First Ayah 1 الأية الأوليبِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَالصَّافَّاتِ صَفًّا
Hausa
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
|
Ayah 37:2 الأية
فَالزَّاجِرَاتِ زَجْرًا
Hausa
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
|
Ayah 37:3 الأية
فَالتَّالِيَاتِ ذِكْرًا
Hausa
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
|
Ayah 37:4 الأية
إِنَّ إِلَٰهَكُمْ لَوَاحِدٌ
Hausa
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
|
Ayah 37:5 الأية
رَّبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ الْمَشَارِقِ
Hausa
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar
rãnã.
|
Ayah 37:6 الأية
إِنَّا زَيَّنَّا السَّمَاءَ الدُّنْيَا بِزِينَةٍ الْكَوَاكِبِ
Hausa
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
|
Ayah 37:7 الأية
وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَانٍ مَّارِدٍ
Hausa
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
|
Ayah 37:8 الأية
لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى الْمَلَإِ الْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ
Hausa
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar
su daga kõwane gẽfe.
|
Ayah 37:9 الأية
دُحُورًا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ
Hausa
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
|
Ayah 37:10 الأية
إِلَّا مَنْ خَطِفَ الْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ ثَاقِبٌ
Hausa
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
|
Ayah 37:11 الأية
فَاسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَا ۚ إِنَّا خَلَقْنَاهُم
مِّن طِينٍ لَّازِبٍ
Hausa
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka
halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
|
Ayah 37:12 الأية
بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ
Hausa
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
|
Ayah 37:13 الأية
وَإِذَا ذُكِّرُوا لَا يَذْكُرُونَ
Hausa
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
|
Ayah 37:14 الأية
وَإِذَا رَأَوْا آيَةً يَسْتَسْخِرُونَ
Hausa
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
|
Ayah 37:15 الأية
وَقَالُوا إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ
Hausa
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
|
Ayah 37:16 الأية
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
Hausa
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa,ashe, lalle mũ
tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
|
Ayah 37:17 الأية
أَوَآبَاؤُنَا الْأَوَّلُونَ
Hausa
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
|
Ayah 37:18 الأية
قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَاخِرُونَ
Hausa
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
|
Ayah 37:19 الأية
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ
Hausa
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
|
Ayah 37:20 الأية
وَقَالُوا يَا وَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ الدِّينِ
Hausa
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
|
Ayah 37:21 الأية
هَٰذَا يَوْمُ الْفَصْلِ الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ
Hausa
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
|
Ayah 37:22 الأية
احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأَزْوَاجَهُمْ وَمَا كَانُوا يَعْبُدُونَ
Hausa
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã
bautãwa.
|
Ayah 37:23 الأية
مِن دُونِ اللَّهِ فَاهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَاطِ الْجَحِيمِ
Hausa
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
|
Ayah 37:24 الأية
وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْئُولُونَ
Hausa
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
|
Ayah 37:25 الأية
مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ
Hausa
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
|
Ayah 37:26 الأية
بَلْ هُمُ الْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ
Hausa
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
|
Ayah 37:27 الأية
وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ
Hausa
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
|
Ayah 37:28 الأية
قَالُوا إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ الْيَمِينِ
Hausa
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka
amince)."
|
Ayah 37:29 الأية
قَالُوا بَل لَّمْ تَكُونُوا مُؤْمِنِينَ
Hausa
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
|
Ayah 37:30 الأية
وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَانٍ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَاغِينَ
Hausa
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne
mãsu kẽtare iyãka."
|
Ayah 37:31 الأية
فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَا ۖ إِنَّا لَذَائِقُونَ
Hausa
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa
ne."
|
Ayah 37:32 الأية
فَأَغْوَيْنَاكُمْ إِنَّا كُنَّا غَاوِينَ
Hausa
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
|
Ayah 37:33 الأية
فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِي الْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ
Hausa
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
|
Ayah 37:34 الأية
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِالْمُجْرِمِينَ
Hausa
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
|
Ayah 37:35 الأية
إِنَّهُمْ كَانُوا إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَا إِلَٰهَ إِلَّا اللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ
Hausa
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su
dõra girman kai.
|
Ayah 37:36 الأية
وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُو آلِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍ
Hausa
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani
mawãƙi mahaukaci?
