« Prev

37. Surah As-Sâffât سورة الصافات

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَالصَّافَّاتِ صَفًّا
Hausa
 
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).

Ayah   37:2   الأية
فَالزَّاجِرَاتِ زَجْرًا
Hausa
 
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.

Ayah   37:3   الأية
فَالتَّالِيَاتِ ذِكْرًا
Hausa
 
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.

Ayah   37:4   الأية
إِنَّ إِلَٰهَكُمْ لَوَاحِدٌ
Hausa
 
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.

Ayah   37:5   الأية
رَّبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ الْمَشَارِقِ
Hausa
 
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.

Ayah   37:6   الأية
إِنَّا زَيَّنَّا السَّمَاءَ الدُّنْيَا بِزِينَةٍ الْكَوَاكِبِ
Hausa
 
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.

Ayah   37:7   الأية
وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَانٍ مَّارِدٍ
Hausa
 
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.

Ayah   37:8   الأية
لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى الْمَلَإِ الْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ
Hausa
 
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.

Ayah   37:9   الأية
دُحُورًا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ
Hausa
 
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.

Ayah   37:10   الأية
إِلَّا مَنْ خَطِفَ الْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ ثَاقِبٌ
Hausa
 
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.

Ayah   37:11   الأية
فَاسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَا ۚ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّن طِينٍ لَّازِبٍ
Hausa
 
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.

Ayah   37:12   الأية
بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ
Hausa
 
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.

Ayah   37:13   الأية
وَإِذَا ذُكِّرُوا لَا يَذْكُرُونَ
Hausa
 
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.

Ayah   37:14   الأية
وَإِذَا رَأَوْا آيَةً يَسْتَسْخِرُونَ
Hausa
 
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.

Ayah   37:15   الأية
وَقَالُوا إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ
Hausa
 
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."

Ayah   37:16   الأية
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
Hausa
 
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa,ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?

Ayah   37:17   الأية
أَوَآبَاؤُنَا الْأَوَّلُونَ
Hausa
 
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"

Ayah   37:18   الأية
قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَاخِرُونَ
Hausa
 
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."

Ayah   37:19   الأية
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ
Hausa
 
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.

Ayah   37:20   الأية
وَقَالُوا يَا وَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ الدِّينِ
Hausa
 
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."

Ayah   37:21   الأية
هَٰذَا يَوْمُ الْفَصْلِ الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ
Hausa
 
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.

Ayah   37:22   الأية
احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأَزْوَاجَهُمْ وَمَا كَانُوا يَعْبُدُونَ
Hausa
 
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.

Ayah   37:23   الأية
مِن دُونِ اللَّهِ فَاهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَاطِ الْجَحِيمِ
Hausa
 
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.

Ayah   37:24   الأية
وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْئُولُونَ
Hausa
 
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.

Ayah   37:25   الأية
مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ
Hausa
 
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?

Ayah   37:26   الأية
بَلْ هُمُ الْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ
Hausa
 
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.

Ayah   37:27   الأية
وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ
Hausa
 
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.

Ayah   37:28   الأية
قَالُوا إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ الْيَمِينِ
Hausa
 
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."

Ayah   37:29   الأية
قَالُوا بَل لَّمْ تَكُونُوا مُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.

Ayah   37:30   الأية
وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَانٍ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَاغِينَ
Hausa
 
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."

Ayah   37:31   الأية
فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَا ۖ إِنَّا لَذَائِقُونَ
Hausa
 
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."

Ayah   37:32   الأية
فَأَغْوَيْنَاكُمْ إِنَّا كُنَّا غَاوِينَ
Hausa
 
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."

Ayah   37:33   الأية
فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِي الْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ
Hausa
 
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.

Ayah   37:34   الأية
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِالْمُجْرِمِينَ
Hausa
 
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.

Ayah   37:35   الأية
إِنَّهُمْ كَانُوا إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَا إِلَٰهَ إِلَّا اللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ
Hausa
 
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.

