First Ayah 1 الأية الأوليبِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الْحَاقَّةُ
Hausa
Kiran gaskiya!
|
Ayah 69:2 الأية
مَا الْحَاقَّةُ
Hausa
Mẽne ne kiran gaskiya?
|
Ayah 69:3 الأية
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحَاقَّةُ
Hausa
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
|
Ayah 69:4 الأية
كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌ بِالْقَارِعَةِ
Hausa
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
|
Ayah 69:5 الأية
فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا بِالطَّاغِيَةِ
Hausa
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
|
Ayah 69:6 الأية
وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ
Hausa
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare
haddi.
|
Ayah 69:7 الأية
سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَانِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى
الْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ
Hausa
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna,
sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne,
waɗanda suka fãɗi.
|
Ayah 69:8 الأية
فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّن بَاقِيَةٍ
Hausa
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
|
Ayah 69:9 الأية
وَجَاءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُ وَالْمُؤْتَفِكَاتُ بِالْخَاطِئَةِ
Hausa
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu,
sabõda laifi.
|
Ayah 69:10 الأية
فَعَصَوْا رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةً
Hausa
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu
mai ƙãruwar (tsanani).
|
Ayah 69:11 الأية
إِنَّا لَمَّا طَغَى الْمَاءُ حَمَلْنَاكُمْ فِي الْجَارِيَةِ
Hausa
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin
ruwan nan.
|
Ayah 69:12 الأية
لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَا أُذُنٌ وَاعِيَةٌ
Hausa
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye
(shi).
|
Ayah 69:13 الأية
فَإِذَا نُفِخَ فِي الصُّورِ نَفْخَةٌ وَاحِدَةٌ
Hausa
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
|
Ayah 69:14 الأية
وَحُمِلَتِ الْأَرْضُ وَالْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَاحِدَةً
Hausa
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
|
Ayah 69:15 الأية
فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ الْوَاقِعَةُ
Hausa
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
|
Ayah 69:16 الأية
وَانشَقَّتِ السَّمَاءُ فَهِيَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌ
Hausa
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
|
Ayah 69:17 الأية
وَالْمَلَكُ عَلَىٰ أَرْجَائِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ
يَوْمَئِذٍ ثَمَانِيَةٌ
Hausa
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na
ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
|
Ayah 69:18 الأية
يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌ
Hausa
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga
cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
|
Ayah 69:19 الأية
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ فَيَقُولُ هَاؤُمُ اقْرَءُوا
كِتَابِيَهْ
Hausa
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku
karɓa, ku karanta littafina."
|
Ayah 69:20 الأية
إِنِّي ظَنَنتُ أَنِّي مُلَاقٍ حِسَابِيَهْ
Hausa
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
|
Ayah 69:21 الأية
فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ
Hausa
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
|
Ayah 69:22 الأية
فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٍ
Hausa
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
|
Ayah 69:23 الأية
قُطُوفُهَا دَانِيَةٌ
Hausa
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
|
Ayah 69:24 الأية
كُلُوا وَاشْرَبُوا هَنِيئًا بِمَا أَسْلَفْتُمْ فِي الْأَيَّامِ الْخَالِيَةِ
Hausa
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a
cikin kwãnukan da suka shige."
|
Ayah 69:25 الأية
وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِشِمَالِهِ فَيَقُولُ يَا لَيْتَنِي لَمْ أُوتَ
كِتَابِيَهْ
Hausa
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini
littãfina ba!"
|
Ayah 69:26 الأية
وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ
Hausa
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
|
Ayah 69:27 الأية
يَا لَيْتَهَا كَانَتِ الْقَاضِيَةَ
Hausa
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
|
Ayah 69:28 الأية
مَا أَغْنَىٰ عَنِّي مَالِيَهْ ۜ
Hausa
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
|
Ayah 69:29 الأية
هَلَكَ عَنِّي سُلْطَانِيَهْ
Hausa
"Ĩkona ya ɓace mini!"
|
Ayah 69:30 الأية
خُذُوهُ فَغُلُّوهُ
Hausa
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
|
Ayah 69:31 الأية
ثُمَّ الْجَحِيمَ صَلُّوهُ
Hausa
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
|
Ayah 69:32 الأية
ثُمَّ فِي سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَاسْلُكُوهُ
Hausa
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
|
Ayah 69:33 الأية
إِنَّهُ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِاللَّهِ الْعَظِيمِ
Hausa
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
|
Ayah 69:34 الأية
وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ
Hausa
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"
|
Ayah 69:35 الأية
فَلَيْسَ لَهُ الْيَوْمَ هَاهُنَا حَمِيمٌ
Hausa
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
|
Ayah 69:36 الأية
وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍ
Hausa
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
|
Ayah 69:37 الأية
لَّا يَأْكُلُهُ إِلَّا الْخَاطِئُونَ
Hausa
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
|
Ayah 69:38 الأية
فَلَا أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ
Hausa
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
|
Ayah 69:39 الأية
وَمَا لَا تُبْصِرُونَ
Hausa
Da abin da bã ku iya gani.
|
Ayah 69:40 الأية
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
Hausa
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
|
Ayah 69:41 الأية
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تُؤْمِنُونَ
Hausa
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
|
Ayah 69:42 الأية
وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تَذَكَّرُونَ
Hausa
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
|
Ayah 69:43 الأية
تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
|
Ayah 69:44 الأية
وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ الْأَقَاوِيلِ
Hausa
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
|
Ayah 69:45 الأية
لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِالْيَمِينِ
Hausa
Dã Mun kãma shi da dãma.
|
Ayah 69:46 الأية
ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ الْوَتِينَ
Hausa
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
|
Ayah 69:47 الأية
فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَاجِزِينَ
Hausa
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
|
Ayah 69:48 الأية
وَإِنَّهُ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَ
Hausa
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
|
Ayah 69:49 الأية
وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ
Hausa
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
|
Ayah 69:50 الأية
وَإِنَّهُ لَحَسْرَةٌ عَلَى الْكَافِرِينَ
Hausa
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
|
Ayah 69:51 الأية
وَإِنَّهُ لَحَقُّ الْيَقِينِ
Hausa
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
|
Ayah 69:52 الأية
فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِ
Hausa
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|