« Prev

96. Surah Al-'Alaq سورة العلق

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
اقْرَأْ بِاسْمِ رَبِّكَ الَّذِي خَلَقَ
Hausa
 
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.

Ayah   96:2   الأية
خَلَقَ الْإِنسَانَ مِنْ عَلَقٍ
Hausa
 
Ya hahitta mutum daga gudan jini.

Ayah   96:3   الأية
اقْرَأْ وَرَبُّكَ الْأَكْرَمُ
Hausa
 
Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.

Ayah   96:4   الأية
الَّذِي عَلَّمَ بِالْقَلَمِ
Hausa
 
Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.

Ayah   96:5   الأية
عَلَّمَ الْإِنسَانَ مَا لَمْ يَعْلَمْ
Hausa
 
Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.

Ayah   96:6   الأية
كَلَّا إِنَّ الْإِنسَانَ لَيَطْغَىٰ
Hausa
 
A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).

Ayah   96:7   الأية
أَن رَّآهُ اسْتَغْنَىٰ
Hausa
 
Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.

Ayah   96:8   الأية
إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ الرُّجْعَىٰ
Hausa
 
Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.

Ayah   96:9   الأية
أَرَأَيْتَ الَّذِي يَنْهَىٰ
Hausa
 
Shin, kã ga wanda ke hana.

Ayah   96:10   الأية
عَبْدًا إِذَا صَلَّىٰ
Hausa
 
Bãwã idan yã yi salla?

Ayah   96:11   الأية
أَرَأَيْتَ إِن كَانَ عَلَى الْهُدَىٰ
Hausa
 
Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?

Ayah   96:12   الأية
أَوْ أَمَرَ بِالتَّقْوَىٰ
Hausa
 
Ko ya yi umurni da taƙawa?

Ayah   96:13   الأية
أَرَأَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Hausa
 
Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?

Ayah   96:14   الأية
أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ اللَّهَ يَرَىٰ
Hausa
 
Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?

Ayah   96:15   الأية
كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًا بِالنَّاصِيَةِ
Hausa
 
A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.

Ayah   96:16   الأية
نَاصِيَةٍ كَاذِبَةٍ خَاطِئَةٍ
Hausa
 
Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.

Ayah   96:17   الأية
فَلْيَدْعُ نَادِيَهُ
Hausa
 
Sai ya kirayi ƙungiyarsa.

Ayah   96:18   الأية
سَنَدْعُ الزَّبَانِيَةَ
Hausa
 
Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).

Ayah   96:19   الأية
كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَاسْجُدْ وَاقْتَرِب ۩
Hausa
 
A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka). 
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us