Ayah   37:36   الأية
وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُو آلِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍ
Hausa
 
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?

Ayah   37:37   الأية
بَلْ جَاءَ بِالْحَقِّ وَصَدَّقَ الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.

Ayah   37:38   الأية
إِنَّكُمْ لَذَائِقُو الْعَذَابِ الْأَلِيمِ
Hausa
 
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.

Ayah   37:39   الأية
وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
Hausa
 
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.

Ayah   37:40   الأية
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Hausa
 
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Ayah   37:41   الأية
أُولَٰئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌ
Hausa
 
Waɗannan sunã da abinci sananne.

Ayah   37:42   الأية
فَوَاكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ
Hausa
 
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.

Ayah   37:43   الأية
فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِ
Hausa
 
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.

Ayah   37:44   الأية
عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَابِلِينَ
Hausa
 
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.

Ayah   37:45   الأية
يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ
Hausa
 
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.

Ayah   37:46   الأية
بَيْضَاءَ لَذَّةٍ لِّلشَّارِبِينَ
Hausa
 
Farã mai dãɗi ga mashãyan.

Ayah   37:47   الأية
لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ
Hausa
 
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,

Ayah   37:48   الأية
وَعِندَهُمْ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ عِينٌ
Hausa
 
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.

Ayah   37:49   الأية
كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌ
Hausa
 
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.

Ayah   37:50   الأية
فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ
Hausa
 
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.

Ayah   37:51   الأية
قَالَ قَائِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٌ
Hausa
 
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."

Ayah   37:52   الأية
يَقُولُ أَإِنَّكَ لَمِنَ الْمُصَدِّقِينَ
Hausa
 
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"

Ayah   37:53   الأية
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَدِينُونَ
Hausa
 
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"

Ayah   37:54   الأية
قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ
Hausa
 
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"

Ayah   37:55   الأية
فَاطَّلَعَ فَرَآهُ فِي سَوَاءِ الْجَحِيمِ
Hausa
 
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.

Ayah   37:56   الأية
قَالَ تَاللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ
Hausa
 
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."

Ayah   37:57   الأية
وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ الْمُحْضَرِينَ
Hausa
 
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."

Ayah   37:58   الأية
أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ
Hausa
 
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."

Ayah   37:59   الأية
إِلَّا مَوْتَتَنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ
Hausa
 
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"

Ayah   37:60   الأية
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ
Hausa
 
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.

Ayah   37:61   الأية
لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ الْعَامِلُونَ
Hausa
 
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.

Ayah   37:62   الأية
أَذَٰلِكَ خَيْرٌ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ الزَّقُّومِ
Hausa
 
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?

Ayah   37:63   الأية
إِنَّا جَعَلْنَاهَا فِتْنَةً لِّلظَّالِمِينَ
Hausa
 
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.

Ayah   37:64   الأية
إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِي أَصْلِ الْجَحِيمِ
Hausa
 
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.

Ayah   37:65   الأية
طَلْعُهَا كَأَنَّهُ رُءُوسُ الشَّيَاطِينِ
Hausa
 
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.

Ayah   37:66   الأية
فَإِنَّهُمْ لَآكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ
Hausa
 
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.

Ayah   37:67   الأية
ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍ
Hausa
 
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.

Ayah   37:68   الأية
ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى الْجَحِيمِ
Hausa
 
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.

Ayah   37:69   الأية
إِنَّهُمْ أَلْفَوْا آبَاءَهُمْ ضَالِّينَ
Hausa
 
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.

Ayah   37:70   الأية
فَهُمْ عَلَىٰ آثَارِهِمْ يُهْرَعُونَ
Hausa
 
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.

Ayah   37:71   الأية
وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ الْأَوَّلِينَ
Hausa
 
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.

Ayah   37:72   الأية
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ
Hausa
 
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.

Ayah   37:73   الأية
فَانظُرْ كَيْفَ كَانَ عَاقِبَةُ الْمُنذَرِينَ
Hausa
 
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.

