« Prev
80. Surah 'Abasa سورة عبس
Next »
First Ayah 1 الأية الأوليبِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
عَبَسَ وَتَوَلَّىٰ
Hausa
Yã game huska kuma ya jũya bãya.
|
Ayah 80:2 الأية
أَن جَاءَهُ الْأَعْمَىٰ
Hausa
Sabõda makãho yã je masa.
|
Ayah 80:3 الأية
وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُ يَزَّكَّىٰ
Hausa
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
|
Ayah 80:4 الأية
أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ الذِّكْرَىٰ
Hausa
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
|
Ayah 80:5 الأية
أَمَّا مَنِ اسْتَغْنَىٰ
Hausa
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
|
Ayah 80:6 الأية
فَأَنتَ لَهُ تَصَدَّىٰ
Hausa
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
|
Ayah 80:7 الأية
وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ
Hausa
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
|
Ayah 80:8 الأية
وَأَمَّا مَن جَاءَكَ يَسْعَىٰ
Hausa
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
|
Ayah 80:9 الأية
وَهُوَ يَخْشَىٰ
Hausa
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
|
Ayah 80:10 الأية
فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ
Hausa
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
|
Ayah 80:11 الأية
كَلَّا إِنَّهَا تَذْكِرَةٌ
Hausa
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
|
Ayah 80:12 الأية
فَمَن شَاءَ ذَكَرَهُ
Hausa
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
|
Ayah 80:13 الأية
فِي صُحُفٍ مُّكَرَّمَةٍ
Hausa
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
|
Ayah 80:14 الأية
مَّرْفُوعَةٍ مُّطَهَّرَةٍ
Hausa
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
|
Ayah 80:15 الأية
بِأَيْدِي سَفَرَةٍ
Hausa
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
|
Ayah 80:16 الأية
كِرَامٍ بَرَرَةٍ
Hausa
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
|
Ayah 80:17 الأية
قُتِلَ الْإِنسَانُ مَا أَكْفَرَهُ
Hausa
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
|
Ayah 80:18 الأية
مِنْ أَيِّ شَيْءٍ خَلَقَهُ
Hausa
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
|
Ayah 80:19 الأية
مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُ فَقَدَّرَهُ
Hausa
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
|
Ayah 80:20 الأية
ثُمَّ السَّبِيلَ يَسَّرَهُ
Hausa
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
|
Ayah 80:21 الأية
ثُمَّ أَمَاتَهُ فَأَقْبَرَهُ
Hausa
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
|
Ayah 80:22 الأية
ثُمَّ إِذَا شَاءَ أَنشَرَهُ
Hausa
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
|
Ayah 80:23 الأية
كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَا أَمَرَهُ
Hausa
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin
kabari).
|
Ayah 80:24 الأية
فَلْيَنظُرِ الْإِنسَانُ إِلَىٰ طَعَامِهِ
Hausa
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
|
Ayah 80:25 الأية
أَنَّا صَبَبْنَا الْمَاءَ صَبًّا
Hausa
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
|
Ayah 80:26 الأية
ثُمَّ شَقَقْنَا الْأَرْضَ شَقًّا
Hausa
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
|
Ayah 80:27 الأية
فَأَنبَتْنَا فِيهَا حَبًّا
Hausa
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya ,a cikinta.
|
Ayah 80:28 الأية
وَعِنَبًا وَقَضْبًا
Hausa
Da inabi da ciyãwa.
|
Ayah 80:29 الأية
وَزَيْتُونًا وَنَخْلًا
Hausa
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
|
Ayah 80:30 الأية
وَحَدَائِقَ غُلْبًا
Hausa
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
|
Ayah 80:31 الأية
وَفَاكِهَةً وَأَبًّا
Hausa
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
|
Ayah 80:32 الأية
مَّتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْ
Hausa
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
|
Ayah 80:33 الأية
فَإِذَا جَاءَتِ الصَّاخَّةُ
Hausa
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
|
Ayah 80:34 الأية
يَوْمَ يَفِرُّ الْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ
Hausa
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
|
Ayah 80:35 الأية
وَأُمِّهِ وَأَبِيهِ
Hausa
Da uwarsa da ubansa.
|
Ayah 80:36 الأية
وَصَاحِبَتِهِ وَبَنِيهِ
Hausa
Da mãtarsa da ɗiyansa.
|
Ayah 80:37 الأية
لِكُلِّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍ شَأْنٌ يُغْنِيهِ
Hausa
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
|
Ayah 80:38 الأية
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ مُّسْفِرَةٌ
Hausa
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
|
Ayah 80:39 الأية
ضَاحِكَةٌ مُّسْتَبْشِرَةٌ
Hausa
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
|
Ayah 80:40 الأية
وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌ
Hausa
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
|
Ayah 80:41 الأية
تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ
Hausa
Baƙi zai rufe su.
|
Ayah 80:42 الأية
أُولَٰئِكَ هُمُ الْكَفَرَةُ الْفَجَرَةُ
Hausa
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|
|