|
Ayah 37:37 الأية
بَلْ جَاءَ بِالْحَقِّ وَصَدَّقَ الْمُرْسَلِينَ
Hausa
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
|
Ayah 37:38 الأية
إِنَّكُمْ لَذَائِقُو الْعَذَابِ الْأَلِيمِ
Hausa
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
|
Ayah 37:39 الأية
وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
Hausa
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
|
Ayah 37:40 الأية
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Hausa
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
|
Ayah 37:41 الأية
أُولَٰئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌ
Hausa
Waɗannan sunã da abinci sananne.
|
Ayah 37:42 الأية
فَوَاكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ
Hausa
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
|
Ayah 37:43 الأية
فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِ
Hausa
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
|
Ayah 37:44 الأية
عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَابِلِينَ
Hausa
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
|
Ayah 37:45 الأية
يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ
Hausa
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
|
Ayah 37:46 الأية
بَيْضَاءَ لَذَّةٍ لِّلشَّارِبِينَ
Hausa
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
|
Ayah 37:47 الأية
لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ
Hausa
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
|
Ayah 37:48 الأية
وَعِندَهُمْ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ عِينٌ
Hausa
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
|
Ayah 37:49 الأية
كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌ
Hausa
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
|
Ayah 37:50 الأية
فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ
Hausa
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
|
Ayah 37:51 الأية
قَالَ قَائِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٌ
Hausa
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a
dũniya)."
|
Ayah 37:52 الأية
يَقُولُ أَإِنَّكَ لَمِنَ الْمُصَدِّقِينَ
Hausa
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
|
Ayah 37:53 الأية
أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَدِينُونَ
Hausa
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ
tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
|
Ayah 37:54 الأية
قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ
Hausa
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
|
Ayah 37:55 الأية
فَاطَّلَعَ فَرَآهُ فِي سَوَاءِ الْجَحِيمِ
Hausa
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
|
Ayah 37:56 الأية
قَالَ تَاللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ
Hausa
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
|
Ayah 37:57 الأية
وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ الْمُحْضَرِينَ
Hausa
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake
halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
|
Ayah 37:58 الأية
أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ
Hausa
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
|
Ayah 37:59 الأية
إِلَّا مَوْتَتَنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ
Hausa
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
|
Ayah 37:60 الأية
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ
Hausa
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
|
Ayah 37:61 الأية
لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ الْعَامِلُونَ
Hausa
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
|
Ayah 37:62 الأية
أَذَٰلِكَ خَيْرٌ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ الزَّقُّومِ
Hausa
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
|
Ayah 37:63 الأية
إِنَّا جَعَلْنَاهَا فِتْنَةً لِّلظَّالِمِينَ
Hausa
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
|
Ayah 37:64 الأية
إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِي أَصْلِ الْجَحِيمِ
Hausa
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
|
Ayah 37:65 الأية
طَلْعُهَا كَأَنَّهُ رُءُوسُ الشَّيَاطِينِ
Hausa
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
|
Ayah 37:66 الأية
فَإِنَّهُمْ لَآكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ
Hausa
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga
gare ta.
|
Ayah 37:67 الأية
ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍ
Hausa
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
|
Ayah 37:68 الأية
ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى الْجَحِيمِ
Hausa
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
|
Ayah 37:69 الأية
إِنَّهُمْ أَلْفَوْا آبَاءَهُمْ ضَالِّينَ
Hausa
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
|
Ayah 37:70 الأية
فَهُمْ عَلَىٰ آثَارِهِمْ يُهْرَعُونَ
Hausa
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
|
Ayah 37:71 الأية
وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ الْأَوَّلِينَ
Hausa
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
|
Ayah 37:72 الأية
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ
Hausa
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
|
Ayah 37:73 الأية
فَانظُرْ كَيْفَ كَانَ عَاقِبَةُ الْمُنذَرِينَ
Hausa
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
|
Ayah 37:74 الأية
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Hausa
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
|
Ayah 37:75 الأية
وَلَقَدْ نَادَانَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ الْمُجِيبُونَ
Hausa
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
|
Ayah 37:76 الأية
وَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ
Hausa
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
|
Ayah 37:77 الأية
وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُ هُمُ الْبَاقِينَ
Hausa
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