Ayah   37:74   الأية
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Hausa
 
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Ayah   37:75   الأية
وَلَقَدْ نَادَانَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ الْمُجِيبُونَ
Hausa
 
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.

Ayah   37:76   الأية
وَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ
Hausa
 
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.

Ayah   37:77   الأية
وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُ هُمُ الْبَاقِينَ
Hausa
 
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.

Ayah   37:78   الأية
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Hausa
 
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.

Ayah   37:79   الأية
سَلَامٌ عَلَىٰ نُوحٍ فِي الْعَالَمِينَ
Hausa
 
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.

Ayah   37:80   الأية
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Hausa
 
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Ayah   37:81   الأية
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.

Ayah   37:82   الأية
ثُمَّ أَغْرَقْنَا الْآخَرِينَ
Hausa
 
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.

Ayah   37:83   الأية
وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِ لَإِبْرَاهِيمَ
Hausa
 
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.

Ayah   37:84   الأية
إِذْ جَاءَ رَبَّهُ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ
Hausa
 
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.

Ayah   37:85   الأية
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَاذَا تَعْبُدُونَ
Hausa
 
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"

Ayah   37:86   الأية
أَئِفْكًا آلِهَةً دُونَ اللَّهِ تُرِيدُونَ
Hausa
 
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"

Ayah   37:87   الأية
فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"

Ayah   37:88   الأية
فَنَظَرَ نَظْرَةً فِي النُّجُومِ
Hausa
 
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.

Ayah   37:89   الأية
فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٌ
Hausa
 
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."

Ayah   37:90   الأية
فَتَوَلَّوْا عَنْهُ مُدْبِرِينَ
Hausa
 
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.

Ayah   37:91   الأية
فَرَاغَ إِلَىٰ آلِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ
Hausa
 
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?

Ayah   37:92   الأية
مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ
Hausa
 
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"

Ayah   37:93   الأية
فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًا بِالْيَمِينِ
Hausa
 
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.

Ayah   37:94   الأية
فَأَقْبَلُوا إِلَيْهِ يَزِفُّونَ
Hausa
 
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.

Ayah   37:95   الأية
قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ
Hausa
 
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,

Ayah   37:96   الأية
وَاللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ
Hausa
 
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"

Ayah   37:97   الأية
قَالُوا ابْنُوا لَهُ بُنْيَانًا فَأَلْقُوهُ فِي الْجَحِيمِ
Hausa
 
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."

Ayah   37:98   الأية
فَأَرَادُوا بِهِ كَيْدًا فَجَعَلْنَاهُمُ الْأَسْفَلِينَ
Hausa
 
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.

Ayah   37:99   الأية
وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهْدِينِ
Hausa
 
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."

Ayah   37:100   الأية
رَبِّ هَبْ لِي مِنَ الصَّالِحِينَ
Hausa
 
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."

Ayah   37:101   الأية
فَبَشَّرْنَاهُ بِغُلَامٍ حَلِيمٍ
Hausa
 
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.

Ayah   37:102   الأية
فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ السَّعْيَ قَالَ يَا بُنَيَّ إِنِّي أَرَىٰ فِي الْمَنَامِ أَنِّي أَذْبَحُكَ فَانظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَا أَبَتِ افْعَلْ مَا تُؤْمَرُ ۖ سَتَجِدُنِي إِن شَاءَ اللَّهُ مِنَ الصَّابِرِينَ
Hausa
 
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."

Ayah   37:103   الأية
فَلَمَّا أَسْلَمَا وَتَلَّهُ لِلْجَبِينِ
Hausa
 
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.

Ayah   37:104   الأية
وَنَادَيْنَاهُ أَن يَا إِبْرَاهِيمُ
Hausa
 
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"

Ayah   37:105   الأية
قَدْ صَدَّقْتَ الرُّؤْيَا ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Hausa
 
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Ayah   37:106   الأية
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْبَلَاءُ الْمُبِينُ
Hausa
 
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.

