيئًا بِمَا أَسْلَفْتُمْ فِي الْأَيَّامِ الْخَالِيَةِ
Hausa
 
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."

Ayah   69:25   الأية
وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِشِمَالِهِ فَيَقُولُ يَا لَيْتَنِي لَمْ أُوتَ كِتَابِيَهْ
Hausa
 
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"

Ayah   69:26   الأية
وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ
Hausa
 
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"

Ayah   69:27   الأية
يَا لَيْتَهَا كَانَتِ الْقَاضِيَةَ
Hausa
 
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!

Ayah   69:28   الأية
مَا أَغْنَىٰ عَنِّي مَالِيَهْ ۜ
Hausa
 
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"

Ayah   69:29   الأية
هَلَكَ عَنِّي سُلْطَانِيَهْ
Hausa
 
"Ĩkona ya ɓace mini!"

Ayah   69:30   الأية
خُذُوهُ فَغُلُّوهُ
Hausa
 
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."

Ayah   69:31   الأية
ثُمَّ الْجَحِيمَ صَلُّوهُ
Hausa
 
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."

Ayah   69:32   الأية
ثُمَّ فِي سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَاسْلُكُوهُ
Hausa
 
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."

Ayah   69:33   الأية
إِنَّهُ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِاللَّهِ الْعَظِيمِ
Hausa
 
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"

Ayah   69:34   الأية
وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ
Hausa
 
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"

Ayah   69:35   الأية
فَلَيْسَ لَهُ الْيَوْمَ هَاهُنَا حَمِيمٌ
Hausa
 
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."

Ayah   69:36   الأية
وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍ
Hausa
 
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."

Ayah   69:37   الأية
لَّا يَأْكُلُهُ إِلَّا الْخَاطِئُونَ
Hausa
 
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."

Ayah   69:38   الأية
فَلَا أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ
Hausa
 
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,

Ayah   69:39   الأية
وَمَا لَا تُبْصِرُونَ
Hausa
 
Da abin da bã ku iya gani.

Ayah   69:40   الأية
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
Hausa
 
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

Ayah   69:41   الأية
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تُؤْمِنُونَ
Hausa
 
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.

Ayah   69:42   الأية
وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تَذَكَّرُونَ
Hausa
 
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.

Ayah   69:43   الأية
تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.

Ayah   69:44   الأية
وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ الْأَقَاوِيلِ
Hausa
 
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.

Ayah   69:45   الأية
لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِالْيَمِينِ
Hausa
 
Dã Mun kãma shi da dãma.

Ayah   69:46   الأية
ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ الْوَتِينَ
Hausa
 
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.

Ayah   69:47   الأية
فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَاجِزِينَ
Hausa
 
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.

Ayah   69:48   الأية
وَإِنَّهُ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَ
Hausa
 
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

Ayah   69:49   الأية
وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ
Hausa
 
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.

Ayah   69:50   الأية
وَإِنَّهُ لَحَسْرَةٌ عَلَى الْكَافِرِينَ
Hausa
 
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.

Ayah   69:51   الأية
وَإِنَّهُ لَحَقُّ الْيَقِينِ
Hausa
 
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.

Ayah   69:52   الأية
فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ
Hausa
 
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us