|
Ayah 37:78 الأية
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Hausa
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
|
Ayah 37:79 الأية
سَلَامٌ عَلَىٰ نُوحٍ فِي الْعَالَمِينَ
Hausa
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
|
Ayah 37:80 الأية
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Hausa
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
|
Ayah 37:81 الأية
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
|
Ayah 37:82 الأية
ثُمَّ أَغْرَقْنَا الْآخَرِينَ
Hausa
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
|
Ayah 37:83 الأية
وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِ لَإِبْرَاهِيمَ
Hausa
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
|
Ayah 37:84 الأية
إِذْ جَاءَ رَبَّهُ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ
Hausa
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
|
Ayah 37:85 الأية
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَاذَا تَعْبُدُونَ
Hausa
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
|
Ayah 37:86 الأية
أَئِفْكًا آلِهَةً دُونَ اللَّهِ تُرِيدُونَ
Hausa
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
|
Ayah 37:87 الأية
فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
|
Ayah 37:88 الأية
فَنَظَرَ نَظْرَةً فِي النُّجُومِ
Hausa
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
|
Ayah 37:89 الأية
فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٌ
Hausa
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
|
Ayah 37:90 الأية
فَتَوَلَّوْا عَنْهُ مُدْبِرِينَ
Hausa
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
|
Ayah 37:91 الأية
فَرَاغَ إِلَىٰ آلِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ
Hausa
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
|
Ayah 37:92 الأية
مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ
Hausa
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
|
Ayah 37:93 الأية
فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًا بِالْيَمِينِ
Hausa
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
|
Ayah 37:94 الأية
فَأَقْبَلُوا إِلَيْهِ يَزِفُّونَ
Hausa
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
|
Ayah 37:95 الأية
قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ
Hausa
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
|
Ayah 37:96 الأية
وَاللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ
Hausa
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
|
Ayah 37:97 الأية
قَالُوا ابْنُوا لَهُ بُنْيَانًا فَأَلْقُوهُ فِي الْجَحِيمِ
Hausa
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
|
Ayah 37:98 الأية
فَأَرَادُوا بِهِ كَيْدًا فَجَعَلْنَاهُمُ الْأَسْفَلِينَ
Hausa
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi
ƙasƙanci.
|
Ayah 37:99 الأية
وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهْدِينِ
Hausa
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar
da ni."
|
Ayah 37:100 الأية
رَبِّ هَبْ لِي مِنَ الصَّالِحِينَ
Hausa
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
|
Ayah 37:101 الأية
فَبَشَّرْنَاهُ بِغُلَامٍ حَلِيمٍ
Hausa
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
|
Ayah 37:102 الأية
فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ السَّعْيَ قَالَ يَا بُنَيَّ إِنِّي أَرَىٰ فِي الْمَنَامِ
أَنِّي أَذْبَحُكَ فَانظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَا أَبَتِ افْعَلْ مَا تُؤْمَرُ
ۖ سَتَجِدُنِي إِن شَاءَ اللَّهُ مِنَ الصَّابِرِينَ
Hausa
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã
gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce:
"Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so,
daga mãsu haƙuri."
|
Ayah 37:103 الأية
فَلَمَّا أَسْلَمَا وَتَلَّهُ لِلْجَبِينِ
Hausa
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
|
Ayah 37:104 الأية
وَنَادَيْنَاهُ أَن يَا إِبْرَاهِيمُ
Hausa
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
|
Ayah 37:105 الأية
قَدْ صَدَّقْتَ الرُّؤْيَا ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Hausa
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
|
Ayah 37:106 الأية
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْبَلَاءُ الْمُبِينُ
Hausa
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
|
Ayah 37:107 الأية
وَفَدَيْنَاهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍ
Hausa
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
|
Ayah 37:108 الأية
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ
Hausa
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
|
Ayah 37:109 الأية
سَلَامٌ عَلَىٰ إِبْرَاهِيمَ
Hausa
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
|
Ayah 37:110 الأية
كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ
Hausa
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
|
Ayah 37:111 الأية
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
|
Ayah 37:112 الأية
وَبَشَّرْنَاهُ بِإِسْحَاقَ نَبِيًّا مِّنَ الصَّالِحِينَ
Hausa
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
|
Ayah 37:113 الأية
وَبَارَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰ إِسْحَاقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ
وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِ مُبِينٌ
Hausa
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu
akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga
zãluncin).
|
Ayah 37:114 الأية
وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ
Hausa
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
|
Ayah 37:115 الأية
وَنَجَّيْنَاهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ
Hausa
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
|
Ayah 37:116 الأية
وَنَصَرْنَاهُمْ فَكَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ
Hausa
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
|
Ayah 37:117 الأية
وَآتَيْنَاهُمَا الْكِتَابَ الْمُسْتَبِينَ
Hausa
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
|
|