Ayah   37:107   الأية
وَفَدَيْنَاهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍ
Hausa
 
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.

Ayah   37:108   الأية
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Hausa
 
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.

Ayah   37:109   الأية
سَلَامٌ عَلَىٰ إِبْرَاهِيمَ
Hausa
 
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.

Ayah   37:110   الأية
كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Hausa
 
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Ayah   37:111   الأية
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

Ayah   37:112   الأية
وَبَشَّرْنَاهُ بِإِسْحَاقَ نَبِيًّا مِّنَ الصَّالِحِينَ
Hausa
 
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.

Ayah   37:113   الأية
وَبَارَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰ إِسْحَاقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِ مُبِينٌ
Hausa
 
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).

Ayah   37:114   الأية
وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ
Hausa
 
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.

Ayah   37:115   الأية
وَنَجَّيْنَاهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ
Hausa
 
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.

Ayah   37:116   الأية
وَنَصَرْنَاهُمْ فَكَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ
Hausa
 
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.

Ayah   37:117   الأية
وَآتَيْنَاهُمَا الْكِتَابَ الْمُسْتَبِينَ
Hausa
 
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.

Ayah   37:118   الأية
وَهَدَيْنَاهُمَا الصِّرَاطَ الْمُسْتَقِيمَ
Hausa
 
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.

Ayah   37:119   الأية
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِي الْآخِرِينَ
Hausa
 
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.

Ayah   37:120   الأية
سَلَامٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ
Hausa
 
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.

Ayah   37:121   الأية
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Hausa
 
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Ayah   37:122   الأية
إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.

Ayah   37:123   الأية
وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

Ayah   37:124   الأية
إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِ أَلَا تَتَّقُونَ
Hausa
 
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"

Ayah   37:125   الأية
أَتَدْعُونَ بَعْلًا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ الْخَالِقِينَ
Hausa
 
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"

Ayah   37:126   الأية
اللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ
Hausa
 
"Allah Ubangijinku,kuma Ubangijin ubanninku farko?"

Ayah   37:127   الأية
فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ
Hausa
 
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).

Ayah   37:128   الأية
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Hausa
 
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Ayah   37:129   الأية
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Hausa
 
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.

Ayah   37:130   الأية
سَلَامٌ عَلَىٰ إِلْ يَاسِينَ
Hausa
 
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.

Ayah   37:131   الأية
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Hausa
 
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Ayah   37:132   الأية
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

Ayah   37:133   الأية
وَإِنَّ لُوطًا لَّمِنَ الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

Ayah   37:134   الأية
إِذْ نَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَ
Hausa
 
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.

Ayah   37:135   الأية
إِلَّا عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَ
Hausa
 
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).

Ayah   37:136   الأية
ثُمَّ دَمَّرْنَا الْآخَرِينَ
Hausa
 
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.

Ayah   37:137   الأية
وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ
Hausa
 
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.

Ayah   37:138   الأية
وَبِاللَّيْلِ ۗ أَفَلَا تَعْقِلُونَ
Hausa
 
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?

Ayah   37:139   الأية
وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

Ayah   37:140   الأية
إِذْ أَبَقَ إِلَى الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ
Hausa
 
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.

Ayah   37:141   الأية
فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ الْمُدْحَضِينَ
Hausa
 
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.

Ayah   37:142   الأية
فَالْتَقَمَهُ الْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌ
Hausa
 
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

Ayah   37:143   الأية
فَلَوْلَا أَنَّهُ كَانَ مِنَ الْمُسَبِّحِينَ
Hausa
 
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,

Ayah   37:144   الأية
لَلَبِثَ فِي بَطْنِهِ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ
Hausa
 
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.

Ayah   37:145   الأية
فَنَبَذْنَاهُ بِالْعَرَاءِ وَهُوَ سَقِيمٌ
Hausa
 
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.

Ayah   37:146   الأية
وَأَنبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةً مِّن يَقْطِينٍ
Hausa
 
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.

Ayah   37:147   الأية
وَأَرْسَلْنَاهُ إِلَىٰ مِائَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ
Hausa
 
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).

Ayah   37:148   الأية
فَآمَنُوا فَمَتَّعْنَاهُمْ إِلَىٰ حِينٍ
Hausa
 
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.

Ayah   37:149   الأية
فَاسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ الْبَنَاتُ وَلَهُمُ الْبَنُونَ
Hausa
 
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"

Ayah   37:150   الأية
أَمْ خَلَقْنَا الْمَلَائِكَةَ إِنَاثًا وَهُمْ شَاهِدُونَ
Hausa
 
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?

Ayah   37:151   الأية
أَلَا إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ
Hausa
 
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.

Ayah   37:152   الأية
وَلَدَ اللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَاذِبُونَ
Hausa
 
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.

Ayah   37:153   الأية
أَصْطَفَى الْبَنَاتِ عَلَى الْبَنِينَ
Hausa
 
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?

Ayah   37:154   الأية
مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ
Hausa
 
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?

Ayah   37:155   الأية
أَفَلَا تَذَكَّرُونَ
Hausa
 
Shin, bã ku tunãni?

Ayah   37:156   الأية
أَمْ لَكُمْ سُلْطَانٌ مُّبِينٌ
Hausa
 
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?

Ayah   37:157   الأية
فَأْتُوا بِكِتَابِكُمْ إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ
Hausa
 
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.

Ayah   37:158   الأية
وَجَعَلُوا بَيْنَهُ وَبَيْنَ الْجِنَّةِ نَسَبًا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ الْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ
Hausa
 
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"

Ayah   37:159   الأية
سُبْحَانَ اللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ
Hausa
 
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.

Ayah   37:160   الأية
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Hausa
 
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Ayah   37:161   الأية
فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ
Hausa
 
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,

Ayah   37:162   الأية
مَا أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَاتِنِينَ
Hausa
 
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.

Ayah   37:163   الأية
إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ الْجَحِيمِ
Hausa
 
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.

Ayah   37:164   الأية
وَمَا مِنَّا إِلَّا لَهُ مَقَامٌ مَّعْلُومٌ
Hausa
 
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."

Ayah   37:165   الأية
وَإِنَّا لَنَحْنُ الصَّافُّونَ
Hausa
 
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."

Ayah   37:166   الأية
وَإِنَّا لَنَحْنُ الْمُسَبِّحُونَ
Hausa
 
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."

Ayah   37:167   الأية
وَإِن كَانُوا لَيَقُولُونَ
Hausa
 
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,

Ayah   37:168   الأية
لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًا مِّنَ الْأَوَّلِينَ
Hausa
 
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."

Ayah   37:169   الأية
لَكُنَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Hausa
 
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."

Ayah   37:170   الأية
فَكَفَرُوا بِهِ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ
Hausa
 
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.

Ayah   37:171   الأية
وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.

Ayah   37:172   الأية
إِنَّهُمْ لَهُمُ الْمَنصُورُونَ
Hausa
 
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.

Ayah   37:173   الأية
وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ الْغَالِبُونَ
Hausa
 
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.

Ayah   37:174   الأية
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ
Hausa
 
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.

Ayah   37:175   الأية
وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ
Hausa
 
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.

Ayah   37:176   الأية
أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ
Hausa
 
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?

Ayah   37:177   الأية
فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَاءَ صَبَاحُ الْمُنذَرِينَ
Hausa
 
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.

Ayah   37:178   الأية
وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ
Hausa
 
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.

Ayah   37:179   الأية
وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ
Hausa
 
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.

Ayah   37:180   الأية
سُبْحَانَ رَبِّكَ رَبِّ الْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ
Hausa
 
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.

Ayah   37:181   الأية
وَسَلَامٌ عَلَى الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.

Ayah   37:182   الأية
وَالْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us